• English
  • Business News
Wednesday, October 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Farashin Raguna Ya Tashi, An Samu Ragon Miliyan 1 Kaduna

by Abubakar Sulaiman
1 year ago
Rago

Yayin da babbar Sallah ke gabatowa, farashin dabbobin hadaya a jihar Kaduna ya yi tashin gwauron zabi, wanda ke nuna ƙalubalen tattalin arziki. Bikin sallar da ake yi da yankan dabbobi domin tunawa da yadda Annabi Ibrahim ya yi sadaukarwa da dansa domin Allah, yana zama nauyi ga mutane da yawa a fannin kudi. A kasuwar dabbobi ta Otal ɗin Dubar, farashin Ragunan ya tashi sosai.

Musa Aliyu, mai sayar da Rago, ya bayyana cewa, Ragon da farashinsa ya kai Naira ₦100,000 a shekarar da ta gabata, yanzu yana kai wa ₦200,000 zuwa ₦250,000.

Matsakaitan Raguna, a baya ₦120,000, yanzu suna tsakanin ₦400,000 zuwa ₦600,000. Manyan Raguna, a da suna kan ₦700,000 sun haura zuwa ₦900,000 zuwa Naira miliyan ɗaya. Ana sayar da ƙananan raguna kan Naira ₦70,000 zuwa ₦80,000.

  • Idan Mace Ta Yi Barin Cikin Wata Biyu, Za Ta Dakatar Da Yin Sallah?
  • Gwamna Radda Ya Amince Da Bai Wa Ma’aikata N15,000 A Matsayin Goron Sallah

Masu sayar da dabbobi irin su Hassan Mohammed sun koka da ƙarancin  masu saye da aka samu saboda tsadar rayuwa. Ya ƙara da cewa an samu ƙarin kuɗin ne daga masu kawo dabbobin da kuma tsadar abincinsu, wanda a yanzu farashinsa ya kai Naira ₦20,000 zuwa Naira ₦25,000 idan aka kwatanta da Naira ₦10,000 a baya.

Duk da irin wannan tsadar, wasu masu saye irin su Mohammed Idris, na ganin dole su sayi raguna saboda al’adu da addini, duk kuwa da ƙarancin kudi a hannun mutane.

LABARAI MASU NASABA

Majalisar Wakilai Ta Amince Da Bukatar Amso Bashin Dala Biliyan 2.34 A Kasuwar Jari Ta Duniya

Kotu Ta Umarci Ƙwace Dala 49,700 Daga Tsohon Jami’in INEC

Mazauna yankin sun bayyana takaicinsu dangane da tashin gwauron zabin dabbobin layyar, saboda fargabar cewa za a jefa iyalai da dama cikin matalauta a bukukuwan Sallah na bana.

Musa Yahaya, ma’aikaci ne mai ‘ya’ya bakwai, ya bayyana irin wahalhalun da ake fuskanta a fannin tattalin arziki. Ya ce hatta kayan masarufi kamar fatun buhu sun yi tsada.

Yahaya ya yi kira ga gwamnati da ta shiga tsakani domin rage wa talakawan Najeriya raɗaɗin tattalin arziƙi, saboda hauhawar farashin kayayyaki na kara sanya rayuwar yau da kullum cikin wahala.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

majalisar kasa
Labarai

Majalisar Wakilai Ta Amince Da Bukatar Amso Bashin Dala Biliyan 2.34 A Kasuwar Jari Ta Duniya

October 29, 2025
Kotu Ta Umarci Ƙwace Dala 49,700 Daga Tsohon Jami’in INEC
Labarai

Kotu Ta Umarci Ƙwace Dala 49,700 Daga Tsohon Jami’in INEC

October 29, 2025
COAS Shaibu Ya Sha Alwashin Murƙushe ‘Yan Ta’addar Lakurawa 
Labarai

COAS Shaibu Ya Sha Alwashin Murƙushe ‘Yan Ta’addar Lakurawa 

October 29, 2025
Next Post
Kasar Sin Ta Gada Tare Da Raya Al’Adun Da Suka Shafi Bikin Gargajiya Na Duanwu 

Kasar Sin Ta Gada Tare Da Raya Al’Adun Da Suka Shafi Bikin Gargajiya Na Duanwu 

LABARAI MASU NASABA

majalisar kasa

Majalisar Wakilai Ta Amince Da Bukatar Amso Bashin Dala Biliyan 2.34 A Kasuwar Jari Ta Duniya

October 29, 2025
An Samu Ingantuwar Yanayin Iska Da Ruwa Cikin Watanni 9 Na Farkon Bana A Sin

An Samu Ingantuwar Yanayin Iska Da Ruwa Cikin Watanni 9 Na Farkon Bana A Sin

October 29, 2025
Kotu Ta Umarci Ƙwace Dala 49,700 Daga Tsohon Jami’in INEC

Kotu Ta Umarci Ƙwace Dala 49,700 Daga Tsohon Jami’in INEC

October 29, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kara Kyautata Tsarin Kare Muradun Al’umma A Bangaren Shari’a

Yadda Kasar Sin Ke Kara Kyautata Tsarin Kare Muradun Al’umma A Bangaren Shari’a

October 29, 2025
COAS Shaibu Ya Sha Alwashin Murƙushe ‘Yan Ta’addar Lakurawa 

COAS Shaibu Ya Sha Alwashin Murƙushe ‘Yan Ta’addar Lakurawa 

October 29, 2025
Binciken ‘Yan Sanda Kan Wanda Ake Zargi Da Tawayen “‘Yancin Kan Taiwan” Mataki Ne Na Adalci Don Kare Hadin Kan Kasa

Binciken ‘Yan Sanda Kan Wanda Ake Zargi Da Tawayen “‘Yancin Kan Taiwan” Mataki Ne Na Adalci Don Kare Hadin Kan Kasa

October 29, 2025
Afuwar Tinubu Ga Fursunoni: Saura Ƙasa Da Shekaru 6 Maryam Sanda Ta Shaƙi Iskar ‘Yanci

Afuwar Tinubu Ga Fursunoni: Saura Ƙasa Da Shekaru 6 Maryam Sanda Ta Shaƙi Iskar ‘Yanci

October 29, 2025
Xi Jinping Zai Gana Da Donald Trump

Xi Jinping Zai Gana Da Donald Trump

October 29, 2025
Gwamnatin Rikon Kwarya: Shirin DSS Ne Na Damke Atiku Da Peter Obi Kafin Rantsar Da Tinubu

DSS Ta Kama Wani Matashi Da Ya Yi Kira A Yi Juyin Mulki A Kafofin Sada Zumunta

October 29, 2025
An Kashe Ɗan Sanda Da Ɗan Hakimi A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Gombe

An Kashe Ɗan Sanda Da Ɗan Hakimi A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Gombe

October 29, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.