• English
  • Business News
Thursday, September 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Fasinjojin Jirgin Kasan Abuja-Kaduna Sun Roki Manyan Kasashen Duniya Su Kawo Musu Dauki 

by Sadiq
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Fasinjojin Jirgin Kasan Abuja-Kaduna Sun Roki Manyan Kasashen Duniya Su Kawo Musu Dauki 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ragowar fasinjojin da aka yi garkuwa da su a jirgin kasan Abuja zuwa Kaduna sun yi kira ga manyan kasashen duniya da su taimaka su shiga tsakani a kan halin da suke ciki da kuma ganin an ceto su daga hannun wadanda suka yi garkuwa da su.

Idan za a iya tunawa, ‘yan ta’adda sun kai wa jirgin kasan Abuja zuwa Kaduna hari a daren ranar Litinin 28 ga watan Maris, 2022, inda fasinjoji tara suka mutu, sannan suka yi awon gaba da wasu da dama yayin da aka ceto wasu da dama da raunuka.

  • Me Ya Sa Kano Pillars Ta Fada Ajin Gajiyayyu A Nijeriya?
  • A Nijeriya Idan Ka Ce Za Ka Rike Aikin Gwamnati Shi Kadai Akwai Kalubale – Fatima (Adon Gari)

Mamu wanda ya jagoranci yin sulhu har aka sako mutane 18 daga cikin fasinjojin rukuni na biyu. Sun saki mutane 11 a ranar 11 ga Yuni, 2022, sai kuma suka sake sakin wani rukuni na fasinjojin bakwai a ranar 9 ga Yuli, 2022.

‘Yan ta’addan sun yi barazanar kashe sauran wadanda ke hannunsu, matukar gwamnatin tarayya ba ta biya musu bukatunsu ba, ciki har da bukatar sakin mayakansu da ake tsare da wadanda aka samu da laifi da kuma wadanda ke jiran hukuncin shari’a.

Daga bisani ‘yan ta’addan na Boko-Haram sun kai hari gidan yarin Kuje da ke Abuja, inda suka saki daruruwan fursunonin da suka hada da wasu 69 daga cikinsu da ke fuskantar tuhumar ta’addanci.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Da yake mayar da martani kan harin, Mamu, ya sanar da janye wa daga tattaunawar neman sakin fasinjojin jirgin da aka sace, inda ya bayyana rashin kulawa daga gwamnatin tarayya ke nunawa da kuma barazana ga rayuwarsa da yake fuskanta.

Ya kuma zargi gwamnatin tarayya gaza yin katabus game da bayanan sirri kan yiwuwar harin na gidan yarin Kuje.

A wani sabon faifan bidiyo da ‘yan ta’addan suka fitar a ranar Asabar, wanda LEADERSHIP ta samu, an ga yadda ‘yan ta’addan ke yi wa wadanda aka yi garkuwa da su bulala, wadanda suka hada da manya maza da mata da kananan yara.

A cikin bidiyon mai tsawon mintuna 10.51, ‘yan ta’addan sun yi barazanar yin garkuwa da shugaban kasa Muhammadu Buhari da kuma gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai tare da kashe su.

‘Yan ta’addan sun kuma sha alwashin cewa za su ruguza kasar nan, su kashe sauran fasinjojin da ke hannunsu sannan su sayar da sauran.

Daya daga cikin ‘yan ta’addan ya yi barazanar cewa idan har gwamnati ba ta biya musu bukatunsu ba, to za su mayar da yankin tamkar mahauta.

“Wannan shi ne sakonmu ga gwamnatin Nijeriya kuma kamar yadda kuka ga wadannan mutane a nan, da yardar Allah za ku ga shugabanninku; Sanatoci da gwamnoninku za su zo gabanmu. Wadannan da kuke gani a nan za mu rike wasu a matsayin bayi, mu sayar da su kamar yadda Imaminmu ya fada muku a baya,” in ji shi.

Bayan ‘yan ta’addan sun yi magana, wasu daga cikin fasinjojin da aka sace sun roki gwamnatin tarayya da manyan kasashen duniya irin su; Faransa, Amurka, Ingila da sauransu da su kawo musu dauki.

Sun koka da halin da suke ciki tare da zargin gwamnati da rashin nuna kulawa, inda suka kara da cewa wadanda suka sace su sun fi mutunta su fiye da gwamnatin Nijeriya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan ta'addaBuhariEl-RufaiFasinjojiGarkuwaJirgin Kasan Abuja-KadunaYan bindiga
ShareTweetSendShare
Previous Post

Me Ya Sa Kano Pillars Ta Fada Ajin Gajiyayyu A Nijeriya?

Next Post

Duk Abinda Na Yi A Rayuwata Bazata Ne – Obasanjo

Related

Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis
Manyan Labarai

Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

4 hours ago
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

5 hours ago
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB
Manyan Labarai

Sojoji Sun Cafke Babban Kwamandan IPOB

8 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

17 hours ago
Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas
Manyan Labarai

Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

22 hours ago
NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025
Da ɗumi-ɗuminsa

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

1 day ago
Next Post
Duk Abinda Na Yi A Rayuwata Bazata Ne – Obasanjo

Duk Abinda Na Yi A Rayuwata Bazata Ne - Obasanjo

LABARAI MASU NASABA

An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Kama Sojan Gona Da Motocin Sata 3 A Jigawa

September 18, 2025
Yadda Muka Zama Bayin ‘Yan Bindiga -Mazaunin Wani Kauye

’Yan Bindiga Sun Sako Ma’aurata A Katsina Bayan Karɓar N50m A Matsayin Kuɗin Fansa

September 18, 2025
Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

September 18, 2025
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

September 18, 2025
’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja

’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja

September 18, 2025
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

Sojoji Sun Cafke Babban Kwamandan IPOB

September 18, 2025
Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

September 17, 2025
Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

September 17, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

September 17, 2025
Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

September 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.