• English
  • Business News
Saturday, July 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Farashin Kayan Amfanin Gona Ya Fara Sauka A Wasu Kasuwanni

by Abubakar Abba
10 months ago
in Noma Da Kiwo
0
Farashin Kayan Amfanin Gona Ya Fara Sauka A Wasu Kasuwanni
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A yayin da aka fara girbe wasu daga cikin amfanin gonar da manoma suka shuka a kakar noman bana, farashin Tumatir, Tattasai, Doya da kuma Rogo, ya ragu a wasu sassa na cikin wannan kasa, wanda hakan ya samar da saukin tsada ga masu amfani da su.

Wannan na zuwa ne, daidai lokacin da kasar ke fuskantar kalubalen rashin abinci, wanda hakan ya haifar da matukar tsadar kayan abincin a dukkanin fadin wannan kasa.

  • Rawar Da Masu Sa Ido Ke Takawa Wajen Magudin Zabe A Nijeriya
  • Zaben Gwamna: Kallo Ya Koma Jihar Edo

Shirin samar da abinci na duniya da ke karkashin kulawar Majalisar Dinkin Duniya (WFP) ya ruwaito cewa, mutane miliyan 4.4 a shiyyar Arewa maso Gabas, na fuskantar kalubalen rashin abinci mai gina jiki.

Haka zalika, wani bincike da jaridar BusinessDay ta gudanar a wasu kasuwanni da ke Jihar Legas ta gano cewa; farashin Rogo ya ragu da kashi 42.5, inda ake sayar da shi a kan Naira 2,300; sabanin yadda ake sayar da shi a watan Yuli kan farashin Naira 4,000.

Bugu da kari, farashin buhun Rogo mai nauyin kilo 50, ya ragu zuwa Naira 65,000; sabanin yadda ake sayar da shi a watan Yuli kan farashin Naira 75,000.

Labarai Masu Nasaba

Asusun NADF, OCP Da Gwamnatin Katsina Sun Kaddamar Da Noman Hekta 50

Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare

Kazalika, farashin Dankali ma ya ragu da kashi 50 cikin 100; sakamakon manomansa sun fara girbinsa a jihohin da aka fi noma shi.

Sannan, farashin Tumatir shi ma ya sauka da kashi 58 cikin 100 a Jihar Legas, inda ake sayar da babban kwando a kan Naira 120,000 zuwa Naira 50,000 a kasuwar Mile 12.

A garin Onitsha kuma, babban kwandon Tumatir ana sayar da shi daga Naira 60,000 zuwa Naira 75,000 a kasuwannin Ochanja da kuma Ose.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Amfanin GonaFarashi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ilimi: Gwamna Yusuf Ya Raba Wa Makarantun Kano Kujerun Zama 73,000

Next Post

Zaɓen Edo: EFCC Ta Kama Wasu Mutune Kan Zargin Sayen Ƙuri’a

Related

Sin Ta Gaggauta Aikin Gyara Da Kyautata Ababen Aikin Gona
Noma Da Kiwo

Asusun NADF, OCP Da Gwamnatin Katsina Sun Kaddamar Da Noman Hekta 50

4 hours ago
Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare

6 hours ago
Abinci
Noma Da Kiwo

Dalilin Gwamnatin Tarayya Na Yin Hadaka Da Jihar Nasarawa Don Bunkasa Noma

1 week ago
Shettima
Noma Da Kiwo

Nijeriya Za Ta Rika Samun Naira Tiriliyan Uku A Aikin Tatsar Rogo Duk Shekara – Kashim

1 week ago
Wa’adin Da Tinubu Ya Bai Wa Manoman Da Suka Ci Bashin ‘Anchor Borrowers’ Ya Cika
Noma Da Kiwo

Dalilin Ware Naira Biliyan 19.5 Da Asusun Bunkasa Aikin Noma Ya Yi

2 weeks ago
Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

2 weeks ago
Next Post
Zaɓen Edo: EFCC Ta Kama Wasu Mutune Kan Zargin Sayen Ƙuri’a

Zaɓen Edo: EFCC Ta Kama Wasu Mutune Kan Zargin Sayen Ƙuri’a

LABARAI MASU NASABA

An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa

Edo Da Taraba : ‘Yansanda Sun Ceto Mutum 31 Da Aka Yi Garkuwa Da Su Bayan Musayar Wuta

July 26, 2025
WAFCON 2025: Yau Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Moroko A Wasan Ƙarshe

WAFCON 2025: Yau Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Moroko A Wasan Ƙarshe

July 26, 2025
Kotu

NSCDC Ta Gurfanar Da Wanda Ake Zargi Da Badakalar Naira Miliyan 159

July 26, 2025
Fasakwauri: ‘Yansandan Indiya Sun Kama ‘Yar Nijeriya Da Kwayar Dala Miliyan 4

Fasakwauri: ‘Yansandan Indiya Sun Kama ‘Yar Nijeriya Da Kwayar Dala Miliyan 4

July 26, 2025
Sin Ta Gaggauta Aikin Gyara Da Kyautata Ababen Aikin Gona

Asusun NADF, OCP Da Gwamnatin Katsina Sun Kaddamar Da Noman Hekta 50

July 26, 2025
Gwamnatin Kano Ta Gabatar Da Buƙatu 10 A Gaban Kwamitin Gyaran Tsarin Mulkin Nijeriya

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincikar Kwamishinan Sufuri Kan Karɓar Belin Dilan Ƙwaya A Kano

July 26, 2025
Manyan Nasarorin Da Dakta Dantsoho Ya Samar Tun Darewarsa Shugabancin NPA

Manyan Nasarorin Da Dakta Dantsoho Ya Samar Tun Darewarsa Shugabancin NPA

July 26, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare

Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare

July 26, 2025
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

July 26, 2025
Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

July 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.