• English
  • Business News
Thursday, September 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Fina-finai Masu Dogon Zango Koma Baya Ne Ga Masana’antar Kannywood – Tanimu Akawu

by Rabilu Sanusi Bena and Sulaiman
1 year ago
in Nishadi
0
Fina-finai Masu Dogon Zango Koma Baya Ne Ga Masana’antar Kannywood – Tanimu Akawu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Daya daga cikin manyan jarumai dattawa a masana’antar Kannywood wadanda suka dade ana damawa da su a wannan masana’antar Tanimu Akawu ya yi karin haske a kan yadda fina-finai masu dogon zango da suka mamaye masana’antar suke kawo cikas ko kuma koma baya ga ita kanta wannan masana’antar ta Kannywood duba da cewar yanzu zamani ya canza ba kamar shekarun da suka shude ba.

 

Jarumin a wata hura mai tsawo da ya yi da jarumar Kannywood Hadiza Aliyu a cikin shirinta mai suna Gabon’s Room Talk Show ya tabo bangarori da dama da suka shafi wannan masana’antar da ya ce ya shafe shekaru 20 a cikinta.

  • Mashawarcin Shugaban Amurka Kan Harkokin Tsaro Jake Sullivan Zai Ziyarci Kasar Sin 
  • Babu Tsaftatacciyar Masana’antar Shirya Fina-finai Kamar Kannywood A Duniya -Tijjani Asase

Da farko dai Tanimu ya karyata mutanen da suke daukarsa a matsayin mai satar fasaha (Piracy) a masana’antar Kannywood inda ya ce tun kafin ya fara fitowa a matsayin jarumin fim shi mutum ne da yake harkar gidajen sinima, inda yake sayen fina-finai daga masu sayarwa kokuma shiryawa shi kuma ya nuna a gidan sinima domin neman halalinsa.

 

Labarai Masu Nasaba

Ina Fatan Watsi Da Harkar Fim Nan Gaba —Umar Hassan

Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

Dangane da maganganu da suke tasowa a masana’antar akan cewa akwai wadansu jarumai da suke butulcewa masu gidajensu a masana’antar bayan sun fara samun daukaka ko kuma rufin asiri, Akawu ya ce wannan maganar gaskiya ce domin kuwa shi kan shi akwai da dama a cikin jarumai da furodusoshin da ya taimakawa a lokacin da suke neman taimako amma yanzu bayan sun samu daukaka su kuma suka butulce masa.

 

Dattijon ya kara da cewa duk da yanzu zamani ya canza mafi yawancin furodusoshi sun fi bukatar shirya fina-finai masu dogon zango sun daina shirya gajerun fina finai,amma wannan ba ita ce hanyar da za ta ciyar da Kannywood gaba ba hasali ma babban koma baya ne ga masana’antar domin kuwa ta wannan hanyar ba kowane fim ne za a yi shi a kammala kuma a samu wani abin kirki na riba ba.

 

Domin kuwa harkar sinima ita ce kadai hantar da mai shirya fim zai samu kudaden da zai cire uwa kuma ya cire ribar shi cikin lokaci, ba yanzu da wayoyin hannu da sauran kafafen talabijin da suke nuna fina-finai kyauta ba, saboda yanzu zaka dora fim a yanar gizo mutane (‘yan downloading) su saka data da Naira 100 su dauko shi su dinga tura wa mutane akan Naira 10 Naira Ashirin ba tareda ka samu ko Kwabo ba a wajensu.

 

Haka kuma akwai da yawa a cikin gidajen talabijin da suke nuna fina-finai a kyauta ba tareda ka saka ko sisi ba don haka mutane sun fi zuwa inda za su kalli fim a kyauta ba tare da sisin su ya yi ciwo ba, har ma a kwanaki akwai wata kafar talabijin da ta yi ikirarin daina saka fina finai a kyauta a tashar ta,amma bayan shawarwari sai aka ce mata muddin ta daina nuna fina finai a kyauta za ta yi asarar miliyoyin abokan huldarta hakan ya sa ta fasa, in ji Tanimu.

