• English
  • Business News
Monday, October 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Firaministan Habasha Ya Gana Da Ministan Harkokin Wajen Kasar Sin Qin Gang

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Firaministan Habasha Ya Gana Da Ministan Harkokin Wajen Kasar Sin Qin Gang
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Firaministan kasar Habasha Abiy Ahmed Ali ya gana da ministan harkokin wajen kasar Sin Qin Gang dake ziyara a kasar a birnin Addis Ababa.

Firaminista Abiy ya bayyana cewa, ministan harkokin wajen kasar Sin ya zabi kasar Habasha a matsayin zango na farko na ziyararsa bayan hawan kujerar mukaminsa, lamarin da ya shaida zumunta mai zurfi da muhimmancin dangantakar dake tsakanin kasashen biyu.

  • Wasan Kwallon Kafa Na Mata A Sin: Ba Za Mu Yi Watsi Da Burinmu Na Cimma Nasara Ba – Shui Qingxia

Ya ce an samu nasarori da dama kan hadin gwiwar dake tsakanin kasar Habasha da kasar Sin a fannonin ayyukan more rayuwa, da tattalin arziki ba tare da gurbata muhalli ba, da aikin gona, da gina yankin raya masana’antu da dai sauransu, wadanda ke da babbar ma’ana, wajen sa kaimi ga raya tattalin arzikin kasar Habasha da sanya ta cikin jerin kasashen dake kan gaba a nahiyar Afirka, kana ya yi maraba da karin kamfanonin Sin da su je kasar Habasha don zuba jari da gudanar da ayyuka.

A nasa bangare, Qin Gang ya bayyana cewa, a cikin fiye da rabin karni bayan kasashen Sin da Habasha sun kulla dangantakar diplomasiyya a tsakaninsu, ko da yake yanayin duniya ya sauya, kasashen biyu sun ci gaba da goyon bayan juna da yin kokari tare, wanda ya zama misalin hadin gwiwar dake tsakanin kasashe masu tasowa. Ya ce kasar Sin ta nuna goyon baya ga kasar Habasha wajen bin hanyar samun ci gaba da ta dace da yanayinta. Haka kuma, kasar Sin tana son zurfafa hadin gwiwar dake tsakanin kasashen biyu a fannoni da dama, da sa kaimi ga karin kamfanonin kasar Sin su zuba jari a kasar Habasha da shiga aikin sake gina kasar. Qin ya kara da cewa, kasar Sin tana son kasar Habasha ta samar da yanayi mai kyau na yin ciniki da daukar matakai don tabbatar da tsaro da moriyar ma’aikata da hukumomin kasar Sin.

Bugu da kari, minista Qin Gang ya tattauna da manema labarai, tare da mataimakin firaministan Habasha, kana ministan harkokin wajen kasar Demeke Mekonnen, bayan tattaunawarsu a Addis Ababa, babban birnin Habasha.

Labarai Masu Nasaba

CMG Zai Watsa Shirin Nishadantarwa Na Murnar Bikin Zhongqiu Gobe Da Dare

Yawan Mutanen Da Suka Yi Zirga-zirga A Rabin Farkon Hutun Bikin Kafuwar PRC Da Bikin Zhongqiu Ya Kai Biliyan 1 Da Miliyan 243

Da aka nemi jin ra’ayinsa game da yarjejeniyar zaman lafiya ta Habasha da ci gaban da aka samu dangane da shawarar da Sin ta gabatar ta “Makomar Zaman Lafiya da Ci Gaban Kahon Afrika” a Habasha, Qin Gang ya ce, Habasha gida ne na bai daya ga al’ummar kasar, ciki har da mutanen Tigray.

Ya ce kasar Sin ta kasance mai girmama cikakken ikon Habasha da yankunanta, kana tana mara baya ga gwamnatin kasar da al’ummarta, a kokarinsu na cimma zaman lafiya da hadin kai da kuma neman ci gaba.

Da ya yi waiwaye kan ziyarar manzon musamman na Sin a kahon Afrika, Xue Bing ya kai wasu kasashen yankin, Qin Gang ya ce kasar Sin ta goyi bayan babban taron zaman lafiya na kahon Afrika na farko, wanda ya bayar da gudunmawa ga cimma matsaya tsakanin dukkan bangarori da inganta zaman lafiya da ci gaban yankin.

Ya kuma bayyana cewa, Sin ta samar da kashi-kashi na kayayyakin abinci da alluran rigakafi da sauran kayayyakin jin kai ga Habasha, domin taimakawa inganta rayuwar al’ummomin dake yankuna masu fama da rikici.

Dadin dadawa, kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Wang Wenbin, ya ce ziyarar da ministan harkokin wajen kasar Sin Qin Gang ya fara a wasu kasashen Afirka, jim kadan da kama aikinsa, ta shaida yadda kasar Sin ke darajanta zumuncin da ke tsakaninta da kasashen Afirka, wadda kuma ke da nufin kara dinke zumunci tsakanin sassan biyu.

Wang Wenbin ya ce, bana ce shekara ta 33 a jere, da ministan harkokin wajen Sin ke kai ziyarar aiki ta farko a duk shekara kasashen Afirka.

