• English
  • Business News
Saturday, October 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

by Rabi'u Ali Indabawa
1 month ago
in Kotu Da Ɗansanda
0
Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wani matashi dan shekara 43 da ake zargin dan Kasar Indiya ne mai suna Sumit Sood, wanda aka kama bisa zargin satar wasu dalibai uku na makarantar Bishop Cotton School da ke gundumar Shimla, da farko ya yi kokarin dora laifin a kan wasu ‘yan kungiyar asiri na Nijeriya, kamar yadda jaridar PUNCH Metro ta ruwaito.

A cewar jaridar The Indian Edpress, ‘yansanda sun ce bayan sace daliban, Sood ya yi kira ta hanyar lambar waya ga iyayensu, yana mai nuna cewa “gungun ‘yan Nijeriya ne” suka tilasta shi ya nemi kudin fansa.

  • Hukumar Kwastam Ta Kama Kayan Maye Na Miliyan 680 A Katsina
  • Jihar Xizang Ta Baiwa Duniya Mamaki Da “Canji Mai Girma” Da Ta Samu a Cikin Shekaru 60 Da Suka Gabata 

An yi zargin cewa ya ba da umarnin a biya kudin fansa a cikin Bitcoin kuma ya gargadi iyayen “ka da su sanar da kowa, musamman jami’an makarantar, idan ba haka ba ‘yan kungiyar za su cutar da yaran da shi.”

Shimla Sufeto na ‘yansanda, Sanjeeb Gandhi, ya shaida wa jaridar The Indian Edpress cewa, “An yi wannan kiran ne ta manhajar TedtMe. Wanda ake zargin ya so a biya kudin fansa a Bitcoin.

“Binciken wayar salular Sood ya nuna cewa ya bincika kuma ya bincuke shafukan intanet sama da dozin uku, tashoshi na labarai na gida, da intanet BCS don duba ko labarin sacewar ya yadu.”

Labarai Masu Nasaba

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi

‘Yansanda Sun Kama Mutum Hudu Da Ake Zargi Da Aikata Muggan Laifuka A Yobe

Gandhi ya kara da cewa lokacin da Sood ya samu labarin da misalin karfe 8 na daren ranar Asabar cewa rahotannin daliban da suka bata sun bayyana, “ya yi shirin dauke su daga kauyensa Kokunala zuwa Chandigarh.

“Sood ya ajiye daliban a gidansa mai hawa uku da ke Kokunala saboda wurin da yake da nisa.” “Babu kowa a gidan lokacin da ya kawo su. Kafin ya aikata laifin, Sood ya sace bindigar mahaifinsa mai lasisi.”

Da yake karin haske game da motsin wanda ake zargin kafin yin garkuwa da shi, SP ya ce, “A daren da ya gabata, ya zauna a gidan kakaninsa da ke Ram Bazar na Shimla.

“Ya kauce wa CCTB ta hanyar daukar hanyar Bemloi-New Shimla kuma ya jira fiye da sa’o’i hudu a cikin motarsa, dauke da farantin karya, wanda ya ajiye kimanin mita 100 daga kofar makarantar. Har ma ya yi fitsari a cikin kwalbar a cikin motar.”

A yayin sake gina wurin da ake aikata laifukan, ‘yansanda sun ce Sood ya gano wurin da ke kusa da Dhalli inda ya rufe idanuwan dalibai uku, inda ya canza lambar motarsa, da kuma hanyoyin da ya bi ya isa gidansa na Kokunala da ke kusa da Kotkhai a ranar 9 ga watan Agusta. An shirya Sood zai gurfana a gaban kotu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Indiya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara

Next Post

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

Related

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi
Kotu Da Ɗansanda

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi

2 hours ago
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutum Hudu Da Ake Zargi Da Aikata Muggan Laifuka A Yobe

3 hours ago
Yaki Da Miyagun Kwayoyi: Kamfanin LEADERSHIP Da NDLEA Sun Kulla Kawance
Kotu Da Ɗansanda

NDLEA Ta Farmaki Masu Safarar Muggan Kwayoyi A Sassan Nijeriya

7 days ago
‘Yansanda Sun Cafke Mutum Hudu Kan Satar Taransifoma A Makaranatar Kebbi
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Cafke Mutum Hudu Kan Satar Taransifoma A Makaranatar Kebbi

7 days ago
Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya
Kotu Da Ɗansanda

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

1 month ago
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Kotu Da Ɗansanda

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

1 month ago
Next Post
NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

LABARAI MASU NASABA

Nijeriya A 65: ACF Da Afenifere Sun Yi Hannun Riga Kan Makomar Nijeriya

Nijeriya A 65: ACF Da Afenifere Sun Yi Hannun Riga Kan Makomar Nijeriya

October 4, 2025
Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi

October 4, 2025
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

‘Yansanda Sun Kama Mutum Hudu Da Ake Zargi Da Aikata Muggan Laifuka A Yobe

October 4, 2025
Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina

Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina

October 3, 2025
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP

Tinubu Zai Ziyarci Jos Domin Halartar Jana’izar Mahaifiyar Shugaban Jam’iyyar APC Na Ƙasa

October 3, 2025
MDD Ta Yi Alƙawarin Tallafa Wa Gidauniyar Malala Mai Rajin Inganta Ilimin ‘Ya’ya Mata

MDD Ta Yi Alƙawarin Tallafa Wa Gidauniyar Malala Mai Rajin Inganta Ilimin ‘Ya’ya Mata

October 3, 2025
Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo

Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo

October 3, 2025
Fim Na Nezha 2 Na Kasar Sin Ya Kara Samun Lambar Yabo

Fim Na Nezha 2 Na Kasar Sin Ya Kara Samun Lambar Yabo

October 3, 2025
ADC Ta Dakatar Da Shugabanta Da Wasu Jiga-jigai 3 A Kebbi

ADC Ta Umarci Dukkan Mambobinta Su Yi Murabus Daga Tsoffin Jam’iyyunsu

October 3, 2025
Xi Ya Taya Grand Duke Guillaume Na Luxembourg Murnar Hawa Karagar Mulki

Xi Ya Taya Grand Duke Guillaume Na Luxembourg Murnar Hawa Karagar Mulki

October 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.