 

Da aka tambayeshi wani irin tasiri role din da yake hawa na mugun mutum a masana’antar Kannywood yayi a rayuwarshi Tanimu ya bayyana cewar gaskiya wannan role din ya saka mutane da dama suna yi ma shi daukar mutum mai mugunta a zahiri,inda har wasu ba su iya hada ido dashi don tsoron kar ya cutar dasu musamman mata.

 

Hakan ya sa nake ganin mutanenmu basu waye wajen kallon fim ba domin suna daukar abin kamar da gaske akeyi,kokuma halayyar da mutum ya nuna a cikin fim haka abin yake a waje wamda ko kusa ba haka abin yake ba sau da dama ka kan samu jarumi mai tausayi ko Imani a cikin fim amma ka same shi akasin haka a zahiri,haka kuma ka kan samu mutum marar imani a cikin shirin fim amma ka samu akasin haka a zahiri kamar dai ni kenan.

 

Da yake karin haske a kan abinda ya sa kwana biyu a daina ganinsa a fina-finai kamar yadda yake fitowa a baya, Tanimu ya bayyana cewar har yanzu yana sha’awar harkar fim duk da dai cewa ta fara isar shi amma rashin samun wata tsayayyar sana’ar ya sa har yanzu yake a Industry.Dangane da daina ganin sa a fina finai kuwa ya ce shi bai dauki sana’ar fim ko ayi ko a mutu kamar yadda wasu suke daukar ta ba.

 

Hakan ya sa idan masu shirya fina-finai (Furodusoshi) suka nemi ya zo su yi aiki tare da shi zai zo amma idan basu neme shi ba, shima ba zai tafi wurinsu ya na kamun kafa a kan su saka shi a fim ba, daga karshe Tanimu Akawu ya tabbatar da cewar harkar fim ta yi mashi riga da wando domin kuwa ta sanadiyar wannan sana’a mutane da dama suka sanshi kuma shima ya san mutane da dama.

 

Kuma yanzu haka yana fadada hanyar neman abincinsa ta hanyar tallace-tallacen ‘yan siyasa da sauran kamfanoni masu bukata, inda ya ce da ba dan wannan sana’a ta shi ta fim ba da bai samu wannan daukakar da mutane suke ganin yana da ita har suke bashi tallace-tallace ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Wace Wainar Ake Toyawa A Jihar Kaduna?

Next Post

Mai Martaba Sarkin Ningi Ya Rasu Yana Da Shekara 88

Related

Ina Fatan Watsi Da Harkar Fim Nan Gaba —Umar Hassan
Nishadi

Ina Fatan Watsi Da Harkar Fim Nan Gaba —Umar Hassan

4 days ago
Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango
Nishadi

Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

6 days ago
Duk Wanda Ya Girme Ni Ubangidana Ne A Harkar Fim – Hauwa Garba (2)
Nishadi

Duk Wanda Ya Girme Ni Ubangidana Ne A Harkar Fim – Hauwa Garba (2)

2 weeks ago
Masana’antar Kannywood Na Tsananin Buqatar Addu’a – Hauwa Garba
Nishadi

Masana’antar Kannywood Na Tsananin Buqatar Addu’a – Hauwa Garba

3 weeks ago
Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah
Nishadi

Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

4 weeks ago
Na Hadu Da Azzalumai Da Mayaudara Farkon Shigata Kannywood – Dan’duniya
Nishadi

Na Hadu Da Azzalumai Da Mayaudara Farkon Shigata Kannywood – Dan’duniya

1 month ago
Next Post
Mai Martaba Sarkin Ningi Ya Rasu Yana Da Shekara 88

Mai Martaba Sarkin Ningi Ya Rasu Yana Da Shekara 88

LABARAI MASU NASABA

Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

September 18, 2025
Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

September 18, 2025
Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

September 18, 2025
Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

September 18, 2025
Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

September 18, 2025
An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

September 18, 2025
NNPP

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

September 18, 2025
Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

September 18, 2025
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

September 18, 2025
Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

September 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.