• English
  • Business News
Friday, August 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

FERMA Ta Kammala Ayyukan Tituna 14 Don Saukaka Jigila Da Sufuri A Kebbi – Injiniya Rilwanu

by Sulaiman and Umar Faruk
3 years ago
in Labarai
0
FERMA Ta Kammala Ayyukan Tituna 14 Don Saukaka Jigila Da Sufuri A Kebbi – Injiniya Rilwanu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar kula da lafiyar tituna da gyara su ta tarayya (FERMA) reshen Jihar Kebbi ta kammala ayyukan tituna guda 14 da aka ware wa jihar a karkashin ayyukan rabon jari na 2021 da kyautata zamantakewa al’umma a jihohin kasar nan.

 

Injiniya mai kula da hukumar a jihar Alhaji Rilwanu Usman, ne ya bayyana haka a lokacin da ya ke zantawa da manema labarai a Birnin Kebbi, ya ce an hanzarta kammala ayyukan ne bisa la’akari da mahimmancin tattalin arziki na amfanin noman da al’ummar jihar ke gudanar wa a yankinsu domin saukaka musu jigika da zirga-zirgan amfanin gona.

  • FERMA Na Bukatar Biliyan 100 Wajen Gwamnati Don Yi Wa Hanyoyi Kwaskwarima

Ya ke cewa: “Ayyukan da aka kammala a karkashin kasafin kudi sun hada da gyare-gyare na musamman na titin Kebbi zuwa Kontagora a kan titin Malando-Ngaski-Warra a Jihar. Ayyukan gyare-gyare ne na musamman da suka hada da cike ramuka, cika wasu sassan titin da kwalta da sauransu, kuma an kammala shi a watan Fabrairu.

 

Labarai Masu Nasaba

Kauyuka 30 Sun Yi Zanga-zanga Kan Ta’addancin ‘Yan Bindiga A Zamfara

Tsoffin Kansilolin APC Sun Yi Zanga-zangar Nesanta Kansu Da Maganganun Abdullahi Abbas 

“Mun yi aikin gyaran kan iyakar Sakkwato da titin Argungu-Birnin Kebbi, wanda ya hada da gyaran bangon siminti a cikin garin Gotomo inda gefe ke barazanar yanke hanyar. Haka kuma an kammala gyaran kafadun hanya a kusa da Zauro-Ambursa, da sauransu, duk an kammala su a watan Fabrairu,” ya shaida.

 

Ya cigaba da cewa, “Mun yi titin kwalta mai tsawon kilomita 2.7 tare da gina magudanan ruwa mai nisan kilomita 1.7 a Jega G.R.A kuma an kammala su a watan Maris na bana. Har ila yau, akwai aikin da muka yi a mazabar Koko-Maiyama na tarayya inda aka gina titin kasa mai tsawon kilomita 1.5 da magudanan ruwa guda biyar a Karaye- Sabon Kamba da Sabon Sara.

 

“Maganar zababbun hanyoyi ta hanyar daidaitawa inda wani sashe gefe a garin Gotomo ke haddasa asarar rayuka da dama kuma muka shiga tsakani muka daidaita.”

 

Injiniya Rilwanu Usman ya kara da cewa akwai kuma ayyuka guda biyar a fadin kananan hukumomin uku na jihar da ke karkashin ayyukan kulawa na musamman. “An yi gyaran hanyar Argungu-Bui mai tsawon mita 550 da ya lalace. Ayyukan gyaran na musamman na hanyar Tuga-Ka’oje, an gyara wani bangare na titin da ya gaza, wanda ya hada da ramuka, gina magudanan ruwa, da sauran su, duk an kammala su a bana.

 

“Haka zalika mun kammala aikin titin Malando-Ngaski-Warra mai tsawon 480, tare da ba da takardar shaida na sashin da ba a yi nasara ba tare da gyara kwalta da facin ramuka baya ga wadda ke karkashin babban aikin. An yi gyaran hanyar Masama-Aljannare-Duroci da ke karkashin gundumar Kebbi ta arewa, da magudanar ruwa da titin mita 180 da kwalta.

 

Kazalika “An yi ayyukan gyaran sassan da suka lalace a kan iyakar Birnin Kebbi zuwa Argungu, an gyara kafadu mai tsawon mita 600, sannan an yi gyaran ramuka mai fadin murabba’in mita 487 tsakanin kan iyakar Kebbi da Sakkwato. Akwai ƙarin ayyuka na yau da kullun a karkashin kasafin kudi na 2022 a cikin jihar.

 

“Akwai gyaran titunan da ke tsakanin ramukan kilomita 18 zuwa 38 da ke kan hanyar Argungu zuwa Bui da ake yi a kai-a kai. 749.2 na sassan da suka gaza fiye da murabba’in 400 an yi faci. Aayyukan da aka yi a kai a kai, an yi gyare-gyare gadan-gadan a kan titin Kalgo-Bunza da Feka, an kuma gyara kafadu mai tsawon kilomita 1.2 a kowane wuri, sannan kuma an yi gyaran wasu ramuka 490.

 

“Akwai kuma gina titin 1.22, magudanar ruwa da magudanan ruwa guda uku a Jega phase 2 G.R.A baya ga titin kwalta mai tsawon kilomita 2.7 a karkashin aikin tarayya.

