ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 8, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Daliban Kano Da Bauchi Sun Lashe Gasar Alkur’ani Ta 2023

by Sadiq
3 years ago
Alkur'ani

Zainab Aliyu Muhammad daga Jihar Kano ta zama gwarzuwar gasar Alkur’ani ta kasa ta shekarar 2023 a bangaren mata a hadda da tafsiri.

A bangaren maza kuwa, Ibrahim Muhammad Nasir daga Jihar Bauchi ne, ya zama gwarzon shekara a musabakar karo na 38, wadda aka kammala a Jihar Yobe.

  • Hare-Hare: Gwamnatin Filato Ta Ayyana Zaman Makokin Mako Guda
  • Ba Za Mu Lamunci Lalaci Daga Waɗanda Aka Naɗa Muƙamai Ba– Tinubu

Mai masaukin baki, Gwamnan Jihar Yobe, Mai Mala Buni, ya karamma Zainab Aliyu Muhammad daga Jihar Kano da kyautar mota kirar Honda Accord.

ADVERTISEMENT

Ibrahim Muhammad Nasir kuma gwamnan ya gwangwaje shi da kyautar mota kirar Honda Accord.

Sannan ya ba da kyautar bas mai daukar mutane 18 kirar Toyota Hummer ga kwamitin shiryar musabakar na kasa don ci gaba da dawainiyar gasar Alku’rani.

LABARAI MASU NASABA

Kwankwaso Ya Mayar wa Ali Modu Sheriff Martani, Ya Ce Peter Obi Na da Gagarumin Goyon Baya a Arewa

Sojoji Da NDLEA Sun Kama Mutanen Da Ake Zargi Da Kai wa ’Yan Ta’adda Miyagun Ƙwayoyi A Katsina

A ranar Asabar ne aka kammala gasar karatun Alkur’anin ta kasa karo na 38 a Damaturu, Jihar Yobe inda alarammomi daga sassan Nijeriya suka nuna bajintarsu.

A lokacin rufe gasar, Mai Alfarma Sarkin Musulmi Muhammad Sa’ad Abubakar, ya yaba wa matasan da suka shiga wannan gasar ta karatun Alkur’ani Mai Girma rukuni-rukuni, sannan ya yi musu fatan alheri.

Sarkin Musulmi, wanda shi ne ya jagoranci taron, ya nuna farin cikinsa bisa yadda aka gudanar da gasar a Yobe cikin kwanciyar hankali kuma a bisa tsari ba tare da an samu cikas ba.

Shi ma shugaban Jami’ar Usmanu Dan Fodiyo da ke Sakkwato, Farfesa Lawan Sulaiman Bilbis, ya yaba wa gwamna Mai Mala Buni bisa yadda ya dauki nauyin gasar da kuma yadda aka gudanar da ita cikin nasara.

Cibiyar Nazarin Addinin Musulunci ta Jami’ar Danfodiyo ce, ke shirya gasar tasa a Nijeriya, kuma wannan shi ne karo na 38.

Mahalarta bikin rufe gasar ta Alkur’ani sun hada da Gwamna Jihar Gombe, Shugaban Kungiyar Gwamnonin Arewa, Inuwa Yahaya, Mataimakin Gwamna Jihar Borno, Mataimakin Gwamnan Jihar Taraba.

Sai masu girma sarakunan Jihar Yobe gaba daya, karkashin Mai Martaba Sarkin Fika, sai Mai Martaba Shehun Dikwa da ya wakilci Mai girma Shehun Borno, sai Mai girma Sarkin Bauchi da sauran manya-manyan baki.

MASU ALAKA

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Labarai

Kwankwaso Ya Mayar wa Ali Modu Sheriff Martani, Ya Ce Peter Obi Na da Gagarumin Goyon Baya a Arewa

July 8, 2026
Sojoji Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Waɗanda Aka Sace A Taraba
Manyan Labarai

Sojoji Da NDLEA Sun Kama Mutanen Da Ake Zargi Da Kai wa ’Yan Ta’adda Miyagun Ƙwayoyi A Katsina

July 8, 2026
Majalisar Zartarwa Ta Jihar Kaduna Ta Amince Da Manufofin Haɓaka Walwalar Al’ummar Jihar
Labarai

Majalisar Zartarwa Ta Jihar Kaduna Ta Amince Da Manufofin Haɓaka Walwalar Al’ummar Jihar

July 8, 2026
Next Post
Tinubu Ya Dakatar Da Halima Shehu, Ya Nada Akindele Egbuwalo A Matsayin Kodinetan NSIPA

Tinubu Ya Dakatar Da Halima Shehu, Ya Nada Akindele Egbuwalo A Matsayin Kodinetan NSIPA

LABARAI MASU NASABA

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Kwankwaso Ya Mayar wa Ali Modu Sheriff Martani, Ya Ce Peter Obi Na da Gagarumin Goyon Baya a Arewa

July 8, 2026
Sojoji Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Waɗanda Aka Sace A Taraba

Sojoji Da NDLEA Sun Kama Mutanen Da Ake Zargi Da Kai wa ’Yan Ta’adda Miyagun Ƙwayoyi A Katsina

July 8, 2026
An Gudanar Da Manyan Tarurruka 3 Game Da Kimiyya Da Fasaha A Beijing

An Gudanar Da Manyan Tarurruka 3 Game Da Kimiyya Da Fasaha A Beijing

July 8, 2026
Majalisar Zartarwa Ta Jihar Kaduna Ta Amince Da Manufofin Haɓaka Walwalar Al’ummar Jihar

Majalisar Zartarwa Ta Jihar Kaduna Ta Amince Da Manufofin Haɓaka Walwalar Al’ummar Jihar

July 8, 2026
Dole Ne Mace Ta Gaya Wa Mijinta Gaskiya Domin Ranar Hisabi – Matar Gwamnan Jigawa

Gwamnatin Jigawa Ta Ɗaga Mafi Ƙarancin Fansho Zuwa Naira 20,000

July 8, 2026
Rahoton Bankin Duniya: Ci Gaban Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Dore

Rahoton Bankin Duniya: Ci Gaban Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Dore

July 7, 2026
Binciken CGTN Ya Shaida Kiraye-kirayen Jama’a Game Da Bukatar Hada Karfi Da Karfe Wajen Shawo Kan Kalubalen Tsanantar Yanayi

Binciken CGTN Ya Shaida Kiraye-kirayen Jama’a Game Da Bukatar Hada Karfi Da Karfe Wajen Shawo Kan Kalubalen Tsanantar Yanayi

July 7, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai

Ɗan Takarar Gwamnan Kaduna Na ADC, Ya Gana da El-Rufai, Ya Sha Alwashin Kawo Karshen Mulkin APC

July 7, 2026
Kulla Yarjejeniyar UNCLOS Da Aiwatar Da Ita Jigo Ne Na Wanzar Da Gaskiya Da Adalci A Odar Teku Tsakanin Kasa Da Kasa

Kulla Yarjejeniyar UNCLOS Da Aiwatar Da Ita Jigo Ne Na Wanzar Da Gaskiya Da Adalci A Odar Teku Tsakanin Kasa Da Kasa

July 7, 2026
Argentina Ta Kai Zagayen Kwata Fainal Bayan Nunawa Egypt Ƙwanji

Argentina Ta Kai Zagayen Kwata Fainal Bayan Nunawa Egypt Ƙwanji

July 7, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.