• English
  • Business News
Monday, July 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ganawar Shugabannin Sin Da Australia Ta Share Fagen Kyautata Dangantaka

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Ganawar Shugabannin Sin Da Australia Ta Share Fagen Kyautata Dangantaka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gana da firaministan Australia Anthony Albanese wanda ya yi ziyarar aiki a Sin. Yayin zantawar shugabannin 2 a ranar Litinin a birnin Beijing, Xi ya jaddada bukatar hadin gwiwar sassan biyu, ta yadda za su gina kyakkyawar alaka bisa daidaito, da cimma matsaya, da kawar da sabani, da hadin gwiwar cimma moriya tsakaninsu. 

A nasa tsokacin kuwa, firaminista Albanese ya ce Australia da Sin na da banbanci ta fuskar tsarin siyasa, kuma hakan ba wata matsala ba ce, sai dai bai dace a bari sabanin ya gurgunta yanayin dangantakar sassan biyu ba. Ya ce tattaunawa da hadin gwiwa ne zabin da ya dace Australia da Sin su runguma.

  • Xi Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Kasa Da Kasa Na Wuzhen Kan Intanet
  • Darajar Cinikayyar Kasar Sin A Ketare Ya Karu Da Kaso 0.03% Cikin Watanni 10 Na Bana

Wannan ne dai karon farko da wani firaministan Australia ya ziyarci kasar Sin cikin shekaru 7 da suka gabata. Kaza lika alakar Sin da Australia na cikin muhimman manufofin kasar Sin game da kasashen yamma masu ci gaba. A matsayinta na babbar abokiyar huldar cinikayyar Australia, sauye-sauye, da bude kofa, da zamanantarwa da Sin ke aiwatarwa na ingiza samuwar damammaki masu tarin yawa ga Australia.

To sai dai kuma duk da haka, a zamanin gwamnatocin Australia biyu da suka gabata, kasar ta rungumi manufar nan ta Amurka mai lakabin “Indo-Pacific strategy”, wadda a karkashinta aka hana karbar fasahar 5G ta kamfanin Huawei, kana aka rika takalar kasar Sin ta fakewa da batutuwa kamar na jihar Xinjiang da tekun kudancin Sin, wanda hakan ya kai ga haifar da koma baya ga dangantakar dake tsakanin Sin da Australia, tare da illata moriyar Australia.

A watan Nuwanban shekarar bara ne kuma, a tsibirin Bali na kasar Indonesiya, shugaba Xi ya gana da mista Albanese wanda jim kadan da kama aikin firaministan kasar Australiya, ya kuma share fagen farfadowa, da kuma inganta alakar Sin da kasarsa. Yayin ganawarsu ta wannan karo a birnin Beijing kuma, bangaren Sin ya jaddada bukatar lura matuka, da nuna adawa da manufofin dake yunkurin jefa yankin Asiya da Pacific cikin rudani, kana ya nuna dalilin da ya sa alakar Sin da Australia ta shiga mawuyacin hali a ’yan shekarun baya.

Labarai Masu Nasaba

Zhao Leji Ya Kai Ziyarar Sada Zumunta A Kyrgyzstan

Sin Ta Samu Ci Gaban Aikin Jigilar Kaya A Rabin Farko Na Bana

Alakar Sin da Australia, wadda ta ci karo da koma baya, a yanzu tana farfadowa cikin kuzari. Kaza lika ana fatan Sin da Australia za su rungumi yanayin zamanin da ake ciki, su kyautata fahimtar juna, da amincewar juna ta hanyar zaman jituwa, kana su cimma bunkasuwar bai daya ta hanyar hadin gwiwar cimma moriya tare. (Saminu Alhassan)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaJapanSin
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kwamishinan Cinikayya Da Zuba Jari Na Najeriya Dake Shanghai Ya Yaba Da Manufofin Kasar Sin Na Fadada Bude Kofa Ga Kasashen Waje

Next Post

Manzon Musamman Na Sin Kan Batun Yankin Gabas Ta Tsakiya Zai Halarci Taron Tallafin Jin Kai A Gaza

