ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Za Ta Ƙaddamar Da Cibiyar Bayar Da Sabon Ingantaccen Fasfo A Zariya Da Daura

...Yayin Da Ganduje Ya Kaddamar Da Katafariyar Cibiyar Wallafa Fasfo A Kano

by Sabo Ahmad
4 years ago
NIS

A kokarin da take yi na inganta ayyukan samar da fasfo ga dimbin masu nema da ke zaune a Kano da kewaye, Hukumar Kula da Shige da Fice ta Kasa (NIS) ta kaddamar da Katafariyar Cibiyar Samar da Fasfo da za ta rika aiki ga ofisoshin fasfo na Jigawa, Katsina da kuma Dawakin Kudu da ke Kanon.

Da yake kaddamar da katafariyar cibiyar a ranar Laraba 11 ga Janairun 2023, Gwamna Abdullahi Umar na Jihar Kano ya taya NIS murna bisa dimbin nasarorin da take samu musamman kasancewarta ta farko da ta fara samar da sabon ingantaccen fasfo na zamani a duk fadin yankin Afirka.

Gwamnan wanda Kwamishinan Kasafin Kudi, Alhaji Danazumi Grazo ya wakilta ya jinjina wa NIS bisa kafa cibiyar a cikin Kano mai dimbin tarihi, yana mai cewa, ya yi amanna, zabar Kano da aka yi wajen kafa cibiyar ba zai rasa nasaba da yanayin zaman lafiya da ake mora a jihar ba.

ADVERTISEMENT

A jawabinsa, Babban Shugaban NIS, Isah Jere Idris, MFR, ya tabbatar wa da ‘yan Nijeriya cewa, ana samun ci gaba a shirin sauya fasalin fasfo da ake yi a halin yanzu, musannam kan tsarin yadda za a yi saurin gane waɗanda suka shigo daga sassa daban-daban na duniya.

Shugaban ya ce, yanzu haka a Kano, sun ƙaddamar da cibiyar aikin yin e-Passport da aka inganta na zamani, kuma suna ci gaba da faɗaɗawa zuwa sauran wurare.
Wanda ya wakilce shi a wajen taron, ACG Sadat Hassan, ya ce, ya yi matuƙar farin ciki da jin irin ci gaban da ake samu a dukkan sassan yin fasfo ɗin a dukkan faɗin ƙasar nan, wanda ya nuna yadda mutanenmu ke bayar da cikakken haɗin kai. “Mun shirya za mu shafe mako biyu cif muna yin wannan aikin daga yanzu har zuwa ranar 21 ga wannan watan na Janairu, wanda kuma a wannan lokacin ne za kamala shirin.”

LABARAI MASU NASABA

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

  • Tinubu Ne Kadai Zai Iya Magance Rashin Tsaro Da Tabarbarewar Tattalin Arziki – Buhari 

Ya kuma ƙara da cewa NIS za ta ci gaba da bayar da fasfo ɗin a tsakanin mako uku zuwa mako shida, kana iya tura bayananka, musamman ga mutanen da ba su da matsala wajen tura bayanan ko kuma a rubuta takardar buƙata.Ya ƙara faɗa da babbar murya cewa NIN na daga cikin shika-shikan yin fasfo wanda kuma dole a tabbatar da cewa, bayanan da ke cikinsu ba su saɓa ba.

“Muna ƙara samun ci gaba ne don haka muke kira ga masu neman fasfo ɗin su guji yin bayanan ƙarya su tabbatar sun yi bayanan da kansu kuma sun biya dukkan kuɗaɗen da hannunsu , za su shigar da bayanansu ta hanyar shiga wannan adireshi, passport.immigration.goɓ.ng.Za kuma mu ci gaba da ƙoƙarin kawo ƙarshen dukkan matsalolin da za a ci karo da su.”

Haka kuma ya ce, zai yi amfani da wannan damar wajen gode wa jama’a kan cikakken goyon bayan da suke samu a wajensu. Haka kuma ya nuna cewa, yanzu haka dai NIS ba ta ɗaukar mutane, kuma duk lokacin da za ta ɗauka za ta sanar a kafafe yaɗa labarai, wato lokacin da muka samu amincewar gwamnatin tarayya.

NIS

Shugaban hukumar, Jere ya tabbatar da cewa, jami’an hukumar a tsaye suke ƙyam wajen ganin ganin sun gudanar da ayyukansu kamar yadda doka ta tanada, saboda haka ne ne ma y ace kullun suke ƙara samun ci gaba wajen gudanar da ayyukansu musamman a ɓangaren gudanar da fasfo da ɓangaren tsaro da samun walwala.

Saboda haka ne ma NIS take son isar da saƙonta ga dukkan jama’a cewa akwai fasfo guda 110,000 da masu su ba su zo sun karɓa ba a jihohi 36 da ke ƙasar nan da Abuja. Saboda haka, shugaban hukumar ya raba manyan jami’an hukumar tun daga kan mataimakinsa zuwa shiyya-shiyya domin ganin an tafiyar ta tsarin bayar da fasfo ɗin kamar yadda ya kamata.

Saboda haka ne ma ake shawartar ‘yan Nijeriya waɗanda suka yi fasfo ɗin ba su karɓa ba su je ofishin yin fasfo na NIS ɗin su duba nasu.

NIS
Sabo Ahmad
+ postsBio
  • Sabo Ahmad
    https://hausa.leadership.ng/author/sabo-ahmad/
    An Gurfanar Da Mutum 3 Bisa Laifin Lakada Wa Wani Duka Har Lahira
  • Sabo Ahmad
    https://hausa.leadership.ng/author/sabo-ahmad/
    Dalilin Da Ya Sa Kotu Ta Tasa Keyar Dakta Idris Dutsen Tanshi Zuwa Gidan Yari
  • Sabo Ahmad
    https://hausa.leadership.ng/author/sabo-ahmad/
    Uwa Ta Mutu A Kokarin Raba Fada Tsakanin ‘Ya’yanta A Abuja
  • Sabo Ahmad
    https://hausa.leadership.ng/author/sabo-ahmad/
    ’Yan Fashi Sun Yi Shigar Injiniyoyi, Sun Saci Manyan Na’urorin Sadarwa

MASU ALAKA

Sabbin Ministoci
Labarai

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 
Labarai

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan
Manyan Labarai

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Next Post
An Yi Shawarwari Karo Na 8 Bisa Manyan Tsare-Tsare Tsakanin Sin Da AU

An Yi Shawarwari Karo Na 8 Bisa Manyan Tsare-Tsare Tsakanin Sin Da AU

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026
‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

July 15, 2026
Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.