ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, November 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gaskiya Ta Bayyana Bayan Da Gwamnatin Amurka Ta Sanar Da Rufe USAID

by Sulaiman
9 months ago
Amurka

Gwamnatin Trump a kwanakin baya ta sanar da rufe hukumar kula da harkokin raya kasa da kasa ta USAID, matakin da ya kasance tamkar ja-in-ja a tsakanin jam’iyyun siyasa na kasar, sai dai hakan ya ta da hankalin wasu kafofin yada labarai da ma kungiyoyin da suka bayyana kansu a matsayin wai “masu zaman kansu”, har ma ya tona mana asirin USAID na fakewa da sunan samar da gudummawa domin amfani da kafafen yada labarai wajen cimma muradunta.

Bethany Allen-Ebrahimian tana aiki da cibiyar nazarin manufofin tsare-tsare na kasar Australia(ASPI), wadda ta sha yada karairayi na shafa wa kasar Sin bakin fenti ta kafofin yada labarai na kasashen yamma. A wata mukalar da ta wallafa a shafin cibiyar ASPI, a bayane ta ce, kungiyoyin NGO da suka samar mata bayanan shafa wa kasar Sin kashin kaza, har da tsarin da kungiyoyin suka kafa na kin jinin kasar Sin, sun dogara ne da kudaden da gwamnatin Amurka ta samar musu. Ta kara da cewa, muddin dai gwamnatin Amurka za ta ci gaba da samar da kudade ga kungiyoyin, to, za ta iya ci gaba da samar da labarai na bata sunan kasar Sin a fadin duniya, a kokarin kare “dimokuradiyya da ‘yanci” da ma “hakkin dan Adam”. Sai dai ba ta yi zaton abin da ya faru bayan da ta wallafa mukalar a shafinta na sada zumunta ba, inda masu bibbiyar shafinta da dama suka gano cewa, ashe su wadannan mutane suna karbar kudade ne don shafa wa kasar Sin kashin kaza, ke nan ya ya za a samu kamshin gaskiyar abubuwan da suka fada? Wasu kuma sun ce, ba za a gano alakar “’yanci da dimokuradiyya da hakkin dan Adam” da wadanda ke karbar kudin gwamnatin Amurka domin tsoma baki cikin harkokin gida na kasar Sin da lalata tsaronta da ikon mulkin kanta ba, a maimakon hakan, matakin ya kara tabbatar da yadda kungiyoyin leken asiri na kasar Amurka ke amfani da USAID wajen hambarar da gwamnatocin wasu kasashe.

  • Yanzu-Yanzu: Ƴan Bindiga Sun Sace Iyali 3 A Filato
  • Kasafin 2025: Kar A Yi Sakaci Macizai Da Birai Su Haɗiye Dala Biliyan 1.07 Da Aka Ware Wa Kiwon Lafiya – Atiku

Kungiyar Reporters Without Borders ma ta damu matuka da matakin gwamnatin Amurka na rufe USAID. Reporters Without Borders kungiya ce ta kasashen yamma wadda ta kan fake da sunan wai “’yancin labarai” da “rahotanni masu zaman kansu” wajen tsoma baki cikin harkokin gidan wasu kasashe. A wani rahoton da ta bayar mai taken “Yadda Trump ya dakatar da samar da kudade ga USAID ya jefa ayyukan labarai na duniya cikin rudani”, ta ce, Yadda Trump ya dakatar da samar da kudade ga USAID na yin tasiri ga ‘yan jarida masu zaman kansu da kungiyoyin da ba na gwamnati ba da ke kasashen Iran da Rasha.” Lallai abin mamaki ne yadda suke karbar kudaden gwamnatin Amurka amma kuma suke bayyana kansu a matsayin masu zaman kansu.

ADVERTISEMENT

Rashin kunya ne yadda Amurka ta dauki irin wadannan munanan matakai na sayen kafafen yada labarai, amma kuma ya kamata mu yi hankali da manufar da take neman cimmawa. Dalilin da ya sa Amurka ke zuba kudade tana sayen ‘yan jarida shi ne, tana bukatar kafofin yada labarai su taimaka mata wajen cimma burinta, ko wajen neman tsoma baki a harkokin wasu ko kuma don wanke kanta daga laifuffukan da ta aikata.

