ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Alakar Arsenal Da ‘Yan Wasa Bakaken Fata

by Abba Ibrahim Wada and Sulaiman
2 years ago
Arsenal

Wasu za su iya cewa kungiyar kwallon kafa ta Chelsea ce ta fi amfani da ‘yan wasa bakar fada a kasar Ingila, sannan akwai kungiyoyi irin su Fouthmouth da Leceister City wadanda duka suke amfani da bakaken ‘yan wasa.

 

Amma lokacin da Dr Clibe Chijioke Nwonka ya je Manchester domin ziyartar abokansa a ranar 28 ga Satumban 2002, ya hadu da muhimmin al’amari, domin kuwa ya kalli wasan kwallon kafa mai cike da tarihi.

ADVERTISEMENT
  • Wakilin Sin Ya Bukaci Sassan Somaliya Da Su Kara Azamar Warware Sabani Ta Hanyar Tattaunawa
  • Tinubu Ya Samar Da Naira Biliyan 29 Don Gyara Hanyoyin Kasar Nan

Kungiyar kwallon kafa ta Arsenal a wannan ranar ta kasance kungiyar kwallon kafa da ta yi amfani da ‘yanwasa tara bakaken fata daga cikin 11 a wasan Premier League kuma uku daga cikinsu, Thierry Henry, Nwankwo Kanu da Kolo Toure, kuma suna cikin wadanda suka jefa kwallo a raga a wasan da Arsenal ta doke Leeds United da ci 4-1.

 

LABARAI MASU NASABA

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa

A hirarsa da Sashen Hausa na BBC, Dr Nwonka, wanda yanzu farfesa ne a Unibersity College London, ya bayyana cewa kwazonsu ya nuna tasirin wannan lokacin mai tarihi da kuma muhimmancin launin fata a duniya.

 

Dr Nwonka ya nuna rawar da kungiyar ta taka ga tarihin al’adun bakaken fata, a matsayin daya daga cikin editan littafin da aka wallafa mai taken “Black Arsenal,” wanda ya kunshi bayanai da hotunan wasu da suke ganin suna da alaka da kungiyar da ke Birnin Landan.

 

“Ni dan Birtaniya ne mai asali daga Nijeriya, kuma ina ganin ‘yan wasa bakaken fata da ‘yan wasan Afrika a kwallon Birtaniya yana da muhimmanci a gare ni,” in ji shi.

 

Wani bangare na littafin ya yi sharhin gudunmuwar Arsenal ga kwararar ‘yan wasa bakaken fata a gasar Premier da kuma samun magoya baya mata a filin kungiyar na Emirates.

 

Ya ce yana jin kullum akwai wani abu muhimmi, kan yadda bakaken fata ke da alaka da Arsenal kuma goyon bayan da kungiyar ke samu zai shafi harakokin yau da kullum na dimbin magoya bayan kungiyar, kuma an tabo wannan a cikin littafin.

 

Wenger da Afirka

Ian Wright, shi ne ya kasance mai farin jini ga dimbin magoya bayan Arsenal bakaken fata a shekarun 1990, saboda yunwarsa ta cin kwallaye sai dai ba dukkanin magoya bayan Arsenal za su amince da hotonsa a bangon littafin Black Arsenal ba, amma Dr Nwonka da sauran ‘‘yan Nijeriya, suna ganin akwai wani muhimmin dan wasa.

 

Sun tuna tawagar Nijeriya da ta lashe sarkar zinari a wasannin Olympics bayan doke Argentina a shekarar 1996, kuma dan wasa Nwanko Kanu ne ya zura kwallon da ta bayar da nasara a wasan kusa da karshe da Brazil.

 

An haifi Kanu a Jihar Imo, dan wasan ya koma Arsenal ne daga kungiyar kwallon kafa ta Inter Milan ta Italiya a 1999 kuma zuwansa Arsenal yana da muhimmanci ga bakaken fata a duniya.

