• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Filato: An Kaddamar Da Rundunar Tsaro Ta Musamman

by Sadiq
1 year ago
in Manyan Labarai
0
Filato: An Kaddamar Da Rundunar Tsaro Ta Musamman
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rundunar ‘yan sandan Nijeriya ta kaddamar da wata runduna ta musamman da za ta yi yaki da bata-gari da ke kashe-kashen rayuka da barnata dukiyoyin jama’a a Jihar Filato.

Sufeto-Janar na ‘yan sandan Nijeriya, Kayode Egbetokun wanda ya kai ziyarar gani da ido kan asarar rayuka da dama a wasu kananan hukumomin Jihar Filato, ya ce rundunar ta musamman da gwamnatin tarayya ta amince da kaddamarwa a jihohi 10 na Nijeriya, za ta fara aiki ne nan take a Jihar Filato.

  • Sabuwar Shekara: Gwamna Inuwa Yahaya Ya Yi Wa Fursunoni 39 Afuwa A Gombe
  • Hare-Hare: Gwamnatin Filato Ta Ayyana Zaman Makokin Mako Guda

Tuni da mataimakin Sufeto-Janar na shiya ta hudu, Ebong Eyibio ya kaddamar da jami’an runduna ta musamman zuwa yankunan da ke fuskantar matsalolin tsaron.

A ci gaba da neman mafita kan batun kalubalen tsaron, Sanata mai wakiltar tsakiyar Filato, Diket Plang ya gabatar da wasu batutuwa a gaban majalisar dattawa, inda ya ce za su taimaka wajen kawo zaman lafiya a jihar.

Sanata Diket Plang ya koka kan yadda maharan su 400 suka ratsa wurare suka mamaye kauyuka fiye da 20 ba tare da wani ya gansu ba.

Labarai Masu Nasaba

‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta ÆŠaya A Kogi

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don YaÆ™ar ‘Yan Ta’adda

Ya kuma koka kan yadda wasu ke mamaye gonaki da gidajen wadanda suka yi gudun hijira, tare da yin kira ga gwamnatin tarayya da ta samar da jami’an tsaro na dindindin a yankunan.

A cewar Dah Mai’anguwa, Jamok Mafwalal Machambe daga gundumar Butura a karamar hukumar Bokkos, sun yi na’am da zuwan jami’an tsaron, ya kuma bukaci jama’a su basu goyon baya don samar da tsaro.

Sakataren kungiyar Miyetti Allah a karamar hukumar Barkin Ladi, Abubakar Gambo yace suna bukatar jami’an tsaron su yi adalci.

A makon da ya gabata ne wasu mahara suka hallaka mutane sama da 160 a wasu kauyuka sama da 20, lamarin da ya haifar da cece-kuce a tsakanin ‘yan Nijeriya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Nasarawa

Next Post

Daliban Kano Da Bauchi Sun Lashe Gasar Alkur’ani Ta 2023

Related

‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta ÆŠaya A Kogi
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta ÆŠaya A Kogi

25 minutes ago
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?
Da É—umi-É—uminsa

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don YaÆ™ar ‘Yan Ta’adda

6 hours ago
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara
Manyan Labarai

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

9 hours ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

10 hours ago
UTME
Manyan Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

18 hours ago
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu
Manyan Labarai

JAMB: TangarÉ—ar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

1 day ago
Next Post
Daliban Kano Da Bauchi Sun Lashe Gasar Alkur’ani Ta 2023

Daliban Kano Da Bauchi Sun Lashe Gasar Alkur’ani Ta 2023

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta ÆŠaya A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta ÆŠaya A Kogi

May 15, 2025
Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

May 15, 2025
An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

May 15, 2025
NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

May 15, 2025
Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

May 15, 2025
Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

May 15, 2025
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don YaÆ™ar ‘Yan Ta’adda

May 15, 2025
ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

May 15, 2025
‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

May 15, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

May 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.