• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Fasinjojin Jirgin Kasan Abuja-Kaduna Sun Roki Manyan Kasashen Duniya Su Kawo Musu Dauki 

by Sadiq
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Fasinjojin Jirgin Kasan Abuja-Kaduna Sun Roki Manyan Kasashen Duniya Su Kawo Musu Dauki 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ragowar fasinjojin da aka yi garkuwa da su a jirgin kasan Abuja zuwa Kaduna sun yi kira ga manyan kasashen duniya da su taimaka su shiga tsakani a kan halin da suke ciki da kuma ganin an ceto su daga hannun wadanda suka yi garkuwa da su.

Idan za a iya tunawa, ‘yan ta’adda sun kai wa jirgin kasan Abuja zuwa Kaduna hari a daren ranar Litinin 28 ga watan Maris, 2022, inda fasinjoji tara suka mutu, sannan suka yi awon gaba da wasu da dama yayin da aka ceto wasu da dama da raunuka.

  • Me Ya Sa Kano Pillars Ta Fada Ajin Gajiyayyu A Nijeriya?
  • A Nijeriya Idan Ka Ce Za Ka Rike Aikin Gwamnati Shi Kadai Akwai Kalubale – Fatima (Adon Gari)

Mamu wanda ya jagoranci yin sulhu har aka sako mutane 18 daga cikin fasinjojin rukuni na biyu. Sun saki mutane 11 a ranar 11 ga Yuni, 2022, sai kuma suka sake sakin wani rukuni na fasinjojin bakwai a ranar 9 ga Yuli, 2022.

‘Yan ta’addan sun yi barazanar kashe sauran wadanda ke hannunsu, matukar gwamnatin tarayya ba ta biya musu bukatunsu ba, ciki har da bukatar sakin mayakansu da ake tsare da wadanda aka samu da laifi da kuma wadanda ke jiran hukuncin shari’a.

Daga bisani ‘yan ta’addan na Boko-Haram sun kai hari gidan yarin Kuje da ke Abuja, inda suka saki daruruwan fursunonin da suka hada da wasu 69 daga cikinsu da ke fuskantar tuhumar ta’addanci.

Labarai Masu Nasaba

Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu

Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

Da yake mayar da martani kan harin, Mamu, ya sanar da janye wa daga tattaunawar neman sakin fasinjojin jirgin da aka sace, inda ya bayyana rashin kulawa daga gwamnatin tarayya ke nunawa da kuma barazana ga rayuwarsa da yake fuskanta.

Ya kuma zargi gwamnatin tarayya gaza yin katabus game da bayanan sirri kan yiwuwar harin na gidan yarin Kuje.

A wani sabon faifan bidiyo da ‘yan ta’addan suka fitar a ranar Asabar, wanda LEADERSHIP ta samu, an ga yadda ‘yan ta’addan ke yi wa wadanda aka yi garkuwa da su bulala, wadanda suka hada da manya maza da mata da kananan yara.

A cikin bidiyon mai tsawon mintuna 10.51, ‘yan ta’addan sun yi barazanar yin garkuwa da shugaban kasa Muhammadu Buhari da kuma gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai tare da kashe su.

‘Yan ta’addan sun kuma sha alwashin cewa za su ruguza kasar nan, su kashe sauran fasinjojin da ke hannunsu sannan su sayar da sauran.

Daya daga cikin ‘yan ta’addan ya yi barazanar cewa idan har gwamnati ba ta biya musu bukatunsu ba, to za su mayar da yankin tamkar mahauta.

“Wannan shi ne sakonmu ga gwamnatin Nijeriya kuma kamar yadda kuka ga wadannan mutane a nan, da yardar Allah za ku ga shugabanninku; Sanatoci da gwamnoninku za su zo gabanmu. Wadannan da kuke gani a nan za mu rike wasu a matsayin bayi, mu sayar da su kamar yadda Imaminmu ya fada muku a baya,” in ji shi.

Bayan ‘yan ta’addan sun yi magana, wasu daga cikin fasinjojin da aka sace sun roki gwamnatin tarayya da manyan kasashen duniya irin su; Faransa, Amurka, Ingila da sauransu da su kawo musu dauki.

Sun koka da halin da suke ciki tare da zargin gwamnati da rashin nuna kulawa, inda suka kara da cewa wadanda suka sace su sun fi mutunta su fiye da gwamnatin Nijeriya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan ta'addaBuhariEl-RufaiFasinjojiGarkuwaJirgin Kasan Abuja-KadunaYan bindiga
ShareTweetSendShare
Previous Post

Me Ya Sa Kano Pillars Ta Fada Ajin Gajiyayyu A Nijeriya?

Next Post

Duk Abinda Na Yi A Rayuwata Bazata Ne – Obasanjo

Related

Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu
Manyan Labarai

Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu

5 hours ago
Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki
Manyan Labarai

Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

16 hours ago
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka
Manyan Labarai

Ganduje Ya Ajiye Shugabancin Jam’iyyar APC

18 hours ago
Ƴan Majalisa Na Binciken Cibiyoyin Ci Gaban Masana’antu 30 Da Aka Yi Watsi Da Su
Manyan Labarai

Ƴan Majalisa Na Binciken Cibiyoyin Ci Gaban Masana’antu 30 Da Aka Yi Watsi Da Su

23 hours ago
Tinubu Ya Sasanta Wike, Fubara, Da Ƴan Majalisar Ribas
Manyan Labarai

Tinubu Ya Sasanta Wike, Fubara, Da Ƴan Majalisar Ribas

24 hours ago
Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tabbatar Da Kisan Jami’anta A Kaduna Da Neja
Manyan Labarai

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tabbatar Da Kisan Jami’anta A Kaduna Da Neja

1 day ago
Next Post
Duk Abinda Na Yi A Rayuwata Bazata Ne – Obasanjo

Duk Abinda Na Yi A Rayuwata Bazata Ne - Obasanjo

LABARAI MASU NASABA

Za a Binne Ɗantata A Madina, Za Ai Yi Sallar Ga’ibi A Kano

Za a Binne Ɗantata A Madina, Za Ai Yi Sallar Ga’ibi A Kano

June 28, 2025
Me Ya Sa Syria Ta Bari Ana Amfani Da Sararin Samaniyarta Wajen Kai Wa Iran Hari?

Me Ya Sa Syria Ta Bari Ana Amfani Da Sararin Samaniyarta Wajen Kai Wa Iran Hari?

June 28, 2025
Wace Nahiya Ce Ta Fi Iya Ƙwallon Ƙafa Tsakanin Turai Da Kudancin Amurka?

Wace Nahiya Ce Ta Fi Iya Ƙwallon Ƙafa Tsakanin Turai Da Kudancin Amurka?

June 28, 2025
Ƙasashen Afrika 10 Da Suka Fi Girman Kasafin Kudi A 2025

Ƙasashen Afrika 10 Da Suka Fi Girman Kasafin Kudi A 2025

June 28, 2025
Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato

Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato

June 28, 2025
Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu

Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu

June 28, 2025
Hoton Tallan Taliyar Indomie

Indomie Ta Kaddamar Da Shirin Gangamin Abinci Mai Gina Jiki Na ‘Ingantaccen Abinci Domin Nasara’

June 28, 2025
Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

June 27, 2025
Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

June 27, 2025
Sojojin DRC: Ƴan Tawayen M23 Sun Kashe Fararen Hula 17

Sojojin DRC: Ƴan Tawayen M23 Sun Kashe Fararen Hula 17

June 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.