• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

FCDA Zata Rushe Duk Gine-Ginen Da Ke Kan Hanyoyin Ruwa A Abuja

by Muhammad
2 years ago
in Manyan Labarai
0
FCDA Zata Rushe Duk Gine-Ginen Da Ke Kan Hanyoyin Ruwa A Abuja
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Babban Sakataren Hukumar Raya Babban Birnin Tarayya Abuja (FCDA), Malam Shehu Ahmed, ya ce hukumar babban birnin tarayya Abuja za ta rusa dukkan gine-ginen da ke kan hanyoyin ruwa a fadin babban birnin kasar nan.

Ahmed ya bayyana hakan ne a wata sanarwa da ya fitar ranar Lahadi a Abuja.

  • Ambaliyar Ruwa: Mutum 1 Ya Mutu, An Ceto 4 A Abuja
  • Ambaliyar Ruwa Ta Shafi Mutum 24,714 A Abuja

Ya ce wasu gine-ginen na hana ruwa gudu ta hanyar da ta dace wanda ke haddasa ambaliya da aka samu a wasu sassan birnin.

“Mutane suna ta korafin cewa mu yi gaggawar daukar matakai don ceton rayuka. Kuma wannan shi ne abin da dole ne mu yi. Ba za mu iya kawar da kai kamar ba mu ga wannan matsala da mutane suka haifar da wadanda suka karya tsarin Abuja ba.”

” Gine-ginen da ke cikin rukunin gidaje na Trademore an yi musu alama da yawa don rushewa. An yi gargadin shekara bayan shekara amma mazauna wannan yankin suka ci gaba da yin kasada da rayukansu da na wasu.

Labarai Masu Nasaba

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

“Mun gaya wa mazauna Trademore su yi kaura. Yankin yana kan hanyar ruwa. Ambaliyar ruwa na iya zuwa a kowane lokaci. Sun san wannan amma suka yi ta zama da wannan matsalar tsawon shekaru. ”

Sakataren zartarwa hukumar, wanda shi ne shugaban kwamitin ayyuka na musamman akan rage ambaliyar ruwa, ya bayyana cewa za a rushe wani ofishin ‘yan sanda a Trademore da sauran gine-gine.

“Muna da ofishin ‘yan sanda a Trademore za a rushe tare da sauran gine-gine. Mun sanar da rundunar ‘yan sandan FCT kuma mun samar da wurin da ya dace domin gudanar da ayyukansu da kuma yaki da masu kunnan kashi.”

Sakataren zartarwa ya nuna cewa Trademore Estate ba shi da tsarin gini na FCDA da aka amince da shi kuma wuraren da ake ci gaba da samun ambaliya za a iya barin su don zaman wuraren shakatawa ba na zama ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AbujaAmbaliyar RuwaFCDARusau
ShareTweetSendShare
Previous Post

Shugaba Xi Jinping Ya Yi Kira Da A Kara Samun Nasarorin Sabbin kirkire-kirkire a JKS

Next Post

Kashin Farko Na Daliban Da Za Su Tafi Karatu Kasashen Waje Za Su Tafi A Watan Satumba – Abba

Related

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

21 hours ago
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano
Manyan Labarai

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

2 days ago
Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

2 days ago
Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi
Manyan Labarai

Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi

2 days ago
Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa
Manyan Labarai

Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa

2 days ago
Hukumar kashe gobara
Manyan Labarai

An Samu Asarar Dukiya ta Miliyan ₦273, Tare Da Mutuwar Mutum 5 A Kano – Hukuma

3 days ago
Next Post
Hajji 2023: Alhazan Nijeriya 6 Sun Rasu, 30 Na Da Tabin Hankali A Saudiyya

Kashin Farko Na Daliban Da Za Su Tafi Karatu Kasashen Waje Za Su Tafi A Watan Satumba – Abba

LABARAI MASU NASABA

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.