A ranar 30 ga watan Disamban da ya gabata ne aka nada Qin Gang a matsayin ministan harkokin wajen kasar Sin, ya kuma fara ziyarar a ranar Talata, inda ya fara da yada zango a kasar Habasha. (Faeza Mustapha, Saminu Alhassan)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 2 Tare Da Yin Garkuwa Da Matan Aure 4 A Kaduna

Next Post

NIS Za Ta Ƙaddamar Da Cibiyar Bayar Da Sabon Ingantaccen Fasfo A Zariya Da Daura

Related

CMG Zai Watsa Shirin Nishadantarwa Na Murnar Bikin Zhongqiu Gobe Da Dare
Daga Birnin Sin

CMG Zai Watsa Shirin Nishadantarwa Na Murnar Bikin Zhongqiu Gobe Da Dare

2 hours ago
Yawan Mutanen Da Suka Yi Zirga-zirga A Rabin Farkon Hutun Bikin Kafuwar PRC Da Bikin Zhongqiu Ya Kai Biliyan 1 Da Miliyan 243
Daga Birnin Sin

Yawan Mutanen Da Suka Yi Zirga-zirga A Rabin Farkon Hutun Bikin Kafuwar PRC Da Bikin Zhongqiu Ya Kai Biliyan 1 Da Miliyan 243

3 hours ago
Kamfanin Sin Ya Kaddamar Da Ginin Katafaren Wurin Shakatawa Na Zamani A Ghana
Daga Birnin Sin

Kamfanin Sin Ya Kaddamar Da Ginin Katafaren Wurin Shakatawa Na Zamani A Ghana

4 hours ago
Za A Gudanar Da Taron Motoci Masu Amfani Da Fasahohin Zamani Na Duniya Na Shekarar 2025 A Beijing
Daga Birnin Sin

Za A Gudanar Da Taron Motoci Masu Amfani Da Fasahohin Zamani Na Duniya Na Shekarar 2025 A Beijing

5 hours ago
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Ziyarci Italiya Da Switzerland
Daga Birnin Sin

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Ziyarci Italiya Da Switzerland

6 hours ago
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa
Daga Birnin Sin

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

1 day ago
Next Post
NIS Za Ta Ƙaddamar Da Cibiyar Bayar Da Sabon Ingantaccen Fasfo A Zariya Da Daura

NIS Za Ta Ƙaddamar Da Cibiyar Bayar Da Sabon Ingantaccen Fasfo A Zariya Da Daura

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Ƙaryata Rahoton Cewa Ƴan Bindiga Sun Mamaye Sansaninsu A Kwara

Sojoji Sun Ƙaryata Rahoton Cewa Ƴan Bindiga Sun Mamaye Sansaninsu A Kwara

October 5, 2025
Kotu Ta Kori Buƙatar Ministan Tinubu Na Hana Fitar Da Takardun Karatunsa

Kotu Ta Kori Buƙatar Ministan Tinubu Na Hana Fitar Da Takardun Karatunsa

October 5, 2025
CMG Zai Watsa Shirin Nishadantarwa Na Murnar Bikin Zhongqiu Gobe Da Dare

CMG Zai Watsa Shirin Nishadantarwa Na Murnar Bikin Zhongqiu Gobe Da Dare

October 5, 2025
Nijeriya Ta Zamo Ƙasa Mafi Ƙarancin Tsammanin Tsawon Rayuwa A Duniya

Nijeriya Ta Zamo Ƙasa Mafi Ƙarancin Tsammanin Tsawon Rayuwa A Duniya

October 5, 2025
Yawan Mutanen Da Suka Yi Zirga-zirga A Rabin Farkon Hutun Bikin Kafuwar PRC Da Bikin Zhongqiu Ya Kai Biliyan 1 Da Miliyan 243

Yawan Mutanen Da Suka Yi Zirga-zirga A Rabin Farkon Hutun Bikin Kafuwar PRC Da Bikin Zhongqiu Ya Kai Biliyan 1 Da Miliyan 243

October 5, 2025
NUJ Ta Yi Maraba Da Sakin Ƴan Jaridar Da DSS Ta Kama A Jana’izar Mahaifiyar Shugaban APC

NUJ Ta Yi Maraba Da Sakin Ƴan Jaridar Da DSS Ta Kama A Jana’izar Mahaifiyar Shugaban APC

October 5, 2025
Kamfanin Sin Ya Kaddamar Da Ginin Katafaren Wurin Shakatawa Na Zamani A Ghana

Kamfanin Sin Ya Kaddamar Da Ginin Katafaren Wurin Shakatawa Na Zamani A Ghana

October 5, 2025
Uwargidan Shugaban Ƙasa, Remi Tinubu, Ta Nuna Damuwa Kan Ƙarancin Malamai A Duniya

Uwargidan Shugaban Ƙasa, Remi Tinubu, Ta Nuna Damuwa Kan Ƙarancin Malamai A Duniya

October 5, 2025
Za A Gudanar Da Taron Motoci Masu Amfani Da Fasahohin Zamani Na Duniya Na Shekarar 2025 A Beijing

Za A Gudanar Da Taron Motoci Masu Amfani Da Fasahohin Zamani Na Duniya Na Shekarar 2025 A Beijing

October 5, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Ziyarci Italiya Da Switzerland

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Ziyarci Italiya Da Switzerland

October 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.