Jama’a da dama ne suka tarbi wani shugaban masu garkuwa da mutane, Hamisu Bala, wanda aka fi sani da Wadume, yayin da ya iso zuwa mahaifarsa da ke Ibbi jihar Taraba, a ranar Lahadi.
Wadume, wanda jami’an rundunar ‘yansandan farin kaya ta ‘Intelligence Response Team’ da ke karkashin kulawar Babban sufeton ‘yansanda suka kama shi a shekarar 2019, an sake shi daga gidan yarin Kuje ne da ke Abuja, a ranar Juma’a, kamar yadda majiya ta bayyana.
- 2023: Manyan Jiragen Ruwa 75,000 Suka Yi Hada-hada A Tashar Lekki
- Karin Kudin Hajji: Gwamna Inuwa Ya Tallafa Wa Maniyyatan Gombe Da Naira 500,000 Kowanne
Majiyar gidan yarin ta shaida wa Daily Trust cewa, Wadume ya kammala hukuncin daurin da aka yanke masa ne a gidan yarin.
Jaridar ta rahoto cewa, dimbin jama’a ne da suka hada da matarsa da sauran jama’a ne suka tarbe shi a kogin Benuwai kan hanyarsa ta zuwa garin Ibbi inda mahaifarsa ta ke.
Wani mazaunin garin Ibbi mai suna Musa Garba ya ce, garin ya tsaya cak yana tsumayin isowar Wadume.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp