• English
  • Business News
Saturday, October 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

FIFA Ta Dakatar Da Eto’o Zuwa Kallon Wasanni Har Tsawon Watanni Shida

by Abba Ibrahim Wada and Abubakar Sulaiman
1 year ago
Fifa

Hukumar Kula da Kwallon Kafa ta Duniya FIFA, ta dakatar da shugaban hukumar kwallon kafar Kamaru, Samuel Eto’o daga zuwa kallon wasannin kasar zuwa watanni shida sakamakon samun sa da laifin karya dokar da’a karo biyu ta FIFA.

 

An hukunta tsohon dan wasan Barcelona da Chelsea ne sakamakon abin da ya faru a gasar kofin duniya ta matasa ‘‘yan kasa da shekara 20 ranar 11 ga watan Satumba, inda Brazil ta doke Kamaru 3-1 a zagaye na biyu.

  • Alakar Arsenal Da ‘Yan Wasa Bakaken Fata
  • Jihar Sokoto Za Ta Gina Sabbin Madatsun Ruwa Uku

Kamar yadda FIFA ta fitar da jawabi, an yi kalamai na batanci da nuna halin rashin da’a daga ‘‘yan wasa da jami’ai a karawar da aka yi a Bogota a Colombia, inda Eto’o ya halarci karawar. Hukuncin yana nufin an hana Eto’o mai shekara 43 a duniya halartar duk wani wasan Kamaru na maza da na mata tun daga masu karancin shekaru zuwa babbar kungiya har wata shida, kuma FIFA ta ce hukuncin ya fara aiki nan take, ta kuma ce ta sanar da Eto’o kan wannan matakin da ta dauka.

 

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Ɗan Wasan Dambe, Ricky Hatton Ya Rataye Kansa

Da Ɗumi-ɗumi: Ladan Bosso Ya Ajiye Aikin Horar Da Barau Fc 

Tawagar Kamaru za ta kara da Kenya gida da waje a wasan neman shiga gasar kofin Afirka 2025 da za a yi a Morocco, inda za su kara a cikin watan Oktoba.

 

A ranar Litinin Eto’o ya ja ragamar taron hukumar kwallon kafar kasar kan tsara yadda za su fuskanci Harambe Stars ranar 11 ga watan Oktoba, amma kuma har yanzu hukumar kwallon kafar Kamaru ba ta ce komai ba kan wannan hukuncin.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tsohon Ɗan Wasan Dambe, Ricky Hatton Ya Rataye Kansa
Wasanni

Tsohon Ɗan Wasan Dambe, Ricky Hatton Ya Rataye Kansa

October 16, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Ladan Bosso Ya Ajiye Aikin Horar Da Barau Fc 
Wasanni

Da Ɗumi-ɗumi: Ladan Bosso Ya Ajiye Aikin Horar Da Barau Fc 

October 15, 2025
Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Benin A Uyo
Wasanni

Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Benin A Uyo

October 14, 2025
Next Post
APP Ta Lashe Kujeru 22 A Zaben Kananan Hukumomin Ribas

APP Ta Lashe Kujeru 22 A Zaben Kananan Hukumomin Ribas

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Kama Gungun Masu Sojan Gona Suna Aikata Laifuka A Kano

Ƴansanda Sun Kama Gungun Masu Sojan Gona Suna Aikata Laifuka A Kano

October 18, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Ofishin Ƴansanda, Sun Kashe 2 A Kaduna

Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Ofishin Ƴansanda, Sun Kashe 2 A Kaduna

October 18, 2025
Radda

Gwamnan Katsina Ya Bukaci Al’umma Su Hada Hannu Da Gwamnati Wajen Kawar Da Matsalar Tsaro

October 18, 2025
Yajin Aikin ASUU: Majalisar Dattawa Ta Tsoma Baki, Za Ta Gana Da Ministan Ilimi

Yajin Aikin ASUU: Majalisar Dattawa Ta Tsoma Baki, Za Ta Gana Da Ministan Ilimi

October 18, 2025
IMF

Fitar Da Kudi Ta Haramtacciyar Hanya Na Kara Dagula Matsalar Tattalin Arziki – IMF

October 18, 2025
majalisar kasa

Majalisar Wakilai Ta Gayyaci CBN Da Bankuna Kan Cire Wa Kwastomomi Kudi Ba Dalili

October 18, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

Matashi Ya Kashe Ɗan Acaɓa Don Neman Kuɗin Auren Mace Ta Uku A Bauchi

October 17, 2025
katsina

Tawagar Bankin Duniya Ta Gana Da Gwamnan Katsina Kan Mayar Da ‘Yan Gudun Hijira Muhallinsu

October 17, 2025
Tinubu Ya Amince A Fara Aikin Tashoshin Jiragen Ruwa Na Apapa Da Kalaba Da Fatakwal Da Warri — NPA

Tinubu Ya Amince A Fara Aikin Tashoshin Jiragen Ruwa Na Apapa Da Kalaba Da Fatakwal Da Warri — NPA

October 17, 2025
Akwai Bukatar Al’umma Ta San Aikin Da Asusun Tallafa Wa Manyan Makarantu (TETFUND) Ya Yi  – Masari

Akwai Bukatar Al’umma Ta San Aikin Da Asusun Tallafa Wa Manyan Makarantu (TETFUND) Ya Yi  – Masari

October 17, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.