• English
  • Business News
Thursday, June 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gasar Nakasassu Ta Duniya: Yadda Nijeriya Ta Kare A Mataki Na 40

by Abba Ibrahim Wada
9 months ago
in Wasanni
0
Gasar Nakasassu Ta Duniya: Yadda Nijeriya Ta Kare A Mataki Na 40
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ranar Lahadin satin da ya gabata ne aka kammala wasannin Nakasassu da ya hada ‘yan wasa daga sassa daban-daban na Duniya kamar yadda aka kammala na masu lafiya a watan da ya gabata a kasar ta Faransa.

Sai dai daman tun farko hukumomin Birnin na Paris sun yi alkawarin gudanar da gasar da za a dade ana tuna ta yayin da suke shirin karbar bakuncin gasar Olympics ta Nakasassu ta wannan shekara ta 2024.

  • Sakon Da Aka Isar Game Da Yanayin Tekun Kudancin Kasar Sin Daga Wasu Taruka Uku
  • Lallai Ƴan Nijeriya Suke Bibiyar Aiyukan Ƴan Majalisu – Shugaban EFCC

Bayan da aka yi gasar wasannin Tokyo a 2021 ba tare da ‘yan kallo ba saboda Annobar Korona, sannan ita kuma gasar Rio ta 2016 ta gamu da matsalollin kudi , Birnin Paris ya kasance cikin matsin lamba kan ya gudanar da gasar da za ta kasance daidai da wadda aka yi a Birnin Landan a 2012 ko ma gasar ta Paris ta zarta ta.

Bikin bude gasar da za a ranar Larabar da ta gabata da karfe 7:00 na yamma agogon

Nijeriya zai kasance ne a ‘Place de la Concorde’, inda za a bayar da kyaututtuka na lambobin Zinare 549 ga ‘yan wasan da suka yi bajinta a washegari.

Labarai Masu Nasaba

Cristiano Ronaldo Na Shirin Tsawaita Kwantiraginsa A Kungiyar Al-Nassr

Manchester United Da Everton Na Zawarcin Wilfred Ndidi

Sannan an kammala gasar inda aka yi bikin rufewa a filin wasa na Stade de France ranr Lahadi 8 ga watan Satumba 2024, sannan an sayar da tikiti kusan miliyn biyu na shiga gasar zuwa yanzu, inda kuma har yanzu akwai 500,000 da ba a saya ba. Bayan irin nasarar da aka samu ta gasar Olympics da aka kammala a Paris hukumomin birnin sun ce wannan somin-tabi ne.

Gasar ta Paris ta samu ‘yan wasa mata da tawagogin ‘yan wasa da ba a taba samu ba a wata gasa ta Nakasassu ta Olympics, sannan kuma za a nuna a tashoshin talabijin a yankuna da dama masu yawan da ba a taba yi ba a baya.

Kuma Faransa ba ta taba karbar bakuncin wasannin Nakasassu na bazara ba, koda yake ta karbi bakuncin wasannin lokacin hunturu na 1992 da aka yi a Albertbille.

Nijeriya ta kammala wasannin wannan shekarar inda ta kammala a mataki na 40 bayan ta lashe lambar yabo guda bakwai ciki kuwa akwai gwal guda biyu da tagulla guda uku da kuma azurfa guda biyu da aka samu a gasar.

‘Yan wasa irin su Onyinyechi Mark da Folashade Oluwafemiayo da Bose Omolayo da Flora Ugwunwa da Esther Nworgu da sau Ogunkunle su ne suka lashewa Nijeriya wadannan kyaututtukan a wannan shekarar da aka kammala.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: GasaNakasassuNijeriya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Wadanne Jarumai Ne Suka Samu Kyautukan Motoci?

