• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ganawar Shugabannin Sin Da Australia Ta Share Fagen Kyautata Dangantaka

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Ganawar Shugabannin Sin Da Australia Ta Share Fagen Kyautata Dangantaka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gana da firaministan Australia Anthony Albanese wanda ya yi ziyarar aiki a Sin. Yayin zantawar shugabannin 2 a ranar Litinin a birnin Beijing, Xi ya jaddada bukatar hadin gwiwar sassan biyu, ta yadda za su gina kyakkyawar alaka bisa daidaito, da cimma matsaya, da kawar da sabani, da hadin gwiwar cimma moriya tsakaninsu. 

A nasa tsokacin kuwa, firaminista Albanese ya ce Australia da Sin na da banbanci ta fuskar tsarin siyasa, kuma hakan ba wata matsala ba ce, sai dai bai dace a bari sabanin ya gurgunta yanayin dangantakar sassan biyu ba. Ya ce tattaunawa da hadin gwiwa ne zabin da ya dace Australia da Sin su runguma.

  • Xi Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Kasa Da Kasa Na Wuzhen Kan Intanet
  • Darajar Cinikayyar Kasar Sin A Ketare Ya Karu Da Kaso 0.03% Cikin Watanni 10 Na Bana

Wannan ne dai karon farko da wani firaministan Australia ya ziyarci kasar Sin cikin shekaru 7 da suka gabata. Kaza lika alakar Sin da Australia na cikin muhimman manufofin kasar Sin game da kasashen yamma masu ci gaba. A matsayinta na babbar abokiyar huldar cinikayyar Australia, sauye-sauye, da bude kofa, da zamanantarwa da Sin ke aiwatarwa na ingiza samuwar damammaki masu tarin yawa ga Australia.

To sai dai kuma duk da haka, a zamanin gwamnatocin Australia biyu da suka gabata, kasar ta rungumi manufar nan ta Amurka mai lakabin “Indo-Pacific strategy”, wadda a karkashinta aka hana karbar fasahar 5G ta kamfanin Huawei, kana aka rika takalar kasar Sin ta fakewa da batutuwa kamar na jihar Xinjiang da tekun kudancin Sin, wanda hakan ya kai ga haifar da koma baya ga dangantakar dake tsakanin Sin da Australia, tare da illata moriyar Australia.

A watan Nuwanban shekarar bara ne kuma, a tsibirin Bali na kasar Indonesiya, shugaba Xi ya gana da mista Albanese wanda jim kadan da kama aikin firaministan kasar Australiya, ya kuma share fagen farfadowa, da kuma inganta alakar Sin da kasarsa. Yayin ganawarsu ta wannan karo a birnin Beijing kuma, bangaren Sin ya jaddada bukatar lura matuka, da nuna adawa da manufofin dake yunkurin jefa yankin Asiya da Pacific cikin rudani, kana ya nuna dalilin da ya sa alakar Sin da Australia ta shiga mawuyacin hali a ’yan shekarun baya.

Labarai Masu Nasaba

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Alakar Sin da Australia, wadda ta ci karo da koma baya, a yanzu tana farfadowa cikin kuzari. Kaza lika ana fatan Sin da Australia za su rungumi yanayin zamanin da ake ciki, su kyautata fahimtar juna, da amincewar juna ta hanyar zaman jituwa, kana su cimma bunkasuwar bai daya ta hanyar hadin gwiwar cimma moriya tare. (Saminu Alhassan)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaJapanSin
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kwamishinan Cinikayya Da Zuba Jari Na Najeriya Dake Shanghai Ya Yaba Da Manufofin Kasar Sin Na Fadada Bude Kofa Ga Kasashen Waje

Next Post

Manzon Musamman Na Sin Kan Batun Yankin Gabas Ta Tsakiya Zai Halarci Taron Tallafin Jin Kai A Gaza

Related

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa
Daga Birnin Sin

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

4 hours ago
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

5 hours ago
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

6 hours ago
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci
Daga Birnin Sin

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

7 hours ago
Xi Da Takwaransa Na Bangladesh Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Alakar Kasashensu
Daga Birnin Sin

Xi Da Takwaransa Na Bangladesh Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Alakar Kasashensu

8 hours ago
Fim Na Nezha 2 Na Kasar Sin Ya Kara Samun Lambar Yabo
Daga Birnin Sin

Fim Na Nezha 2 Na Kasar Sin Ya Kara Samun Lambar Yabo

1 day ago
Next Post
Manzon Musamman Na Sin Kan Batun Yankin Gabas Ta Tsakiya Zai Halarci Taron Tallafin Jin Kai A Gaza

Manzon Musamman Na Sin Kan Batun Yankin Gabas Ta Tsakiya Zai Halarci Taron Tallafin Jin Kai A Gaza

LABARAI MASU NASABA

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

October 4, 2025
Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

October 4, 2025
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.