• English
  • Business News
Saturday, May 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

FCDA Zata Rushe Duk Gine-Ginen Da Ke Kan Hanyoyin Ruwa A Abuja

by Muhammad
2 years ago
in Manyan Labarai
0
FCDA Zata Rushe Duk Gine-Ginen Da Ke Kan Hanyoyin Ruwa A Abuja
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Babban Sakataren Hukumar Raya Babban Birnin Tarayya Abuja (FCDA), Malam Shehu Ahmed, ya ce hukumar babban birnin tarayya Abuja za ta rusa dukkan gine-ginen da ke kan hanyoyin ruwa a fadin babban birnin kasar nan.

Ahmed ya bayyana hakan ne a wata sanarwa da ya fitar ranar Lahadi a Abuja.

  • Ambaliyar Ruwa: Mutum 1 Ya Mutu, An Ceto 4 A Abuja
  • Ambaliyar Ruwa Ta Shafi Mutum 24,714 A Abuja

Ya ce wasu gine-ginen na hana ruwa gudu ta hanyar da ta dace wanda ke haddasa ambaliya da aka samu a wasu sassan birnin.

“Mutane suna ta korafin cewa mu yi gaggawar daukar matakai don ceton rayuka. Kuma wannan shi ne abin da dole ne mu yi. Ba za mu iya kawar da kai kamar ba mu ga wannan matsala da mutane suka haifar da wadanda suka karya tsarin Abuja ba.”

” Gine-ginen da ke cikin rukunin gidaje na Trademore an yi musu alama da yawa don rushewa. An yi gargadin shekara bayan shekara amma mazauna wannan yankin suka ci gaba da yin kasada da rayukansu da na wasu.

Labarai Masu Nasaba

Zulum Ya Haramta Sayar Da Fetur A Bama Don Yaƙi Da Ta’addanci

Bayan Cin Kamfanin META Tarar Dala Miliyan 220: Sun Yi Bazaranar Katse Kafofin Facebook, WhatsApp, Da Instagram A Nijeriya

“Mun gaya wa mazauna Trademore su yi kaura. Yankin yana kan hanyar ruwa. Ambaliyar ruwa na iya zuwa a kowane lokaci. Sun san wannan amma suka yi ta zama da wannan matsalar tsawon shekaru. ”

Sakataren zartarwa hukumar, wanda shi ne shugaban kwamitin ayyuka na musamman akan rage ambaliyar ruwa, ya bayyana cewa za a rushe wani ofishin ‘yan sanda a Trademore da sauran gine-gine.

“Muna da ofishin ‘yan sanda a Trademore za a rushe tare da sauran gine-gine. Mun sanar da rundunar ‘yan sandan FCT kuma mun samar da wurin da ya dace domin gudanar da ayyukansu da kuma yaki da masu kunnan kashi.”

Sakataren zartarwa ya nuna cewa Trademore Estate ba shi da tsarin gini na FCDA da aka amince da shi kuma wuraren da ake ci gaba da samun ambaliya za a iya barin su don zaman wuraren shakatawa ba na zama ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AbujaAmbaliyar RuwaFCDARusau
ShareTweetSendShare
Previous Post

Shugaba Xi Jinping Ya Yi Kira Da A Kara Samun Nasarorin Sabbin kirkire-kirkire a JKS

Next Post

Kashin Farko Na Daliban Da Za Su Tafi Karatu Kasashen Waje Za Su Tafi A Watan Satumba – Abba

Related

Zulum Ya Haramta Sayar Da Fetur A Bama Don Yaƙi Da Ta’addanci
Manyan Labarai

Zulum Ya Haramta Sayar Da Fetur A Bama Don Yaƙi Da Ta’addanci

8 minutes ago
Bayan Cin Kamfanin META Tarar Dala Miliyan 220: Sun Yi Bazaranar Katse Kafofin Facebook, WhatsApp, Da Instagram A Nijeriya
Manyan Labarai

Bayan Cin Kamfanin META Tarar Dala Miliyan 220: Sun Yi Bazaranar Katse Kafofin Facebook, WhatsApp, Da Instagram A Nijeriya

6 hours ago
Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje
Manyan Labarai

Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

1 day ago
Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai
Manyan Labarai

Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai

1 day ago
Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa
Manyan Labarai

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

2 days ago
Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma
Da ɗumi-ɗuminsa

Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma

2 days ago
Next Post
Hajji 2023: Alhazan Nijeriya 6 Sun Rasu, 30 Na Da Tabin Hankali A Saudiyya

Kashin Farko Na Daliban Da Za Su Tafi Karatu Kasashen Waje Za Su Tafi A Watan Satumba – Abba

LABARAI MASU NASABA

Zulum Ya Haramta Sayar Da Fetur A Bama Don Yaƙi Da Ta’addanci

Zulum Ya Haramta Sayar Da Fetur A Bama Don Yaƙi Da Ta’addanci

May 10, 2025
Rikicin Filato Ya Sa Makiyaya Yin Asarar Naira Miliyan 300 Cikin Wata 2

Rikicin Filato Ya Sa Makiyaya Yin Asarar Naira Miliyan 300 Cikin Wata 2

May 10, 2025
FCDA

ECOWAS Ta Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Bunkasar Tattalin Arzikin Afrika Ta Yamma – Kwamred Bishir Dauda

May 10, 2025
Ƙungiyar Sadarwa Ta Ƙasa Ta Fitar da Sabbin Matakan Tallata Nasarorin Gwamnatin Tinubu

Ƙungiyar Sadarwa Ta Ƙasa Ta Fitar da Sabbin Matakan Tallata Nasarorin Gwamnatin Tinubu

May 10, 2025
Nazari Kan Dabarun Taimaka Wa Masu Kiwon Kifi Domin Jurewa Sauyin Yanayi

Nazari Kan Dabarun Taimaka Wa Masu Kiwon Kifi Domin Jurewa Sauyin Yanayi

May 10, 2025
Noman 2025: Dole Ne Manoma Su Kiyaye Hasashen Hukumar NiMet

Noman 2025: Dole Ne Manoma Su Kiyaye Hasashen Hukumar NiMet

May 10, 2025
Mambobin APC Sun Buƙaci EFCC Ta Sake Buɗe Binciken Matawalle

Mambobin APC Sun Buƙaci EFCC Ta Sake Buɗe Binciken Matawalle

May 10, 2025
Bayan Cin Kamfanin META Tarar Dala Miliyan 220: Sun Yi Bazaranar Katse Kafofin Facebook, WhatsApp, Da Instagram A Nijeriya

Bayan Cin Kamfanin META Tarar Dala Miliyan 220: Sun Yi Bazaranar Katse Kafofin Facebook, WhatsApp, Da Instagram A Nijeriya

May 10, 2025
Likitocin Sin Sun Ba Da Jinya Kyauta A Yankunan Karkara Na Saliyo

Likitocin Sin Sun Ba Da Jinya Kyauta A Yankunan Karkara Na Saliyo

May 9, 2025
Babban Bankin Sin Zai Inganta Hidimomin Kudi Don Habaka Amfani Da Shi

Babban Bankin Sin Zai Inganta Hidimomin Kudi Don Habaka Amfani Da Shi

May 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.