• English
  • Business News
Wednesday, July 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mai Martaba Sarkin Ningi Ya Rasu Yana Da Shekara 88

by Khalid Idris Doya and Sulaiman
11 months ago
in Labarai
0
Mai Martaba Sarkin Ningi Ya Rasu Yana Da Shekara 88
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Allah ya yi wa mai martaba Sarkin Ningi, Alhaji (Dr.) Yunusa Muhammad Danyaya OON, rasuwa ya na da shekaru 88 a duniya.

 

Sarkin Mai daraja ta 1 ya shafe fiye da shekaru 40 a ƙaragar mulki, ya rasu da safiyar ranar Lahadi.

  • Mashawarcin Shugaban Amurka Kan Harkokin Tsaro Jake Sullivan Zai Ziyarci Kasar Sin 
  • Wace Wainar Ake Toyawa A Jihar Kaduna?

Rasuwar, babbar giɓi ce da ya bar wa al’ummar masarautar Ningi ta jihar Bauchi da ma ƙasa baki ɗaya, domin kuwa ya kasance sarki mai kima da mutunci a idon ɓangarorin al’umma daban-daban.

 

Labarai Masu Nasaba

Amurka Ta Tsaurara Matakan Bai Wa ‘Yan Nijeriya Biza

Sanata Natasha Ta Bayyana Dalilin Da Ya Sa Ba Ta Koma Majalisa Ba

An shirya cewa, za a yi wa Marigayin sallar jana’iza da ƙarfe 4 na yammaci yau Lahadi a masarautar Ningi kamar yadda addinin Musulunci ya tanadar.

 

A saƙon ta’aziyya da ya fitar cikin gaggawa, gwamnan jihar, Bauchi Bala Muhammad, ya koka da rashin tare da misalta Sarkin a matsayin jigon son zaman lafiya, adali wanda ya himmatu wajen kyautata jin daɗi da walwalar al’ummarsa.

 

Ya ce, a tsawon shekarun da ya shafe a mulki, ya kasance mai gudanar da mulki abun koyi, inganta haɗin kai, cigaba, zaman lafiya da kuma bunƙasar masarautar Ningi.

 

A cewar Gwamnan, tsarin mulkin marigayi ya taimaka sosai wajen kiyaye darajar sarauta, al’adu har ma da mutunta addinin musulunci, kuma hakan zai zama abun cigaba da koyi ga hakan ga ‘yan baya masu zuwa.

 

A kan wannan, ta cikin sanarwar da kakakinsa, Mukhtar Gidado ya fitar, gwamnan ya miƙa ta’aziyyarsa ga masarautar Ningi, iyalan mamacin da ma ɗaukacin al’ummar jihar Bauchi bisa wannan babban rashin da aka yi.

 

Ya nuna cewa za su cigaba da tuna Sarkin a matsayinsa na uba, jigo a rayuwarsu wanda ya taka muhimmiyar rawa wajen cigaban jihar Bauchi da ma Nijeriya.

 

Ya yi addu’ar Allah ya jiƙan marigayi Sarki ya sanya shi cikin Aljanna maɗaukakiya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BauchiSarkin NingiTarihin Masarautar Ningi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Fina-finai Masu Dogon Zango Koma Baya Ne Ga Masana’antar Kannywood – Tanimu Akawu

Next Post

Matsalar Kifewar Kwale-kwale A Jihar Jigawa

Related

Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa
Labarai

Amurka Ta Tsaurara Matakan Bai Wa ‘Yan Nijeriya Biza

3 hours ago
Sanata Natasha Ta Bayyana Dalilin Da Ya Sa Ba Ta Koma Majalisa Ba
Manyan Labarai

Sanata Natasha Ta Bayyana Dalilin Da Ya Sa Ba Ta Koma Majalisa Ba

4 hours ago
Dangote Ya Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa Naira 820
Manyan Labarai

Dangote Ya Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa Naira 820

6 hours ago
Malaman Firamare Sun Janye Yajin Aiki A Abuja, An Umarci Su Koma Bakin Aiki
Manyan Labarai

Malaman Firamare Sun Janye Yajin Aiki A Abuja, An Umarci Su Koma Bakin Aiki

7 hours ago
Tinubu Ba Zai Yarda Hayaniyar Siyasar 2027 Ta Ɗauke Masa Hankali Ba – Ministan Yaɗa Labarai
Labarai

Tinubu Ba Zai Yarda Hayaniyar Siyasar 2027 Ta Ɗauke Masa Hankali Ba – Ministan Yaɗa Labarai

15 hours ago
Igbo Ne Ke Aikata Laifuka A Kudu, Ba Fulani Makiyaya Ba – Gwamna Soludo
Manyan Labarai

Igbo Ne Ke Aikata Laifuka A Kudu, Ba Fulani Makiyaya Ba – Gwamna Soludo

17 hours ago
Next Post
Sarkin Ningi

Matsalar Kifewar Kwale-kwale A Jihar Jigawa

LABARAI MASU NASABA

An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Babu Wanda Ya Buƙaci Atiku Ka Da Ya Yi Takara A 2027 – ADC

July 9, 2025
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa

Amurka Ta Tsaurara Matakan Bai Wa ‘Yan Nijeriya Biza

July 9, 2025
Sanata Natasha Ta Bayyana Dalilin Da Ya Sa Ba Ta Koma Majalisa Ba

Sanata Natasha Ta Bayyana Dalilin Da Ya Sa Ba Ta Koma Majalisa Ba

July 9, 2025
Dangote Ya Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa Naira 820

Dangote Ya Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa Naira 820

July 9, 2025
Kofin Duniya: Chelsea Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Ta Doke Fluminense

Kofin Duniya: Chelsea Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Ta Doke Fluminense

July 9, 2025
Malaman Firamare Sun Janye Yajin Aiki A Abuja, An Umarci Su Koma Bakin Aiki

Malaman Firamare Sun Janye Yajin Aiki A Abuja, An Umarci Su Koma Bakin Aiki

July 9, 2025
Sin Ta Ware Yuan Biliyan 10 Don Shirye-Shiryen Ba Da Tallafin Aiki

Sin Ta Ware Yuan Biliyan 10 Don Shirye-Shiryen Ba Da Tallafin Aiki

July 9, 2025
Tinubu Ba Zai Yarda Hayaniyar Siyasar 2027 Ta Ɗauke Masa Hankali Ba – Ministan Yaɗa Labarai

Tinubu Ba Zai Yarda Hayaniyar Siyasar 2027 Ta Ɗauke Masa Hankali Ba – Ministan Yaɗa Labarai

July 8, 2025
Firaminsitan Sin: Dole Ne Hadin Gwiwar Brics Ya Gaggauta Kafa Ka’idar Ciniki Da Tattalin Arzikin Duniya Mai Adalci Da Bude Kofa

Firaminsitan Sin: Dole Ne Hadin Gwiwar Brics Ya Gaggauta Kafa Ka’idar Ciniki Da Tattalin Arzikin Duniya Mai Adalci Da Bude Kofa

July 8, 2025
Babatun Lai Ching-Te Ba Zai Taba Girgiza Kasancewar Sin Day Tak A Duniya Ba

Babatun Lai Ching-Te Ba Zai Taba Girgiza Kasancewar Sin Day Tak A Duniya Ba

July 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.