• Leadership Hausa
Friday, December 8, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Fintiri Ya Rantsar Da Mace Ta Farko Babbar Mai Shari’a A Adamawa

by Muh'd Shafi'u Saleh
7 months ago
in Labarai
0
Fintiri Ya Rantsar Da Mace Ta Farko Babbar Mai Shari’a A Adamawa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan jihar Adamawa Ahamdu Umaru Fintiri, ya rantsar da mace ta farko Justis Hafsat AbdulRahman, a matsayar babbar Mai Shari’a kuma alkaliyar-alkalan jihar, ranar Litinin, a gidan gwamnati dake Yola fadar jihar Adamawa.

 

Haka kuma cikin mutanen da gwamnan ya rantsar sun hada da Ibrahim Sudi da Audu Balami, a matsayin manyan alkalan kotun Shari’ar Musulunci da kotun daukaka kara ta shari’ar gargajiya.

  • ‘Yansanda Sun Damke Wani Mutum Da Ya Kashe Matarsa A Adamawa

Da yake jawabi jimkadan da rantsarwar gwamna Ahamadu Umaru Fintiri, yace sabbin alkalan-alkalan jihar su na da cikakken ikon gudanar da aikinsu kamar yadda doka ta ba su, saboda haka zaiyi aiki da su a matsayinsu cikakkun alkalai.

 

Labarai Masu Nasaba

Hukumar Kwastam A Kano Ta Samu Kudin Shiga Naira Biliyan 6.9 A Nuwamba

Kyautata Rayuwar Matasa Ne Fatanmu – Kwamoti La’ori 

Gwamnan ya kuma yabawa babbar Mai shari’a Hafsat AbdulRahman bisa kwarewa da gogiwa da jajircewar da take dashi, da yace hakan ya kai ga kwarewarta da rike mukamai a fannin shari’a a tsawon shekarun aikin da ta yi.

 

Ya ci gaba da cewa “gwamnatinmu ta kafa tarihi ta hanyar rantsar da mace a matsayar babbar alkalin-alkalan jiha, nasararta babban ci gaba ne ga mata, hadarin da ‘yancin yara mata ke ciki, ya nuna abune da yanzu akwai kyakkyawar fata.

 

“Iyaye, idan muna nemawa yayanmu mata hanyar da ta dace, wannan shine ingantaccen wurin da za mu zo, kyakkyawar fata, ‘yanci, gaskiya da kuma aiki tukuru, kallafawa, amana da adalci.

 

“Rantsar da ku, yana daga shawarwarin da majalisar shari’a ta NJC ta bamu, shawarar na su wata alamace ta aikinmu ya dace, aiki ne wanda NCJ ke da ikon nada manyan masu shari’a” inji Fintiri.

 

Da take jawabin godiya a madadin alkalan, Mai shari’a Hafsat AbdulRahman, ta yabawa gwamnan bisa gaggawar amincewa da shawarwarin majalisar shari’a ta kasa (NCJ).

 

Justis Hafsat, ta kuma tabbatar da cewa za su yi abinda ya dace, domin daukaka matsayin shari’a a jihar da rantsarwar da suka dauka,

 

Ta kuma yaba da babban gudumuwar da gwamnatin jihar ke ci gaba da bayarwa wajan daukaka matsayin shari’a, musamman ta fuskacin daukan ma’aikata.

 

Ta ce “daga shekarar 2020 zuwa yanzu, alkalan-alkalan manyan kotuna 10, garan Khadi 3, kotunan daukaka kara da manyan alkalan kotunan shari’ar gargajiya 3, aka nada da rantsar da su” inji Mai shari’a Hafsat.

ShareTweetSendShare
Previous Post

Qin Gang Ya Gana Da Jakadan Amurka Dake Sin

Next Post

Buhari Ya Kafa Hukumar Gudanarwa Ta Hukumar Haɓaka Arewa-maso-gabas (NEDC)  

Related

kwastam
Labarai

Hukumar Kwastam A Kano Ta Samu Kudin Shiga Naira Biliyan 6.9 A Nuwamba

59 mins ago
Kyautata Rayuwar Matasa Ne Fatanmu – Kwamoti La’ori 
Labarai

Kyautata Rayuwar Matasa Ne Fatanmu – Kwamoti La’ori 

4 hours ago
NAHCON
Labarai

Hajjin 2024: NAHCON Za Ta Sabunta Ka’idojin Ciyar Da Alhazai Da Masaukansu

5 hours ago
kaduna
Manyan Labarai

Matsalar Da Ta Haddasa Harin Bom Na Kaduna

6 hours ago
Ministan Yaɗa Labarai Ya Kafa Kwamitin Tsara Cusa Ɗa’a Da Kishin Ƙasa
Labarai

Ministan Yaɗa Labarai Ya Kafa Kwamitin Tsara Cusa Ɗa’a Da Kishin Ƙasa

14 hours ago
Shettima Ya Ziyarci Wadanda Sojoji Suka Jefawa Bam A Kaduna
Manyan Labarai

Shettima Ya Ziyarci Wadanda Sojoji Suka Jefawa Bam A Kaduna

16 hours ago
Next Post
Buhari Ya Kafa Hukumar Gudanarwa Ta Hukumar Haɓaka Arewa-maso-gabas (NEDC)  

Buhari Ya Kafa Hukumar Gudanarwa Ta Hukumar Haɓaka Arewa-maso-gabas (NEDC)  

LABARAI MASU NASABA

kwastam

Hukumar Kwastam A Kano Ta Samu Kudin Shiga Naira Biliyan 6.9 A Nuwamba

December 8, 2023
Al’ajabi: Saurayi Ya Yi Wa Zakara Fyade A Adamawa

Al’ajabi: Saurayi Ya Yi Wa Zakara Fyade A Adamawa

December 8, 2023
tallafi

Gwamnatin Tarayya Za Ta Fara Raba Tallafi Ga Masu Kananan Masana’antu

December 8, 2023
Akpabio

‘Yan Nijeriya Ba Sa Amanna Da Jam’iyyun Siyasa – Akpabio

December 8, 2023
Manzon Allah

Daga Cikin Mutane Aka Aiko Manzon Allah Amma Ba Mutum Ne Kamar Kowa Ba (SAW)

December 8, 2023
Kyautata Rayuwar Matasa Ne Fatanmu – Kwamoti La’ori 

Kyautata Rayuwar Matasa Ne Fatanmu – Kwamoti La’ori 

December 8, 2023
Ba Za A Cimma Wannan Yarjejeniya Ba Tare Da Taimakon Sin Ba

Ba Za A Cimma Wannan Yarjejeniya Ba Tare Da Taimakon Sin Ba

December 8, 2023
NAHCON

Hajjin 2024: NAHCON Za Ta Sabunta Ka’idojin Ciyar Da Alhazai Da Masaukansu

December 8, 2023
kaduna

Matsalar Da Ta Haddasa Harin Bom Na Kaduna

December 8, 2023
Ministan Yaɗa Labarai Ya Kafa Kwamitin Tsara Cusa Ɗa’a Da Kishin Ƙasa

Ministan Yaɗa Labarai Ya Kafa Kwamitin Tsara Cusa Ɗa’a Da Kishin Ƙasa

December 7, 2023
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.