ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rawar Da Masu Sa Ido Ke Takawa Wajen Magudin Zabe A Nijeriya

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Rawar

Ana nuna damuwa kan sahihancin rahotannin kungiyoyin masu sa ido kan zabe, saboda mafi yawancinsu suna nuna son ransu wajen bayar da rahotanni, yayin da wasu kuma ake ke hada kai da su wajen tafka magudin zabe ko su yi biyayya ga iyayen gidansu ko kuma wadanda suke ra’ayinsu.

Zabuka a Nijeriya na cike da masu sa ido da kungiyoyi daban-daban ke turawa. Domin sa ido a babban zaben 2023, an tura masu sa ido na cikin gida da na kasashen waje 146,913. Sannan kimanin 1,000 daga cikinsu ake sa ran za su saka ido zaben gwamnan Jihar Edo.

  • Dakta Gadan-ƙaya Ya Bada Haƙuri Kan Zargin Auren Jinsi Da Ya Yi A Bauchi
  • Yawan Mutanen Da Suka Shiga Da Fita Daga Kasar Sin A Hutun Bikin Tsakiyar Kaka Ya Zarce Miliyan 5.25

Yayin da akasarin kungiyoyin masu sa ido ba sa gabatar da rahotanni a karshen zabukan, kamar yadda shugaban hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC), Farfesa Mahmood Yakubu ya bayyana cewa wasu da suka mika rahoton ana tambayar su kan sahihincin rahotannin.

ADVERTISEMENT

Yayin da yake jawabi ga kungiyoyin farar hula, Yakubu ya ce, “Da yawa daga cikinku da suka gabatar da rahotonsu, har yanzu wasu masu sa ido da aka amince da su ba su yi haka ba a zabukan da ya gabata da zabukan cike gibi da kuma zaben fitar da gwani.

“Don haka zan iya yin amfani da wannan damar don tunatar da wadanda har yanzu ba su gabatar da rahoton bincikensu ba cewa ya zama dole su bayar idan suna so a kara ba su damar sa ido a zaben da za a yi nan gaba.”

LABARAI MASU NASABA

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

Da yake zantawa da LEADERSHIP, ko’odinetan gidauniyar samar da ci gaba mai dorewa, Jude Uzoma, ya yarda cewa rahotannin da wasu kungiyoyin sa ido kan zabuka na hada kai da ‘yan siyasa wajen bayar da rahotonnin da ba su dace ba.

Uzoma ya ce, kamar yadda cin hanci da rashawa ya mamaye dukkan bangarori na rayuwar al’ummar Nijeriya, haka ma yake tasiri wajen sa ido a harkokin zabe.

“Kamar yadda mutane ke cewa, cin hanci da rashawa yana dukkanin bangarorin rayuwarmu, tun daga addini, tattalin arziki, siyasa, kasuwanci da duk wani abu.

“Babu wanda ya kubuta daga cin hanci da rashawa, ciki har da kungiyoyin farar hula da ke aiki da hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) a matsayin masu sa ido na kasashen waje ko kuma masu sa ido na cikin gida. Wasu kungiyoyin sa ido suna goyi bayan jam’iyyar PDP, yayin da wasu ke goyon bayan APC a lokacin zabe,” in ji shi.

Masana sun tabbatar da cewa masu saka ido a zabe suna da matukar tasiri wajen gudanar da sahihin zabe a Nijeriya, wanda suke bayar da rahotanni inda aka yi dai-dai da inda ba a yi ba.

Rawar
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Masana Tattalin Arziki Sun Yi Watsi Da Rahoton NBS Kan Tattalin Arziki
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Alƙawarin Wa’adi Ɗaya Na Peter Obi Ya Raba Kawunan Ƴan Arewa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    ‘Yan Majalisar Wakilai 50 Da Suka Rasa Tikitin Takara A Zaɓen Fid Da Gwani Na APC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaɓen Fitar Da Gwani: APC Na Fuskantar Barazanar Tawaye

MASU ALAKA

Rawar
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

May 16, 2026
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

May 15, 2026
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Hadakar ‘Yan Adawa Ta Rushe Yayin Da Tikitin Takarar Shugaban Kasa Ya Raba Kan Shugabannin ADC

May 9, 2026
Next Post
Sin Ta Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Danyen Aikin Dake Barazanar Jefa Yankin Cikin Wani Bala’i

Sin Ta Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Danyen Aikin Dake Barazanar Jefa Yankin Cikin Wani Bala’i

LABARAI MASU NASABA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.