• English
  • Business News
Saturday, September 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gaskiya Ta Bayyana Bayan Da Gwamnatin Amurka Ta Sanar Da Rufe USAID

by Sulaiman
7 months ago
in Ra'ayi Riga
0
Gaskiya Ta Bayyana Bayan Da Gwamnatin Amurka Ta Sanar Da Rufe USAID
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Trump a kwanakin baya ta sanar da rufe hukumar kula da harkokin raya kasa da kasa ta USAID, matakin da ya kasance tamkar ja-in-ja a tsakanin jam’iyyun siyasa na kasar, sai dai hakan ya ta da hankalin wasu kafofin yada labarai da ma kungiyoyin da suka bayyana kansu a matsayin wai “masu zaman kansu”, har ma ya tona mana asirin USAID na fakewa da sunan samar da gudummawa domin amfani da kafafen yada labarai wajen cimma muradunta.

Bethany Allen-Ebrahimian tana aiki da cibiyar nazarin manufofin tsare-tsare na kasar Australia(ASPI), wadda ta sha yada karairayi na shafa wa kasar Sin bakin fenti ta kafofin yada labarai na kasashen yamma. A wata mukalar da ta wallafa a shafin cibiyar ASPI, a bayane ta ce, kungiyoyin NGO da suka samar mata bayanan shafa wa kasar Sin kashin kaza, har da tsarin da kungiyoyin suka kafa na kin jinin kasar Sin, sun dogara ne da kudaden da gwamnatin Amurka ta samar musu. Ta kara da cewa, muddin dai gwamnatin Amurka za ta ci gaba da samar da kudade ga kungiyoyin, to, za ta iya ci gaba da samar da labarai na bata sunan kasar Sin a fadin duniya, a kokarin kare “dimokuradiyya da ‘yanci” da ma “hakkin dan Adam”. Sai dai ba ta yi zaton abin da ya faru bayan da ta wallafa mukalar a shafinta na sada zumunta ba, inda masu bibbiyar shafinta da dama suka gano cewa, ashe su wadannan mutane suna karbar kudade ne don shafa wa kasar Sin kashin kaza, ke nan ya ya za a samu kamshin gaskiyar abubuwan da suka fada? Wasu kuma sun ce, ba za a gano alakar “’yanci da dimokuradiyya da hakkin dan Adam” da wadanda ke karbar kudin gwamnatin Amurka domin tsoma baki cikin harkokin gida na kasar Sin da lalata tsaronta da ikon mulkin kanta ba, a maimakon hakan, matakin ya kara tabbatar da yadda kungiyoyin leken asiri na kasar Amurka ke amfani da USAID wajen hambarar da gwamnatocin wasu kasashe.

  • Yanzu-Yanzu: Ƴan Bindiga Sun Sace Iyali 3 A Filato
  • Kasafin 2025: Kar A Yi Sakaci Macizai Da Birai Su Haɗiye Dala Biliyan 1.07 Da Aka Ware Wa Kiwon Lafiya – Atiku

Kungiyar Reporters Without Borders ma ta damu matuka da matakin gwamnatin Amurka na rufe USAID. Reporters Without Borders kungiya ce ta kasashen yamma wadda ta kan fake da sunan wai “’yancin labarai” da “rahotanni masu zaman kansu” wajen tsoma baki cikin harkokin gidan wasu kasashe. A wani rahoton da ta bayar mai taken “Yadda Trump ya dakatar da samar da kudade ga USAID ya jefa ayyukan labarai na duniya cikin rudani”, ta ce, Yadda Trump ya dakatar da samar da kudade ga USAID na yin tasiri ga ‘yan jarida masu zaman kansu da kungiyoyin da ba na gwamnati ba da ke kasashen Iran da Rasha.” Lallai abin mamaki ne yadda suke karbar kudaden gwamnatin Amurka amma kuma suke bayyana kansu a matsayin masu zaman kansu.

Rashin kunya ne yadda Amurka ta dauki irin wadannan munanan matakai na sayen kafafen yada labarai, amma kuma ya kamata mu yi hankali da manufar da take neman cimmawa. Dalilin da ya sa Amurka ke zuba kudade tana sayen ‘yan jarida shi ne, tana bukatar kafofin yada labarai su taimaka mata wajen cimma burinta, ko wajen neman tsoma baki a harkokin wasu ko kuma don wanke kanta daga laifuffukan da ta aikata.