Next Post

Gasar Firimiya: Arsenal Na Cikin Tsaka Mai Wuya

Related

Cristiano Ronaldo Na Shirin Tsawaita Kwantiraginsa A Kungiyar Al-Nassr
Wasanni

Cristiano Ronaldo Na Shirin Tsawaita Kwantiraginsa A Kungiyar Al-Nassr

13 hours ago
Manchester United Da Everton Na Zawarcin Wilfred Ndidi
Wasanni

Manchester United Da Everton Na Zawarcin Wilfred Ndidi

1 day ago
Manchester United Za Ta Biya Fam Miliyan 60 Don ÆŠaukar Mbeumo Daga Brentford
Wasanni

Manchester United Za Ta Biya Fam Miliyan 60 Don ÆŠaukar Mbeumo Daga Brentford

2 days ago
Rashford Na Fatan Buga Ƙwallo Tare Da Lamine Yamal A Barcelona
Wasanni

Rashford Na Fatan Buga Ƙwallo Tare Da Lamine Yamal A Barcelona

4 days ago
Bernado Silba Ya Zama Sabon Kyaftin Din Manchester City 
Wasanni

Bernado Silba Ya Zama Sabon Kyaftin Din Manchester City 

4 days ago
Liverpool Za Ta Kece Raini Da Bournemouth, Arsena Za Ta Bakunci Man Utd A Wasan Mako Na Firimiya Ta BaÉ—i
Wasanni

Liverpool Za Ta Kece Raini Da Bournemouth, Arsena Za Ta Bakunci Man Utd A Wasan Mako Na Firimiya Ta BaÉ—i

4 days ago
Next Post
Gasar Firimiya: Arsenal Na Cikin Tsaka Mai Wuya

Gasar Firimiya: Arsenal Na Cikin Tsaka Mai Wuya

LABARAI MASU NASABA

Kawayen amarya

Da ÆŠumi-É—umi: ‘Yan Bindiga Sun Ƙwace Iko Da Jagorancin Ƙaramar Hukuma A Katsina

June 26, 2025
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna

Musayar Wuta Tsakanin Sojoji Da ‘Yan Bindiga Ta Ci Rayuka Da Dama A Jihar Neja

June 26, 2025
Tinubu

Tinubu Zai Rattaba Hannu Kan Kudirorin Sauya Fasalin Haraji 4 A Yau Alhamis 

June 26, 2025
Cristiano Ronaldo Na Shirin Tsawaita Kwantiraginsa A Kungiyar Al-Nassr

Cristiano Ronaldo Na Shirin Tsawaita Kwantiraginsa A Kungiyar Al-Nassr

June 25, 2025
Ni Ne Na Kai Kaina ga Hukumar EFCC, In Ji Tsohon Jami’in NNPC

Ni Ne Na Kai Kaina ga Hukumar EFCC, In Ji Tsohon Jami’in NNPC

June 25, 2025
Shugabannin Sin Da Mozamqiue Sun Mikawa Juna Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafuwar Huldar Diflomasiyya

Shugabannin Sin Da Mozamqiue Sun Mikawa Juna Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafuwar Huldar Diflomasiyya

June 25, 2025
MSS: Neman Sinawa ‘Yan Leken Asiri Da CIA Ta Yi Tamkar Wasan Ban Dariya Ne

MSS: Neman Sinawa ‘Yan Leken Asiri Da CIA Ta Yi Tamkar Wasan Ban Dariya Ne

June 25, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake ÆŠage Ranar Komawa Makarantu

Kano Ta Ayyana Ranar Alhamis Hutu Domin Murnar Sabuwar Shekarar Musulunci

June 25, 2025
Gwamnan Jigawa Ya Kaddamar Da Rumbun Sauki Don Sayar Wa Ma’aikata Kayayyakin Abinci A Farashi Mai Rahusa A Sakkwato

Gwamnan Jigawa Ya Kaddamar Da Rumbun Sauki Don Sayar Wa Ma’aikata Kayayyakin Abinci A Farashi Mai Rahusa A Sakkwato

June 25, 2025
Sin Ta Sha Alwashin Rarraba Fasahohinta Na Ainihi Da Dabarunta Na Kirkire-Kirkire Tare Da Sauran Sassan Kasa Da Kasa

Sin Ta Sha Alwashin Rarraba Fasahohinta Na Ainihi Da Dabarunta Na Kirkire-Kirkire Tare Da Sauran Sassan Kasa Da Kasa

June 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.