ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Firaministan Habasha Ya Gana Da Ministan Harkokin Wajen Kasar Sin Qin Gang

by CMG Hausa
4 years ago
Habasha

Firaministan kasar Habasha Abiy Ahmed Ali ya gana da ministan harkokin wajen kasar Sin Qin Gang dake ziyara a kasar a birnin Addis Ababa.

Firaminista Abiy ya bayyana cewa, ministan harkokin wajen kasar Sin ya zabi kasar Habasha a matsayin zango na farko na ziyararsa bayan hawan kujerar mukaminsa, lamarin da ya shaida zumunta mai zurfi da muhimmancin dangantakar dake tsakanin kasashen biyu.

  • Wasan Kwallon Kafa Na Mata A Sin: Ba Za Mu Yi Watsi Da Burinmu Na Cimma Nasara Ba – Shui Qingxia

Ya ce an samu nasarori da dama kan hadin gwiwar dake tsakanin kasar Habasha da kasar Sin a fannonin ayyukan more rayuwa, da tattalin arziki ba tare da gurbata muhalli ba, da aikin gona, da gina yankin raya masana’antu da dai sauransu, wadanda ke da babbar ma’ana, wajen sa kaimi ga raya tattalin arzikin kasar Habasha da sanya ta cikin jerin kasashen dake kan gaba a nahiyar Afirka, kana ya yi maraba da karin kamfanonin Sin da su je kasar Habasha don zuba jari da gudanar da ayyuka.

ADVERTISEMENT

A nasa bangare, Qin Gang ya bayyana cewa, a cikin fiye da rabin karni bayan kasashen Sin da Habasha sun kulla dangantakar diplomasiyya a tsakaninsu, ko da yake yanayin duniya ya sauya, kasashen biyu sun ci gaba da goyon bayan juna da yin kokari tare, wanda ya zama misalin hadin gwiwar dake tsakanin kasashe masu tasowa. Ya ce kasar Sin ta nuna goyon baya ga kasar Habasha wajen bin hanyar samun ci gaba da ta dace da yanayinta. Haka kuma, kasar Sin tana son zurfafa hadin gwiwar dake tsakanin kasashen biyu a fannoni da dama, da sa kaimi ga karin kamfanonin kasar Sin su zuba jari a kasar Habasha da shiga aikin sake gina kasar. Qin ya kara da cewa, kasar Sin tana son kasar Habasha ta samar da yanayi mai kyau na yin ciniki da daukar matakai don tabbatar da tsaro da moriyar ma’aikata da hukumomin kasar Sin.

Bugu da kari, minista Qin Gang ya tattauna da manema labarai, tare da mataimakin firaministan Habasha, kana ministan harkokin wajen kasar Demeke Mekonnen, bayan tattaunawarsu a Addis Ababa, babban birnin Habasha.

LABARAI MASU NASABA

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

Da aka nemi jin ra’ayinsa game da yarjejeniyar zaman lafiya ta Habasha da ci gaban da aka samu dangane da shawarar da Sin ta gabatar ta “Makomar Zaman Lafiya da Ci Gaban Kahon Afrika” a Habasha, Qin Gang ya ce, Habasha gida ne na bai daya ga al’ummar kasar, ciki har da mutanen Tigray.

Ya ce kasar Sin ta kasance mai girmama cikakken ikon Habasha da yankunanta, kana tana mara baya ga gwamnatin kasar da al’ummarta, a kokarinsu na cimma zaman lafiya da hadin kai da kuma neman ci gaba.

Da ya yi waiwaye kan ziyarar manzon musamman na Sin a kahon Afrika, Xue Bing ya kai wasu kasashen yankin, Qin Gang ya ce kasar Sin ta goyi bayan babban taron zaman lafiya na kahon Afrika na farko, wanda ya bayar da gudunmawa ga cimma matsaya tsakanin dukkan bangarori da inganta zaman lafiya da ci gaban yankin.

Ya kuma bayyana cewa, Sin ta samar da kashi-kashi na kayayyakin abinci da alluran rigakafi da sauran kayayyakin jin kai ga Habasha, domin taimakawa inganta rayuwar al’ummomin dake yankuna masu fama da rikici.

Dadin dadawa, kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Wang Wenbin, ya ce ziyarar da ministan harkokin wajen kasar Sin Qin Gang ya fara a wasu kasashen Afirka, jim kadan da kama aikinsa, ta shaida yadda kasar Sin ke darajanta zumuncin da ke tsakaninta da kasashen Afirka, wadda kuma ke da nufin kara dinke zumunci tsakanin sassan biyu.

Wang Wenbin ya ce, bana ce shekara ta 33 a jere, da ministan harkokin wajen Sin ke kai ziyarar aiki ta farko a duk shekara kasashen Afirka.

A ranar 30 ga watan Disamban da ya gabata ne aka nada Qin Gang a matsayin ministan harkokin wajen kasar Sin, ya kuma fara ziyarar a ranar Talata, inda ya fara da yada zango a kasar Habasha. (Faeza Mustapha, Saminu Alhassan)

Habasha
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola
Daga Birnin Sin

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026
Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai
Daga Birnin Sin

Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
Daga Birnin Sin

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Next Post
NIS Za Ta Ƙaddamar Da Cibiyar Bayar Da Sabon Ingantaccen Fasfo A Zariya Da Daura

NIS Za Ta Ƙaddamar Da Cibiyar Bayar Da Sabon Ingantaccen Fasfo A Zariya Da Daura

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026
‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

July 15, 2026
Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.