A ‘yan shekarun baya, yayin da kasar Sin ke dada bunkasa, ita Amurka ta yi kuskure har ta dauki kasar Sin a matsayin babbar abokiyar takararta, lamarin da ya sa ta dauki matakan dakile kasar Sin daga dukkan fannoni, ciki har da fannin yada labarai. Musamman ma a yayin da Sin da kasashen Afirka suka yi ta inganta hadin gwiwarsu, har kuma aka aiwatar da shawarar “ziri daya da hanya daya” yadda ya kamata, tattalin arzikin kasashen da abin ya shafa ya yi ta bunkasa, kuma manyan ababen more rayuwa da ma rayuwar al’ummar kasashen ma sun kyautata. Amma Amurka wadda ta dade tana nuna fin karfi a duniya ba ta ji dadin hakan ba, don haka ma muke ta kara karanta rahotanni da ke shafar “sabon salon mulkin mallaka” da “tarkon bashi” da “barazana daga kasar Sin” daga wasu kafofin yada labarai.

LABARAI MASU NASABA

Bikin Baje Koli CIIE, Bikin Zaburar Da Manoman Afirka

CIIE Ya Ba ‘Yan Kasuwar Afirka Damar Habaka Cinikinsu Da Sin 

Sai dai yadda gwamnatin Trump ta sanar da rufe USAID ya ba da damar tona asirinta, kuma tabbas tarihi zai tabbatar da cewa, gaskiya na hannun wadanda ke kokarin samar da ci gaba da kiyaye hadin gwiwar cin moriyar juna da ma wadanda ke kokarin tabbatar da makomar dan Adam ta bai daya.

 

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Bikin Baje Koli CIIE, Bikin Zaburar Da Manoman Afirka
Ra'ayi Riga

Bikin Baje Koli CIIE, Bikin Zaburar Da Manoman Afirka

November 12, 2025
CIIE Ya Ba ‘Yan Kasuwar Afirka Damar Habaka Cinikinsu Da Sin 
Ra'ayi Riga

CIIE Ya Ba ‘Yan Kasuwar Afirka Damar Habaka Cinikinsu Da Sin 

November 11, 2025
Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari
Ra'ayi Riga

Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

November 6, 2025
Next Post
Masana’antar Mutum-mutumi Mai Basira Ta Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Mai Inganci A Shekarar 2024

Masana’antar Mutum-mutumi Mai Basira Ta Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Mai Inganci A Shekarar 2024

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Sin Ba Ta Taba Bukatar Kamfanoni Su Tattara Ko Adana Bayanai Ba Bisa Ka’ida Ba Kuma Ba Za Ta Yi Hakan Ba 

Gwamnatin Sin Ba Ta Taba Bukatar Kamfanoni Su Tattara Ko Adana Bayanai Ba Bisa Ka’ida Ba Kuma Ba Za Ta Yi Hakan Ba 

November 17, 2025
Adadin Motocin Da Sin Ke Fitarwa Waje Ya Karu Da Kashi 15.7 Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana

Adadin Motocin Da Sin Ke Fitarwa Waje Ya Karu Da Kashi 15.7 Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana

November 17, 2025
Farashin Kayan Abinci Na Cigaba Da Sauka A Jihohin Arewa Maso Gabas

Farashin Kayan Abinci Na Cigaba Da Sauka A Jihohin Arewa Maso Gabas

November 17, 2025
An Bude Taron Tattaunawa Kan Wayewar Kai Tsakanin Sin Da Kasashen Larabawa Karo Na 11 A Beijing

An Bude Taron Tattaunawa Kan Wayewar Kai Tsakanin Sin Da Kasashen Larabawa Karo Na 11 A Beijing

November 17, 2025
NBS

Hauhawar Farashin Kayayyaki A Nijeriya Ta Ragu Zuwa Kashi 16.065%

November 17, 2025
Firaministan Sin Ya Isa Rasha Domin Halartar Taron SCO

Firaministan Sin Ya Isa Rasha Domin Halartar Taron SCO

November 17, 2025
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

November 17, 2025
Kudaden Kasafin Kudin Sin Sun Karu Da Kashi 0.8 Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana

Kudaden Kasafin Kudin Sin Sun Karu Da Kashi 0.8 Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana

November 17, 2025
Rashin Tsaro: Atiku Ya Yi Allah-wadai Da Harin Makarantar ‘Yan Mata Ta Kebbi

Rashin Tsaro: Atiku Ya Yi Allah-wadai Da Harin Makarantar ‘Yan Mata Ta Kebbi

November 17, 2025
An Sanya Hannu Kan Yarjejeniyoyin Cinikayya Na Biliyoyin Kudi Yayin Baje Kolin CHTF Na Kasar Sin

An Sanya Hannu Kan Yarjejeniyoyin Cinikayya Na Biliyoyin Kudi Yayin Baje Kolin CHTF Na Kasar Sin

November 17, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.