 

“A kokarin da wasu ‘yan majalisa suka yi, mun sanya fitulun na’ura masu aiki da hasken rana da dama a wasu manyan garuruwa, kuma ana ci gaba da aikin gina magudanun ruwa da sauran ayyukan hanyoyi da dai sauransu,” in ji Injiniya Rilwanu Usman.

 

Daga karshe yaba wa hukumar FERMA da ‘yan majalisar dokoki da Atoni-Janar na kasa Abubakar Malami da Gwamna Atiku Bagudu bisa kokarinsu na ganin jihar ta kasance cikin na gaba wajen kula da hanyoyin tarayya a kasar nan.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Fadar Shugaban Kasa Ta Bullo Da Shirin Ceto Yaran Da Ba Sa Zuwa Makaranta

Next Post

Marwa Ya Kara Samun Lambar Yabo

Related

Kauyuka 30 Sun Yi Zanga-zanga Kan Ta’addancin ‘Yan Bindiga A Zamfara
Manyan Labarai

Kauyuka 30 Sun Yi Zanga-zanga Kan Ta’addancin ‘Yan Bindiga A Zamfara

3 hours ago
Tsoffin Kansilolin APC Sun Yi Zanga-zangar Nesanta Kansu Da Maganganun Abdullahi Abbas 
Labarai

Tsoffin Kansilolin APC Sun Yi Zanga-zangar Nesanta Kansu Da Maganganun Abdullahi Abbas 

4 hours ago
Neja
Labarai

Sulhu Da ‘Yan Bindiga A Jihohin Makwabta, Ya Kara Ta’azzarar Rashin Tsaro A Neja – Bago

5 hours ago
Ranar Cutar Daji Ta 2025: Akwai Matakan Kariya Daga Kamuwa Da Cutar Kansa -Masana
Labarai

Ranar Cutar Daji Ta 2025: Akwai Matakan Kariya Daga Kamuwa Da Cutar Kansa -Masana

6 hours ago
NAF Ta Kashe ‘Yan Bindiga Da Dama A Zamfara
Labarai

An Kashe ‘Yan Ta’adda Fiye Da 30 A Wani Harin Jirgin Sama A Wurin Daurin Aure A Zamfara

7 hours ago
Gwamnan Kano Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Gentle, Ya Bada Umarnin Zakulo Masu Laifin
Manyan Labarai

Gwamnan Kano Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Gentle, Ya Bada Umarnin Zakulo Masu Laifin

8 hours ago
Next Post
Marwa Ya Kara Samun Lambar Yabo

Marwa Ya Kara Samun Lambar Yabo

LABARAI MASU NASABA

Barcelona Ta Tube Ter Stergen Daga Mukaminsa Na Kaftin Din Kungiyar 

Barcelona Ta Tube Ter Stergen Daga Mukaminsa Na Kaftin Din Kungiyar 

August 7, 2025
Tallafin Kammala Makarantun Share Fagen Shiga Firamare Na Gwamnatin Kasar Sin Zai Amfani Mutane Kimanin Miliyan 12

Tallafin Kammala Makarantun Share Fagen Shiga Firamare Na Gwamnatin Kasar Sin Zai Amfani Mutane Kimanin Miliyan 12

August 7, 2025
Kauyuka 30 Sun Yi Zanga-zanga Kan Ta’addancin ‘Yan Bindiga A Zamfara

Kauyuka 30 Sun Yi Zanga-zanga Kan Ta’addancin ‘Yan Bindiga A Zamfara

August 7, 2025
Cinikayyar Kayayyaki a Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.5 Cikin 100 Cikin Watanni 7 Na Farkon Shekarar Nan

Cinikayyar Kayayyaki a Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.5 Cikin 100 Cikin Watanni 7 Na Farkon Shekarar Nan

August 7, 2025
Amurka Ta Fara Girbar Sakamakon Kare-Karen Haraji

Amurka Ta Fara Girbar Sakamakon Kare-Karen Haraji

August 7, 2025
Tsoffin Kansilolin APC Sun Yi Zanga-zangar Nesanta Kansu Da Maganganun Abdullahi Abbas 

Tsoffin Kansilolin APC Sun Yi Zanga-zangar Nesanta Kansu Da Maganganun Abdullahi Abbas 

August 7, 2025
Neja

Sulhu Da ‘Yan Bindiga A Jihohin Makwabta, Ya Kara Ta’azzarar Rashin Tsaro A Neja – Bago

August 7, 2025
Nazarin CGTN: Alummar Duniya Na Adawa Da Fadada Mamaya A Gaza

Nazarin CGTN: Alummar Duniya Na Adawa Da Fadada Mamaya A Gaza

August 7, 2025
Ranar Cutar Daji Ta 2025: Akwai Matakan Kariya Daga Kamuwa Da Cutar Kansa -Masana

Ranar Cutar Daji Ta 2025: Akwai Matakan Kariya Daga Kamuwa Da Cutar Kansa -Masana

August 7, 2025
Kasar Sin Ta Kammala Gwajin Farko Na Sauka Da Tashin Kumbon Binciken Duniyar Wata Mai Dauke Da Bil Adama

Kasar Sin Ta Kammala Gwajin Farko Na Sauka Da Tashin Kumbon Binciken Duniyar Wata Mai Dauke Da Bil Adama

August 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.