• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Fasinjojin Jirgin Kasan Abuja-Kaduna Sun Roki Manyan Kasashen Duniya Su Kawo Musu Dauki 

by Sadiq
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Fasinjojin Jirgin Kasan Abuja-Kaduna Sun Roki Manyan Kasashen Duniya Su Kawo Musu Dauki 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ragowar fasinjojin da aka yi garkuwa da su a jirgin kasan Abuja zuwa Kaduna sun yi kira ga manyan kasashen duniya da su taimaka su shiga tsakani a kan halin da suke ciki da kuma ganin an ceto su daga hannun wadanda suka yi garkuwa da su.

Idan za a iya tunawa, ‘yan ta’adda sun kai wa jirgin kasan Abuja zuwa Kaduna hari a daren ranar Litinin 28 ga watan Maris, 2022, inda fasinjoji tara suka mutu, sannan suka yi awon gaba da wasu da dama yayin da aka ceto wasu da dama da raunuka.

  • Me Ya Sa Kano Pillars Ta Fada Ajin Gajiyayyu A Nijeriya?
  • A Nijeriya Idan Ka Ce Za Ka Rike Aikin Gwamnati Shi Kadai Akwai Kalubale – Fatima (Adon Gari)

Mamu wanda ya jagoranci yin sulhu har aka sako mutane 18 daga cikin fasinjojin rukuni na biyu. Sun saki mutane 11 a ranar 11 ga Yuni, 2022, sai kuma suka sake sakin wani rukuni na fasinjojin bakwai a ranar 9 ga Yuli, 2022.

‘Yan ta’addan sun yi barazanar kashe sauran wadanda ke hannunsu, matukar gwamnatin tarayya ba ta biya musu bukatunsu ba, ciki har da bukatar sakin mayakansu da ake tsare da wadanda aka samu da laifi da kuma wadanda ke jiran hukuncin shari’a.

Daga bisani ‘yan ta’addan na Boko-Haram sun kai hari gidan yarin Kuje da ke Abuja, inda suka saki daruruwan fursunonin da suka hada da wasu 69 daga cikinsu da ke fuskantar tuhumar ta’addanci.

Labarai Masu Nasaba

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

Da yake mayar da martani kan harin, Mamu, ya sanar da janye wa daga tattaunawar neman sakin fasinjojin jirgin da aka sace, inda ya bayyana rashin kulawa daga gwamnatin tarayya ke nunawa da kuma barazana ga rayuwarsa da yake fuskanta.

Ya kuma zargi gwamnatin tarayya gaza yin katabus game da bayanan sirri kan yiwuwar harin na gidan yarin Kuje.

A wani sabon faifan bidiyo da ‘yan ta’addan suka fitar a ranar Asabar, wanda LEADERSHIP ta samu, an ga yadda ‘yan ta’addan ke yi wa wadanda aka yi garkuwa da su bulala, wadanda suka hada da manya maza da mata da kananan yara.

A cikin bidiyon mai tsawon mintuna 10.51, ‘yan ta’addan sun yi barazanar yin garkuwa da shugaban kasa Muhammadu Buhari da kuma gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai tare da kashe su.

‘Yan ta’addan sun kuma sha alwashin cewa za su ruguza kasar nan, su kashe sauran fasinjojin da ke hannunsu sannan su sayar da sauran.

Daya daga cikin ‘yan ta’addan ya yi barazanar cewa idan har gwamnati ba ta biya musu bukatunsu ba, to za su mayar da yankin tamkar mahauta.

“Wannan shi ne sakonmu ga gwamnatin Nijeriya kuma kamar yadda kuka ga wadannan mutane a nan, da yardar Allah za ku ga shugabanninku; Sanatoci da gwamnoninku za su zo gabanmu. Wadannan da kuke gani a nan za mu rike wasu a matsayin bayi, mu sayar da su kamar yadda Imaminmu ya fada muku a baya,” in ji shi.

Bayan ‘yan ta’addan sun yi magana, wasu daga cikin fasinjojin da aka sace sun roki gwamnatin tarayya da manyan kasashen duniya irin su; Faransa, Amurka, Ingila da sauransu da su kawo musu dauki.

Sun koka da halin da suke ciki tare da zargin gwamnati da rashin nuna kulawa, inda suka kara da cewa wadanda suka sace su sun fi mutunta su fiye da gwamnatin Nijeriya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan ta'addaBuhariEl-RufaiFasinjojiGarkuwaJirgin Kasan Abuja-KadunaYan bindiga
ShareTweetSendShare
Previous Post

Me Ya Sa Kano Pillars Ta Fada Ajin Gajiyayyu A Nijeriya?

Next Post

Duk Abinda Na Yi A Rayuwata Bazata Ne – Obasanjo

Related

UTME
Manyan Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

2 hours ago
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu
Manyan Labarai

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

8 hours ago
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya
Manyan Labarai

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

13 hours ago
Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte
Manyan Labarai

Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

17 hours ago
Ko Kanawa Za Su Yafe Wa Ganduje?
Manyan Labarai

Kotu Ta Ce Za A Ci Gaba Da Shari’ar Ganduje Kan Zargin Aikata Rashawa A Kano

18 hours ago
Gwamnan Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar
Manyan Labarai

Gwamnan Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar

1 day ago
Next Post
Duk Abinda Na Yi A Rayuwata Bazata Ne – Obasanjo

Duk Abinda Na Yi A Rayuwata Bazata Ne - Obasanjo

LABARAI MASU NASABA

UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.