• English
  • Business News
Thursday, November 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Fintiri Ya Rantsar Da Mace Ta Farko Babbar Mai Shari’a A Adamawa

by Muh'd Shafi'u Saleh
3 years ago
Fintiri

Gwamnan jihar Adamawa Ahamdu Umaru Fintiri, ya rantsar da mace ta farko Justis Hafsat AbdulRahman, a matsayar babbar Mai Shari’a kuma alkaliyar-alkalan jihar, ranar Litinin, a gidan gwamnati dake Yola fadar jihar Adamawa.

 

Haka kuma cikin mutanen da gwamnan ya rantsar sun hada da Ibrahim Sudi da Audu Balami, a matsayin manyan alkalan kotun Shari’ar Musulunci da kotun daukaka kara ta shari’ar gargajiya.

  • ‘Yansanda Sun Damke Wani Mutum Da Ya Kashe Matarsa A Adamawa

Da yake jawabi jimkadan da rantsarwar gwamna Ahamadu Umaru Fintiri, yace sabbin alkalan-alkalan jihar su na da cikakken ikon gudanar da aikinsu kamar yadda doka ta ba su, saboda haka zaiyi aiki da su a matsayinsu cikakkun alkalai.

 

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Don Karɓo Rancen N1.15trn Don Cike Giɓin Kasafin Kuɗin 2025

Jirgin Ƙasa Ya Murƙushe Direban Adaidaita Sahu Da Fasinja A Jos

Gwamnan ya kuma yabawa babbar Mai shari’a Hafsat AbdulRahman bisa kwarewa da gogiwa da jajircewar da take dashi, da yace hakan ya kai ga kwarewarta da rike mukamai a fannin shari’a a tsawon shekarun aikin da ta yi.

 

Ya ci gaba da cewa “gwamnatinmu ta kafa tarihi ta hanyar rantsar da mace a matsayar babbar alkalin-alkalan jiha, nasararta babban ci gaba ne ga mata, hadarin da ‘yancin yara mata ke ciki, ya nuna abune da yanzu akwai kyakkyawar fata.

 

“Iyaye, idan muna nemawa yayanmu mata hanyar da ta dace, wannan shine ingantaccen wurin da za mu zo, kyakkyawar fata, ‘yanci, gaskiya da kuma aiki tukuru, kallafawa, amana da adalci.

 

“Rantsar da ku, yana daga shawarwarin da majalisar shari’a ta NJC ta bamu, shawarar na su wata alamace ta aikinmu ya dace, aiki ne wanda NCJ ke da ikon nada manyan masu shari’a” inji Fintiri.

 

Da take jawabin godiya a madadin alkalan, Mai shari’a Hafsat AbdulRahman, ta yabawa gwamnan bisa gaggawar amincewa da shawarwarin majalisar shari’a ta kasa (NCJ).

 

Justis Hafsat, ta kuma tabbatar da cewa za su yi abinda ya dace, domin daukaka matsayin shari’a a jihar da rantsarwar da suka dauka,

 

Ta kuma yaba da babban gudumuwar da gwamnatin jihar ke ci gaba da bayarwa wajan daukaka matsayin shari’a, musamman ta fuskacin daukan ma’aikata.

 

Ta ce “daga shekarar 2020 zuwa yanzu, alkalan-alkalan manyan kotuna 10, garan Khadi 3, kotunan daukaka kara da manyan alkalan kotunan shari’ar gargajiya 3, aka nada da rantsar da su” inji Mai shari’a Hafsat.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Amnesty International Ta Soki Tinubu Kan Yi Wa Masu Laifin Take Haƙƙin Ɗan Adam Afuwa
Labarai

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Don Karɓo Rancen N1.15trn Don Cike Giɓin Kasafin Kuɗin 2025

November 6, 2025
Jirgin Ƙasa Ya Murƙushe Direban Adaidaita Sahu Da Fasinja A Jos
Labarai

Jirgin Ƙasa Ya Murƙushe Direban Adaidaita Sahu Da Fasinja A Jos

November 6, 2025
Ɓarayi Sun Shiga Ofishin Shugaban Karama Hukuma A Kano, Sun Tafka Sata
Labarai

Ɓarayi Sun Shiga Ofishin Shugaban Karama Hukuma A Kano, Sun Tafka Sata

November 6, 2025
Next Post
Buhari Ya Kafa Hukumar Gudanarwa Ta Hukumar Haɓaka Arewa-maso-gabas (NEDC)  

Buhari Ya Kafa Hukumar Gudanarwa Ta Hukumar Haɓaka Arewa-maso-gabas (NEDC)  

LABARAI MASU NASABA

Amnesty International Ta Soki Tinubu Kan Yi Wa Masu Laifin Take Haƙƙin Ɗan Adam Afuwa

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Don Karɓo Rancen N1.15trn Don Cike Giɓin Kasafin Kuɗin 2025

November 6, 2025
Jirgin Ƙasa Ya Murƙushe Direban Adaidaita Sahu Da Fasinja A Jos

Jirgin Ƙasa Ya Murƙushe Direban Adaidaita Sahu Da Fasinja A Jos

November 6, 2025
Osimhen Ya Kafa Tarihi A Gasar Zakarun Turai Bayan Zura Ƙwallo 3 A Ragar Ajax

Osimhen Ya Kafa Tarihi A Gasar Zakarun Turai Bayan Zura Ƙwallo 3 A Ragar Ajax

November 6, 2025
Ɓarayi Sun Shiga Ofishin Shugaban Karama Hukuma A Kano, Sun Tafka Sata

Ɓarayi Sun Shiga Ofishin Shugaban Karama Hukuma A Kano, Sun Tafka Sata

November 6, 2025
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP

Majalisa Ta Ɗage Tantance Ministan Tinubu Saboda Rashin Rahoton Tsaro

November 6, 2025
Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

November 5, 2025
Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

November 5, 2025
Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

November 5, 2025
Majalisar Dattawa

Majalisa Ta Amince Da Ɗaurin Shekaru 14 A Gidan Yari Ga Malamai Masu Cin Zarafin Mata A Jami’o’i

November 5, 2025
Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin

Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin

November 5, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.