• English
  • Business News
Friday, June 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Fatara Da Talauci Na Yi Wa ‘Yan Nijeriya Miliyan 13 Barazanar Fadawa Kangin Talauci A 2025 — Rahoto

by Khalid Idris Doya and Sulaiman
4 months ago
in Labarai
0
Fatara Da Talauci Na Yi Wa ‘Yan Nijeriya Miliyan 13 Barazanar Fadawa Kangin Talauci A 2025 — Rahoto
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hauhawar farashin kayayyakin masarufi, tashin kudin ruwa da kuma rugujewar darajar naira ka iya kwasan wasu karin ‘yan Nijeriya miliyan 13 ya jefa su cikin kangin talauci da fatara a shekarar 2025, a cewar rahoton ‘Pricewaterhouse Coopers (PwC) International Limited’.

Rahoton mai taken: Kasafin Nijeriya na 2025 da yanayin tattalin arzikinta, wanda PwP ta wallafa a shafinta: www.pwc.com ta lura da matsaloli da kalubalen tattalin arziki da Nijeriya ke fuskanta.

  • An Samu Ci Gaba A Bangaren Kayayyakin Da Sin Ta Fitar Zuwa Kasashe Da Yankuna 160 A 2024
  • Gwamnati Ta Sake Haɗa Tubabbun Mayaƙan Boko Haram 5,000 Da Iyalansu

Rahoton ya yi nuni da halin tattalin arzikin Nijeriya da dora shi a kan mizanin tashin farashin kayan masarufi da tsadar rayuwa da matsi da ake kara shiga na kan gaba wajen jefa jama’a cikin talauci, lamarin da ke dagula sha’anin ‘yan kasar musamman yanayin walwalarsu.

Rahoton na PwC ya yi harsashen karuwar matalauta sosai a Nijeriya ne bisa dogara da rahoton kididdigar talauci na kasa da kasa (MPI) ta 2022.

Haka kuma rahoton ya shelanta cewa ‘yan Nijeriya miliyan 133 a halin yanzu wato kaso sama da 60 na yawan al’umman Nijeriya sun kasance matalauta ne sosai da suke da karancin samun ababen more rayuka kamar kiwon lafiya, ilimi, ayyukan yi, da kuma karancin yanayin rayuwa mai inganci.

Labarai Masu Nasaba

Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano

‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 

A sabon rahoton 2024 da Bankin Duniya ya fitar, ya ce a kalla ‘yan Nijeriya miliyan 129 ne suke rayuwa cikin talauci, da ke nuni da cewa an samu kari fadawar mutane cikin talauci daga kaso 40.1 a 2018 zuwa kaso 56 a 2024.

Tabarbarewar tattalin arzikin da ake fama da ita tare da karuwar yawan jama’a cikin sauri, ya tsananta matakan talauci. Raguwar tattalin arziki kasar ga kowane mutum, wanda ya ragu da kashi 25.04 cikin dari daga dala 2,162.6 a 2022 zuwa dala 1,621.1 a 2023, ya kara jaddada raguwar karfin saye da kuma tabarbarewar rayuwa bisa ga rahoton PWC.

Tashin farashin kayayyaki shi ne ke kan gaba wajen janyo wa tattalin arzikin Nijeriya matsaloli. Zuwa watan Disamban 2024, kason hauhawar farashin kayan masarufi ya kai zuwa kaso 34.8 lamarin da ke kara lafta wa ‘yan Nijeriya damuwuwi musamman na yadda suke kasa iya sayen ababen bukata kama daga kayan abinci, gidaje da kuma kiwon lafiya.

Daga watan Janairu zuwa Satumban 2024, sufuri da kayan abinci su ne aka samu karuwa sosai a kansu. Tashin kudin man fetur shi ne ya janyo dukkanin tashin kudin sufuri da na kayan abinci.

Karuwar farashin kayan abinci na nuni da barazanar adana abinci da ake ciki, wanda ya shafi ‘yan Nijeriya miliyan 25.1 a 2024. Sai dai rahoton na PwP ya yi gargadin cewa adadin zai iya karuwa zuwa miliyan 33.1 a 2025 muddin hauhawar farashin ya ci gaba da tashi.

