• English
  • Business News
Sunday, October 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Fataucin Yara: ‘Yansanda Sun Ceto Jarirai 3, Sun Cafke Mutane 16 A Gombe

by Sadiq
2 years ago
Gombe

Rundunar ‘yansandan Jihar Gombe ta ceto jarirai uku tare da cafke wasu mutane 16 da ake zargi da laifin safarar yara a jihar.

Kakakin rundunar ‘yansandan jihar, ASP Mahid Abubakar, ne ya bayyana haka a lokacin da yake zantawa da manema labarai a madadin kwamishinan ‘yansandan jihar, Hayatu Usman a Gombe a ranar Laraba.

  • CBN Ya Nada Sabbin Shugabannin Gudanarwar Wasu Bankuna
  • Bangaren Layin Dogo Na Sin Ya Yi Jigilar Fasinjoji Mafi Yawa A 2023

Abubakar, ya ce an shigar karar ne a karshen mako biyo bayan rahoton sirri da aka samu daga mutanen yankin Barunde na Jihar Gombe.

Ya ce an ceto jarirai uku daga hannun wadanda ake zargin, yayin da wasu biyu kuma aka yi safarar su daga jihar.

A cewarsa, daya daga cikin jariran da aka yi safarar su a yanzu yana Legas, yayin da dayan kuma an ceto shi a Anambra.

LABARAI MASU NASABA

Tornadoes Ta Doke Pillars A Wasan Farko Na Babaganaru

Gwarzon Kamfanin Samar Da Kayayyakin Gida Na Mai Da Gas Na Shekarar 2025 Kamfanin GEIL

Ya bayyana cewa ana kokarin kwato sauran jariran biyu da kuma mayar da su jihar.

Abubakar, ya bayyana cewa, yayin bincike, an gano cewa an sayar da daya daga cikin jariran kan Naira 400,000.

Ya ce an sayar da jaririn ga wani mutum a jihar tare da hadin gwiwar wani ma’aikaci a jihar.

A cewar kakakin rundunar ‘yansandan, rundunar ta samu rahoton sirri kan daya daga cikin iyayen da suka sayar da dansu ga wadanda ake zargin.

“Wannan wani laifi ne na hada baki da fataucin yara inda aka kama wata Khadija Manzo da wasu 15 bayan rahoton sirri da aka samu daga al’ummar Barundde a karshen mako.

“A wani lokaci a shekarar da ta gabata, wata Khadija Manzo da wasu 15 sun shiga harkar sayar da jarirai.

“Da samun rahoton, jami’an tsaro na Lowcost Division sun gudanar da bincike wanda ya kai ga kama Manzo, da sauran wadanda ake zargi,” in ji shi.

Abubakar ya ce bincike ya nuna cewa Manzo ya sayar da jarirai biyu ga Ukamaka Ugwu a lokuta daban-daban.

Ya ce an kama wasu da ake zargi da hannu wajen aikata laifin.

Da yake karin bayani, Abubakar ya ce: “Bincike ya nuna cewa ta sayar da wani jariri kan Naira 400,000 ga wata Tina Raphael.

“Kuma ta bayar da Naira 200,000 ga wani Haruna Abubakar, wanda ke aiki da gwamnatin Gombe.

“Yahaya Suleiman ya karbi Naira 200,000 daga hannun ta ya bai wa Haruna Abubakar.

“Ukamaka Ugwu ya sayi yara biyu daya a halin yanzu yana Legas daya kuma a Anambra, amma ‘yansanda na kokarin ganin an dawo da jariran.”

Abubakar ya ce nan ba da jimawa ba za a gurfanar da wadanda ake zargin a gaban kotu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tornadoes Ta Doke Pillars A Wasan Farko Na Babaganaru
Wasanni

Tornadoes Ta Doke Pillars A Wasan Farko Na Babaganaru

October 26, 2025
Gwarzon Kamfanin Samar Da Kayayyakin Gida Na Mai Da Gas Na Shekarar 2025 Kamfanin GEIL
Manyan Labarai

Gwarzon Kamfanin Samar Da Kayayyakin Gida Na Mai Da Gas Na Shekarar 2025 Kamfanin GEIL

October 26, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji
Manyan Labarai

Gwarzon Ɗan Majalisa Na Shekarar 2025: Benjamin Okezie Kalu

October 26, 2025
Next Post
Ogun: Kotun Koli Ta Dakatar Da Karar Korar Abiodun

Ogun: Kotun Koli Ta Dakatar Da Karar Korar Abiodun

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Raba Wa Masu Ƙananan Sana’o’i Biliyan 75 Domin Bunƙasa Kasuwancinsu

October 26, 2025
Ɗan Majalisa Ya Ce Ba Zai Sake Takara Ba, Ya Sadaukar Da Ita Ga Matasa

Ɗan Majalisa Ya Ce Ba Zai Sake Takara Ba, Ya Sadaukar Da Ita Ga Matasa

October 26, 2025
Abin Da Ya Sa Aka Yi Watsi Da Tashar Jiragen Ruwa Ta Kan Tudu Da Ke Jihar Kaduna

Abin Da Ya Sa Aka Yi Watsi Da Tashar Jiragen Ruwa Ta Kan Tudu Da Ke Jihar Kaduna

October 26, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

‘Yansanda Sun Kama Wasu Mutum Biyu Da Ake Zargi Da Haɗa Baki Da ‘Yan Bindiga A Kano

October 26, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwamnatin Kaduna Tare Da  AUDA–NEPAD Sun Tallafa Wa Manoma 400 Da Kayan Noma

October 26, 2025
Tornadoes Ta Doke Pillars A Wasan Farko Na Babaganaru

Tornadoes Ta Doke Pillars A Wasan Farko Na Babaganaru

October 26, 2025
Gwarzon Kamfanin Samar Da Kayayyakin Gida Na Mai Da Gas Na Shekarar 2025 Kamfanin GEIL

Gwarzon Kamfanin Samar Da Kayayyakin Gida Na Mai Da Gas Na Shekarar 2025 Kamfanin GEIL

October 26, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwarzon Ɗan Majalisa Na Shekarar 2025: Benjamin Okezie Kalu

October 26, 2025
An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

October 25, 2025

Nafisa Abdullahi Aminu: Yarinyar Da Ta Ɗaukaka Darajar Nijeriya A Idon Duniya

October 25, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.