ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 11, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yansanda Sun Damke Wani Mutum Da Ya Kashe Matarsa A Adamawa

by Sadiq
3 years ago
Adamawa

Rundunar ‘yansandan Jihar Adamawa ta cafke wani magidanci mai suna Aminu Abubakar mai shekara 56 bisa laifin kashe matarsa.

Abubakar, mazaunin Lelewaji, a yankin Shagari Phase 2 a Yola, a karamar hukumar Yola ta Kudu a jihar, an zargin ya yi wa matarsa ​​Nana Fadimatu dukan tsiya wanda ya yi ajalinta har lahira, bayan ya fahimci shirinta na auren wani mutum.

  • Alkawarin Da Tinubu Ya Yi Wa Ma’aikatan Gwamnati
  • Batun Sake Nazarin Dakatar Da Tsohon Sarkin Kano…

Ana zargin Abubakar da sakin mamaciyar har sau biyu tare da ba ta masauki ba, har zuwa lokacin da za a sasanta auren.

ADVERTISEMENT

Amma kafin su sasanta, an ce marigayiyar na shirin auren wani mutum, lamarin da ya harzuka Abubakar, inda ya shiga tashin hankali.

Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, a cikin wata sanarwa da ya fitar, ya ce, “Wanda ake zargin, Aminu Abubakar, mazaunin Lelewaji, Shagari Phase 2, a karamar hukumar Yola ta Kudu, ya yi wa marigayiya Nana Fadimatu dukan tsiya bayan wata ‘yar rashin jituwa da ta barke tsakaninsu lokacin da ya ji labarin cewa marigayiyar za ta auri wani daban.

LABARAI MASU NASABA

2027: Tinubu Ya Sake Zaɓar Shettima A Matsayin Abokin Takararsa

An Ceto Dukkanin Ɗalibai Da Malaman Da Aka Sace A Jihar Oyo — Fadar Shugaban Ƙasa

“Wanda ake zargin ya fusata ya danne ta a ranar 5/5/2023 da misalin karfe 10 na dare, inda ya buge ta da karfi ta hanyar buga mata wani abu mai kauri sakamakon hakan ta fadi a sume sannan aka sanar da cewa ta mutu.

“’Yansanda sun kama wanda ake zargin ne a hedikwatar ‘yansanda ta Shagari sakamakon rahoton da aka samu daga sabon angon nata, Mahmud Rufa’i na Shagari a karamar hukumar Yola ta Kudu.

“Bincike ya zuwa yanzu ya nuna cewa wanda ake zargin shi ne manajan kamfanin ruwa na Anasam a gidan Jambutu 50 yana da ’ya daya tare da marigayiyar bayan shekaru tara da aurensu.

“Kwamishanan ‘yansanda CP Afolabi Babatola yayin da yake bayyana kaduwarsa ya yaba wa DPO din Shagari bisa kama wanda ake zargin.”

Ya kara da cewa CP din ya umarci jami’an sashen yaki da kisan kai da ke ma’aikatan CID na jihar da su dauki nauyin gudanar da bincike tare da tabbatar da cewa doka ta yi aiki.

Haka zalika ya yi kira ga jama’ar yankin da su rika kai rahoton mutanen da ba su da alaka da su a unguwanninsu ga ‘yansanda.

MASU ALAKA

2027: Tinubu Ya Sake Zaɓar Shettima A Matsayin Abokin Takararsa
Da ɗumi-ɗuminsa

2027: Tinubu Ya Sake Zaɓar Shettima A Matsayin Abokin Takararsa

July 10, 2026
An Ceto Dukkanin Ɗalibai Da Malaman Da Aka Sace A Jihar Oyo — Fadar Shugaban Ƙasa
Manyan Labarai

An Ceto Dukkanin Ɗalibai Da Malaman Da Aka Sace A Jihar Oyo — Fadar Shugaban Ƙasa

July 10, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Manyan Labarai

Sana’ar Ɗinki: Yadda Telolin Zariya Suka Yi Fice A Sassan Afirka

July 10, 2026
Next Post
Sin: Za A Harba Kumbon Jigilar Kaya Samfurin Tianzhou-6

Sin: Za A Harba Kumbon Jigilar Kaya Samfurin Tianzhou-6

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Fitar Da Shirin Kai Wa Matakin Koli Na Fitar Da Hayakin Carbon

Kasar Sin Ta Fitar Da Shirin Kai Wa Matakin Koli Na Fitar Da Hayakin Carbon

July 10, 2026
Sin Ta Yi Nasarar Dawo Da Rokar Da Ake Sarrafa Dawowarta A Tashin Farko Na Samfurin Long March-10B

Sin Ta Yi Nasarar Dawo Da Rokar Da Ake Sarrafa Dawowarta A Tashin Farko Na Samfurin Long March-10B

July 10, 2026
CMG Ya Gabatar Da Shiri Na Musamman Mai Taken “Samun Nasara Dangane Da AI+” A Ketare

CMG Ya Gabatar Da Shiri Na Musamman Mai Taken “Samun Nasara Dangane Da AI+” A Ketare

July 10, 2026
Zargin Da Wasu Sassa Ke Yiwa Kasar Sin Na Takure Sauran Kasashe Masu Tasowa Ba Shi da Tushe Ko Makama

Zargin Da Wasu Sassa Ke Yiwa Kasar Sin Na Takure Sauran Kasashe Masu Tasowa Ba Shi da Tushe Ko Makama

July 10, 2026
2027: Tinubu Ya Sake Zaɓar Shettima A Matsayin Abokin Takararsa

2027: Tinubu Ya Sake Zaɓar Shettima A Matsayin Abokin Takararsa

July 10, 2026
Taron Kara Wa Juna Sani Na Duniya Ya Yi Nazari Kan Kwarewar Kasar Sin Wajen Rage Talauci

Taron Kara Wa Juna Sani Na Duniya Ya Yi Nazari Kan Kwarewar Kasar Sin Wajen Rage Talauci

July 10, 2026
An Ceto Dukkanin Ɗalibai Da Malaman Da Aka Sace A Jihar Oyo — Fadar Shugaban Ƙasa

An Ceto Dukkanin Ɗalibai Da Malaman Da Aka Sace A Jihar Oyo — Fadar Shugaban Ƙasa

July 10, 2026
Xi Ya Zanta Da Shugabar Namibia

Xi Ya Zanta Da Shugabar Namibia

July 10, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Ko Ka San Dalilin Da Ya Sa Chana Da Indiya Ba Sa Buga Kofin Duniya?

July 10, 2026
“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

July 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.