Duk da cewa gwamnatin tarayya ta biyo da wasu tsare-tsaren da take ganin za su saukaka kamar karancin albashi, sai dai kaso 4.1 cikin 100 kacal na ‘yan kasar ne ke aiki, lamarin da ke nuni da cewa hakan ba zai yi tasiri ba.

Masu ruwa da tsaki sun lura da cewa lamarin karuwar masu fadawa cikin talauci lamari ne da ke bukatar daukan matakan gaggawa na shawo kan matsalolin da suka dabaibaye tattalin arziki. Duk da karuwar tattalin arzikin Nijeriya na GDP da kaso 3.0 a 2024 akwai bukatar kara himma a 2025.

Rahoton ya yi kira da a samar da ingantattun matakan kawar da fatara, gami da sa kaimi ga al’umma da gyare-gyaren tsari don magance hauhawar farashin kayayyaki da bunkasar tattalin arziki mai dorewa.

A cewar rahoton, idan ba a dauki kwakkwaran mataki ba, matsalar tattalin arzikin da miliyoyin ‘yan Nijeriya ke fuskanta zai kara tabarbarewa tare da jefa dimbin iyalai cikin fatara da kuma kawo cikas ga ci gaban kasar na dogon lokaci.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ana ɗar ɗar Kan Mutuwar Sojoji Bayan Da Mota Ta Kwace A Legas

Next Post

Gwamnan Gombe Ya Jaddada Aniyarsa Ta Inganta Fannin Shari’a

Related

Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano
Labarai

Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano

8 hours ago
‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 
Labarai

‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 

10 hours ago
Bukola Saraki Ya Tallafawa Al’ummar Mokwa Da Gudunmawar Kuɗi
Labarai

Bukola Saraki Ya Tallafawa Al’ummar Mokwa Da Gudunmawar Kuɗi

10 hours ago
Wannan Kyakkyawan Tunani Ya Shafa Ma Hamadar Sahara Launin Kore
Ra'ayi Riga

Wannan Kyakkyawan Tunani Ya Shafa Ma Hamadar Sahara Launin Kore

12 hours ago
Hukumar kashe gobara
Manyan Labarai

An Samu Asarar Dukiya ta Miliyan ₦273, Tare Da Mutuwar Mutum 5 A Kano – Hukuma

14 hours ago
Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafa Wa Yekuwar Rigakafin Cutar Ƙyandar Jamus
Labarai

Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafa Wa Yekuwar Rigakafin Cutar Ƙyandar Jamus

14 hours ago
Next Post
gombe

Gwamnan Gombe Ya Jaddada Aniyarsa Ta Inganta Fannin Shari'a

LABARAI MASU NASABA

Shugabannin Sin Da Amurka Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

Shugabannin Sin Da Amurka Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

June 6, 2025
Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

June 5, 2025
Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai

Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai

June 5, 2025
Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano

Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano

June 5, 2025
Ma’aikatar Harkokin Waje: Kasar Sin Ta Kasance Gwarzuwa Wajen Samar Da Ci Gaba Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba

Ma’aikatar Harkokin Waje: Kasar Sin Ta Kasance Gwarzuwa Wajen Samar Da Ci Gaba Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba

June 5, 2025
‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 

‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 

June 5, 2025
Lambar “-1.5” Gargadi Ce Da Al’ummar Duniya Ke Yi Ga Azzaluma 

Lambar “-1.5” Gargadi Ce Da Al’ummar Duniya Ke Yi Ga Azzaluma 

June 5, 2025
Sabbin Matakan Amurka Game Da Masu Shiga Kasar Sun Ci Karo Da Ikirarinta Na Mutunta Hakkokin Bil Adama

Sabbin Matakan Amurka Game Da Masu Shiga Kasar Sun Ci Karo Da Ikirarinta Na Mutunta Hakkokin Bil Adama

June 5, 2025
Bukola Saraki Ya Tallafawa Al’ummar Mokwa Da Gudunmawar Kuɗi

Bukola Saraki Ya Tallafawa Al’ummar Mokwa Da Gudunmawar Kuɗi

June 5, 2025
Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa Barcelona

Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa Barcelona

June 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.