Related

Zhao Leji Ya Kai Ziyarar Sada Zumunta A Kyrgyzstan
Daga Birnin Sin

Zhao Leji Ya Kai Ziyarar Sada Zumunta A Kyrgyzstan

4 hours ago
Sin Ta Samu Ci Gaban Aikin Jigilar Kaya A Rabin Farko Na Bana
Daga Birnin Sin

Sin Ta Samu Ci Gaban Aikin Jigilar Kaya A Rabin Farko Na Bana

5 hours ago
Kudin Shigar Da Kasuwar Fina-Finai Ta Sin Ta Samu A Lokacin Zafi Na Bana Ya Zarce Yuan Biliyan 5
Daga Birnin Sin

Kudin Shigar Da Kasuwar Fina-Finai Ta Sin Ta Samu A Lokacin Zafi Na Bana Ya Zarce Yuan Biliyan 5

6 hours ago
Shanghai Ya Gabatar Da Shirin Gina Yankin Motoci Masu Tuka Kansu
Daga Birnin Sin

Shanghai Ya Gabatar Da Shirin Gina Yankin Motoci Masu Tuka Kansu

7 hours ago
Sin: Fasahar Rage Asarar Hatsi Ta Yi Amfani
Daga Birnin Sin

Sin: Fasahar Rage Asarar Hatsi Ta Yi Amfani

8 hours ago
Masanin Kimiyyar Na’ura Mai Kwakwalwa Robert Tarjan Ya Jinjinawa Dabarun Sin Na Ingiza Ilimin Kimiyya
Daga Birnin Sin

Masanin Kimiyyar Na’ura Mai Kwakwalwa Robert Tarjan Ya Jinjinawa Dabarun Sin Na Ingiza Ilimin Kimiyya

1 day ago
Next Post
Manzon Musamman Na Sin Kan Batun Yankin Gabas Ta Tsakiya Zai Halarci Taron Tallafin Jin Kai A Gaza

Manzon Musamman Na Sin Kan Batun Yankin Gabas Ta Tsakiya Zai Halarci Taron Tallafin Jin Kai A Gaza

LABARAI MASU NASABA

Mazauna Sokoto Sun Yi Murna Bayan Nasarar Kashe Fitattun ‘Yan Bindiga 3 A Jihar

Mazauna Sokoto Sun Yi Murna Bayan Nasarar Kashe Fitattun ‘Yan Bindiga 3 A Jihar

July 27, 2025
Zhao Leji Ya Kai Ziyarar Sada Zumunta A Kyrgyzstan

Zhao Leji Ya Kai Ziyarar Sada Zumunta A Kyrgyzstan

July 27, 2025
Gwamnan Bauchi Ya Sulhunta Rikicin Manoma Da Makiyaya A Darazo

Gwamnan Bauchi Ya Sulhunta Rikicin Manoma Da Makiyaya A Darazo

July 27, 2025
Sin Ta Samu Ci Gaban Aikin Jigilar Kaya A Rabin Farko Na Bana

Sin Ta Samu Ci Gaban Aikin Jigilar Kaya A Rabin Farko Na Bana

July 27, 2025
Kudin Shigar Da Kasuwar Fina-Finai Ta Sin Ta Samu A Lokacin Zafi Na Bana Ya Zarce Yuan Biliyan 5

Kudin Shigar Da Kasuwar Fina-Finai Ta Sin Ta Samu A Lokacin Zafi Na Bana Ya Zarce Yuan Biliyan 5

July 27, 2025
Shanghai Ya Gabatar Da Shirin Gina Yankin Motoci Masu Tuka Kansu

Shanghai Ya Gabatar Da Shirin Gina Yankin Motoci Masu Tuka Kansu

July 27, 2025
Sin: Fasahar Rage Asarar Hatsi Ta Yi Amfani

Sin: Fasahar Rage Asarar Hatsi Ta Yi Amfani

July 27, 2025
‘Yansanda Sun Cafke Wasu Sojojin Bogi 2 A Legas

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yanbindiga Uku Da Kama AK-47 Guda Goma

July 27, 2025
Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

July 27, 2025
Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

July 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.