A ‘yan shekarun baya, yayin da kasar Sin ke dada bunkasa, ita Amurka ta yi kuskure har ta dauki kasar Sin a matsayin babbar abokiyar takararta, lamarin da ya sa ta dauki matakan dakile kasar Sin daga dukkan fannoni, ciki har da fannin yada labarai. Musamman ma a yayin da Sin da kasashen Afirka suka yi ta inganta hadin gwiwarsu, har kuma aka aiwatar da shawarar “ziri daya da hanya daya” yadda ya kamata, tattalin arzikin kasashen da abin ya shafa ya yi ta bunkasa, kuma manyan ababen more rayuwa da ma rayuwar al’ummar kasashen ma sun kyautata. Amma Amurka wadda ta dade tana nuna fin karfi a duniya ba ta ji dadin hakan ba, don haka ma muke ta kara karanta rahotanni da ke shafar “sabon salon mulkin mallaka” da “tarkon bashi” da “barazana daga kasar Sin” daga wasu kafofin yada labarai.

Labarai Masu Nasaba

Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe

Kowa Ya Ci Zomo Ya Ci Gudu: Shekaru 80 Da Nasarar Sinawa A Kan Zalunci Da Danniyar Japanawa

Sai dai yadda gwamnatin Trump ta sanar da rufe USAID ya ba da damar tona asirinta, kuma tabbas tarihi zai tabbatar da cewa, gaskiya na hannun wadanda ke kokarin samar da ci gaba da kiyaye hadin gwiwar cin moriyar juna da ma wadanda ke kokarin tabbatar da makomar dan Adam ta bai daya.

 

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Yanzu-Yanzu: Ƴan Bindiga Sun Sace Iyali 3 A Filato

Next Post

Masana’antar Mutum-mutumi Mai Basira Ta Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Mai Inganci A Shekarar 2024

Related

Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe

22 hours ago
Kowa Ya Ci Zomo Ya Ci Gudu: Shekaru 80 Da Nasarar Sinawa A Kan Zalunci Da Danniyar Japanawa
Ra'ayi Riga

Kowa Ya Ci Zomo Ya Ci Gudu: Shekaru 80 Da Nasarar Sinawa A Kan Zalunci Da Danniyar Japanawa

1 day ago
Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Ba Da Gudummawarta Wajen Kiyaye Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya 
Ra'ayi Riga

Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Ba Da Gudummawarta Wajen Kiyaye Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya 

2 days ago
Sin: Bin Tafarki Na Gaskiya
Ra'ayi Riga

Sin: Bin Tafarki Na Gaskiya

3 days ago
Kyakkyawan Fata Kan Nasarar Yaki Da Akidar Mulkin Danniya A Duniya
Ra'ayi Riga

Kyakkyawan Fata Kan Nasarar Yaki Da Akidar Mulkin Danniya A Duniya

4 days ago
Shawarar GGI: Faduwa Ta Zo Daidai Da Zama
Ra'ayi Riga

Shawarar GGI: Faduwa Ta Zo Daidai Da Zama

4 days ago
Next Post
Masana’antar Mutum-mutumi Mai Basira Ta Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Mai Inganci A Shekarar 2024

Masana’antar Mutum-mutumi Mai Basira Ta Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Mai Inganci A Shekarar 2024

LABARAI MASU NASABA

Mutanen Gari Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Wasu A Sakkwato

Mutanen Gari Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Wasu A Sakkwato

September 6, 2025
Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa

Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa

September 6, 2025
Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON

Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON

September 6, 2025
Gwamnatin Kogi Ta Jaddada Aniyar Magance Ambaliya Da Zaizayar Ƙasa

Gwamnatin Kogi Ta Jaddada Aniyar Magance Ambaliya Da Zaizayar Ƙasa

September 6, 2025
Zulum Ya Ba Da Tallafin ₦300,000 Ga Iyaye, Da Ciyar Da Ɗalibai 90 Kyauta A Borno

Zulum Ya Ba Da Tallafin ₦300,000 Ga Iyaye, Da Ciyar Da Ɗalibai 90 Kyauta A Borno

September 6, 2025
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho

Kungiyoyi Da Abokan Arziki Na Ci Gaba Da Taya Dantsoho Murna

September 6, 2025
Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

September 6, 2025
Tsohon Mataimakin Gwamnan Gombe Da Wasu jigogin PDP Sun Koma APC

Tsohon Mataimakin Gwamnan Gombe Da Wasu jigogin PDP Sun Koma APC

September 6, 2025

Ilimi Shi Ne Matakin Nasarar Rayuwar Duniya Da Lahira – Yerima Shettima

September 6, 2025
NUPENG Za Ta Fara Yajin Aiki, Dangote Na Shirin Shiga Harkar Sufurin Mai

NUPENG Za Ta Fara Yajin Aiki, Dangote Na Shirin Shiga Harkar Sufurin Mai

September 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.