ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Fintiri Ya Rantsar Da Mace Ta Farko Babbar Mai Shari’a A Adamawa

by Muh'd Shafi'u Saleh
3 years ago
Fintiri

Gwamnan jihar Adamawa Ahamdu Umaru Fintiri, ya rantsar da mace ta farko Justis Hafsat AbdulRahman, a matsayar babbar Mai Shari’a kuma alkaliyar-alkalan jihar, ranar Litinin, a gidan gwamnati dake Yola fadar jihar Adamawa.

 

Haka kuma cikin mutanen da gwamnan ya rantsar sun hada da Ibrahim Sudi da Audu Balami, a matsayin manyan alkalan kotun Shari’ar Musulunci da kotun daukaka kara ta shari’ar gargajiya.

ADVERTISEMENT
  • ‘Yansanda Sun Damke Wani Mutum Da Ya Kashe Matarsa A Adamawa

Da yake jawabi jimkadan da rantsarwar gwamna Ahamadu Umaru Fintiri, yace sabbin alkalan-alkalan jihar su na da cikakken ikon gudanar da aikinsu kamar yadda doka ta ba su, saboda haka zaiyi aiki da su a matsayinsu cikakkun alkalai.

 

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Gwamnan ya kuma yabawa babbar Mai shari’a Hafsat AbdulRahman bisa kwarewa da gogiwa da jajircewar da take dashi, da yace hakan ya kai ga kwarewarta da rike mukamai a fannin shari’a a tsawon shekarun aikin da ta yi.

 

Ya ci gaba da cewa “gwamnatinmu ta kafa tarihi ta hanyar rantsar da mace a matsayar babbar alkalin-alkalan jiha, nasararta babban ci gaba ne ga mata, hadarin da ‘yancin yara mata ke ciki, ya nuna abune da yanzu akwai kyakkyawar fata.

 

“Iyaye, idan muna nemawa yayanmu mata hanyar da ta dace, wannan shine ingantaccen wurin da za mu zo, kyakkyawar fata, ‘yanci, gaskiya da kuma aiki tukuru, kallafawa, amana da adalci.

 

“Rantsar da ku, yana daga shawarwarin da majalisar shari’a ta NJC ta bamu, shawarar na su wata alamace ta aikinmu ya dace, aiki ne wanda NCJ ke da ikon nada manyan masu shari’a” inji Fintiri.

 

Da take jawabin godiya a madadin alkalan, Mai shari’a Hafsat AbdulRahman, ta yabawa gwamnan bisa gaggawar amincewa da shawarwarin majalisar shari’a ta kasa (NCJ).

 

Justis Hafsat, ta kuma tabbatar da cewa za su yi abinda ya dace, domin daukaka matsayin shari’a a jihar da rantsarwar da suka dauka,

 

Ta kuma yaba da babban gudumuwar da gwamnatin jihar ke ci gaba da bayarwa wajan daukaka matsayin shari’a, musamman ta fuskacin daukan ma’aikata.

 

Ta ce “daga shekarar 2020 zuwa yanzu, alkalan-alkalan manyan kotuna 10, garan Khadi 3, kotunan daukaka kara da manyan alkalan kotunan shari’ar gargajiya 3, aka nada da rantsar da su” inji Mai shari’a Hafsat.

Fintiri
Muh'd Shafi'u Saleh
+ postsBio
  • Muh'd Shafi'u Saleh
    https://hausa.leadership.ng/author/muhd-shafiu-saleh/
    Jami’in Tsaro Ya Mayar da Dala 505 Da Riyal 30 Da Ya Tsinta A Yola
  • Muh'd Shafi'u Saleh
    https://hausa.leadership.ng/author/muhd-shafiu-saleh/
    Shahararren Malamin Addinin Islama A Adamawa Sheikh Ibrahim Abubakar Daware Ya Rasu
  • Muh'd Shafi'u Saleh
    https://hausa.leadership.ng/author/muhd-shafiu-saleh/
    An Yi Wa ‘Yansanda 110 Ƙarin Girma A Adamawa
  • Muh'd Shafi'u Saleh
    https://hausa.leadership.ng/author/muhd-shafiu-saleh/
    Gwamna Fintiri Ya Nada Sabbin Sarakuna 7 A Jihar Adamawa

MASU ALAKA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato
Tsaro

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Next Post
Buhari Ya Kafa Hukumar Gudanarwa Ta Hukumar Haɓaka Arewa-maso-gabas (NEDC)  

Buhari Ya Kafa Hukumar Gudanarwa Ta Hukumar Haɓaka Arewa-maso-gabas (NEDC)  

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.