 

Tsohon kocin Arsenal, Arsene Wenger, wanda ya yi fice wajen sayen ‘yan wasan Faransa da bakaken fata, tare da renon ‘yan wasa da dama a shekara 22 da ya shafe yana horar da Arsenal tsakanin 1996 zuwa 2018.

 

Wenger ya samu karbuwa da girmamawa kan tsarinsa na tafiyar aikinsa musamman lokacin da Arsenal ta lashe kofi a kakar wasa ta 2003 zuwa 2004, kuma irin wannan nasarar ce wani bangare na magoya baya suka koma goyon bayan Chelsea abokiyar gabar Arsenal a London, wadda ta yi fice zamanin Jose Mourinho lokacin da ya dauko ‘yan wasa bakaken fata kamar su Didier Drogba na Ibory Coast da dan wasan Ghana Michael Essien da kuma dan wasan tsakiya na Nijeriya John Obi Mikel.

 

Amma duk da nasarorin ‘yan wasa bakaken fata, har yanzu wariyar launin fata babbar matsala ce a filin wasa domin kuwa a shekarar 2021, bayan rashin nasara a wasan karshe a gasar cin kofin Turai ta Euro 2020, hannun Italiya, ‘yan wasa uku na Ingila – Bukayo Saka, Jadon Sancho da Marcus Rashford, sun fuskanci wariyar launin fata saboda sun barar da bugun daga kai sai mai tsaron raga.

 

An kama mutum 11, kuma Arsenal ta fitar da sanarwa tana nuna goyon baya ga dan wasanta Saka da sauran abokan wasansa na Ingila, sai dai an dade Saka yana fuskantar wariya, ciki har da lokacin da Arsenal ta sha kashi a hannun Nottingham Forest a bara.

 

Matsalar wariya ta kasance ruwan dare a dukkanin bangarori na kwallon kafa da aka fi bayar da rahoto a Ingila, kamar yadda alkalumman kungiyar yaki da wariyar launin fata ta duniya mai suna Kick It Out suka nuna.

 

A kakar bana, Arsenal ta yi bikin alakarta da Afirka ta hanyar samar da rigar ‘yan wasa da ke da launi irin na tutar kasashen nahiyar Afirka kuma Foday Dumbuya, dan asalin kasar Saliyo, shi ne ya tsara rigar kuma a Birnin Freetown aka dauki bidiyon tallan sabbin tufafin ‘yan wasan.

 

Dan wasa Bukayo Saka, iyayensa ‘yan Nijeriya ne da suka haife shi a Landan, kuma yanzu shi yake da farin jinin magoya bayan Arsenal, sannan dan wasan mai shekara 23 ya yi wa Arsenal wasanni 230 kuma ya dade yana adawa da nuna wariyar launin fata, har ila yau, yanzu shi ne kan gaba a bunkasar alakar Arsenal da bakaken fata a duniya.

Arsenal
Abba Ibrahim Wada
Website |  + posts Bio
  • Abba Ibrahim Wada
    Ko Kasan ‘Yanwasan Da Za Su Buga Kofin Duniya Na Ƙarshe?
  • Abba Ibrahim Wada
    Nijeriya Ta Samu Lambobin Yabo 16 A Wasannin Tseren Keke
  • Abba Ibrahim Wada
    Nijeriya Za Ta Karbi Bakuncin Babban Taron Hukumar CAF Na Bana
  • Abba Ibrahim Wada
    Shin Ko Arsenal Za Ta Mamaye Duniya?
Arsenal
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • Sulaiman
    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
  • Sulaiman
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

MASU ALAKA

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya
Wasanni

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa
Wasanni

Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa

June 2, 2026
Super Eagles Ta Tafi Poland Domin Wasan Sada Zumunta
Adabi

Super Eagles Ta Tafi Poland Domin Wasan Sada Zumunta

May 31, 2026
Next Post
An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa

An Kama Mutum 89 Da Ake Zargi Da Fashi Da Dillancin Muggan Kwayoyi A Kano

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.