ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

FERMA Ta Kammala Ayyukan Tituna 14 Don Saukaka Jigila Da Sufuri A Kebbi – Injiniya Rilwanu

by Sulaiman and Umar Faruk
4 years ago
FERMA

Hukumar kula da lafiyar tituna da gyara su ta tarayya (FERMA) reshen Jihar Kebbi ta kammala ayyukan tituna guda 14 da aka ware wa jihar a karkashin ayyukan rabon jari na 2021 da kyautata zamantakewa al’umma a jihohin kasar nan.

 

Injiniya mai kula da hukumar a jihar Alhaji Rilwanu Usman, ne ya bayyana haka a lokacin da ya ke zantawa da manema labarai a Birnin Kebbi, ya ce an hanzarta kammala ayyukan ne bisa la’akari da mahimmancin tattalin arziki na amfanin noman da al’ummar jihar ke gudanar wa a yankinsu domin saukaka musu jigika da zirga-zirgan amfanin gona.

ADVERTISEMENT
  • FERMA Na Bukatar Biliyan 100 Wajen Gwamnati Don Yi Wa Hanyoyi Kwaskwarima

Ya ke cewa: “Ayyukan da aka kammala a karkashin kasafin kudi sun hada da gyare-gyare na musamman na titin Kebbi zuwa Kontagora a kan titin Malando-Ngaski-Warra a Jihar. Ayyukan gyare-gyare ne na musamman da suka hada da cike ramuka, cika wasu sassan titin da kwalta da sauransu, kuma an kammala shi a watan Fabrairu.

 

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

“Mun yi aikin gyaran kan iyakar Sakkwato da titin Argungu-Birnin Kebbi, wanda ya hada da gyaran bangon siminti a cikin garin Gotomo inda gefe ke barazanar yanke hanyar. Haka kuma an kammala gyaran kafadun hanya a kusa da Zauro-Ambursa, da sauransu, duk an kammala su a watan Fabrairu,” ya shaida.

 

Ya cigaba da cewa, “Mun yi titin kwalta mai tsawon kilomita 2.7 tare da gina magudanan ruwa mai nisan kilomita 1.7 a Jega G.R.A kuma an kammala su a watan Maris na bana. Har ila yau, akwai aikin da muka yi a mazabar Koko-Maiyama na tarayya inda aka gina titin kasa mai tsawon kilomita 1.5 da magudanan ruwa guda biyar a Karaye- Sabon Kamba da Sabon Sara.

 

“Maganar zababbun hanyoyi ta hanyar daidaitawa inda wani sashe gefe a garin Gotomo ke haddasa asarar rayuka da dama kuma muka shiga tsakani muka daidaita.”

 

Injiniya Rilwanu Usman ya kara da cewa akwai kuma ayyuka guda biyar a fadin kananan hukumomin uku na jihar da ke karkashin ayyukan kulawa na musamman. “An yi gyaran hanyar Argungu-Bui mai tsawon mita 550 da ya lalace. Ayyukan gyaran na musamman na hanyar Tuga-Ka’oje, an gyara wani bangare na titin da ya gaza, wanda ya hada da ramuka, gina magudanan ruwa, da sauran su, duk an kammala su a bana.

 

“Haka zalika mun kammala aikin titin Malando-Ngaski-Warra mai tsawon 480, tare da ba da takardar shaida na sashin da ba a yi nasara ba tare da gyara kwalta da facin ramuka baya ga wadda ke karkashin babban aikin. An yi gyaran hanyar Masama-Aljannare-Duroci da ke karkashin gundumar Kebbi ta arewa, da magudanar ruwa da titin mita 180 da kwalta.

 

Kazalika “An yi ayyukan gyaran sassan da suka lalace a kan iyakar Birnin Kebbi zuwa Argungu, an gyara kafadu mai tsawon mita 600, sannan an yi gyaran ramuka mai fadin murabba’in mita 487 tsakanin kan iyakar Kebbi da Sakkwato. Akwai ƙarin ayyuka na yau da kullun a karkashin kasafin kudi na 2022 a cikin jihar.

 

“Akwai gyaran titunan da ke tsakanin ramukan kilomita 18 zuwa 38 da ke kan hanyar Argungu zuwa Bui da ake yi a kai-a kai. 749.2 na sassan da suka gaza fiye da murabba’in 400 an yi faci. Aayyukan da aka yi a kai a kai, an yi gyare-gyare gadan-gadan a kan titin Kalgo-Bunza da Feka, an kuma gyara kafadu mai tsawon kilomita 1.2 a kowane wuri, sannan kuma an yi gyaran wasu ramuka 490.

 

“Akwai kuma gina titin 1.22, magudanar ruwa da magudanan ruwa guda uku a Jega phase 2 G.R.A baya ga titin kwalta mai tsawon kilomita 2.7 a karkashin aikin tarayya.

 

“A kokarin da wasu ‘yan majalisa suka yi, mun sanya fitulun na’ura masu aiki da hasken rana da dama a wasu manyan garuruwa, kuma ana ci gaba da aikin gina magudanun ruwa da sauran ayyukan hanyoyi da dai sauransu,” in ji Injiniya Rilwanu Usman.

 

Daga karshe yaba wa hukumar FERMA da ‘yan majalisar dokoki da Atoni-Janar na kasa Abubakar Malami da Gwamna Atiku Bagudu bisa kokarinsu na ganin jihar ta kasance cikin na gaba wajen kula da hanyoyin tarayya a kasar nan.

FERMA
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna
  • Sulaiman
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
FERMA
Umar Faruk
+ posts Bio
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Gwamnatin Kebbi Ta Amince Da ₦2.07bn Alawus-alawus Ga Ma’aikatan Manyan Makarantu
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Gwamnan Kebbi Ya Maye Gurbin Mataimakinsa Da Ibrahim Augie A Zaɓen 2027
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Matashi Ya Shiga Hannu Kan Zargin Wulaƙanta Alƙur’ani A Kebbi
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Gwamnan Kebbi Ya Miƙa Yara 5 Da Aka Ceto Daga Hannun Masu Safarar Mutane Ga Iyayensu

MASU ALAKA

'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare
Labarai

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Next Post
Marwa Ya Kara Samun Lambar Yabo

Marwa Ya Kara Samun Lambar Yabo

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.