ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gaskiya Ta Bayyana Bayan Da Gwamnatin Amurka Ta Sanar Da Rufe USAID

by Sulaiman
1 year ago
Amurka

Gwamnatin Trump a kwanakin baya ta sanar da rufe hukumar kula da harkokin raya kasa da kasa ta USAID, matakin da ya kasance tamkar ja-in-ja a tsakanin jam’iyyun siyasa na kasar, sai dai hakan ya ta da hankalin wasu kafofin yada labarai da ma kungiyoyin da suka bayyana kansu a matsayin wai “masu zaman kansu”, har ma ya tona mana asirin USAID na fakewa da sunan samar da gudummawa domin amfani da kafafen yada labarai wajen cimma muradunta.

Bethany Allen-Ebrahimian tana aiki da cibiyar nazarin manufofin tsare-tsare na kasar Australia(ASPI), wadda ta sha yada karairayi na shafa wa kasar Sin bakin fenti ta kafofin yada labarai na kasashen yamma. A wata mukalar da ta wallafa a shafin cibiyar ASPI, a bayane ta ce, kungiyoyin NGO da suka samar mata bayanan shafa wa kasar Sin kashin kaza, har da tsarin da kungiyoyin suka kafa na kin jinin kasar Sin, sun dogara ne da kudaden da gwamnatin Amurka ta samar musu. Ta kara da cewa, muddin dai gwamnatin Amurka za ta ci gaba da samar da kudade ga kungiyoyin, to, za ta iya ci gaba da samar da labarai na bata sunan kasar Sin a fadin duniya, a kokarin kare “dimokuradiyya da ‘yanci” da ma “hakkin dan Adam”. Sai dai ba ta yi zaton abin da ya faru bayan da ta wallafa mukalar a shafinta na sada zumunta ba, inda masu bibbiyar shafinta da dama suka gano cewa, ashe su wadannan mutane suna karbar kudade ne don shafa wa kasar Sin kashin kaza, ke nan ya ya za a samu kamshin gaskiyar abubuwan da suka fada? Wasu kuma sun ce, ba za a gano alakar “’yanci da dimokuradiyya da hakkin dan Adam” da wadanda ke karbar kudin gwamnatin Amurka domin tsoma baki cikin harkokin gida na kasar Sin da lalata tsaronta da ikon mulkin kanta ba, a maimakon hakan, matakin ya kara tabbatar da yadda kungiyoyin leken asiri na kasar Amurka ke amfani da USAID wajen hambarar da gwamnatocin wasu kasashe.

  • Yanzu-Yanzu: Ƴan Bindiga Sun Sace Iyali 3 A Filato
  • Kasafin 2025: Kar A Yi Sakaci Macizai Da Birai Su Haɗiye Dala Biliyan 1.07 Da Aka Ware Wa Kiwon Lafiya – Atiku

Kungiyar Reporters Without Borders ma ta damu matuka da matakin gwamnatin Amurka na rufe USAID. Reporters Without Borders kungiya ce ta kasashen yamma wadda ta kan fake da sunan wai “’yancin labarai” da “rahotanni masu zaman kansu” wajen tsoma baki cikin harkokin gidan wasu kasashe. A wani rahoton da ta bayar mai taken “Yadda Trump ya dakatar da samar da kudade ga USAID ya jefa ayyukan labarai na duniya cikin rudani”, ta ce, Yadda Trump ya dakatar da samar da kudade ga USAID na yin tasiri ga ‘yan jarida masu zaman kansu da kungiyoyin da ba na gwamnati ba da ke kasashen Iran da Rasha.” Lallai abin mamaki ne yadda suke karbar kudaden gwamnatin Amurka amma kuma suke bayyana kansu a matsayin masu zaman kansu.

ADVERTISEMENT

Rashin kunya ne yadda Amurka ta dauki irin wadannan munanan matakai na sayen kafafen yada labarai, amma kuma ya kamata mu yi hankali da manufar da take neman cimmawa. Dalilin da ya sa Amurka ke zuba kudade tana sayen ‘yan jarida shi ne, tana bukatar kafofin yada labarai su taimaka mata wajen cimma burinta, ko wajen neman tsoma baki a harkokin wasu ko kuma don wanke kanta daga laifuffukan da ta aikata.

A ‘yan shekarun baya, yayin da kasar Sin ke dada bunkasa, ita Amurka ta yi kuskure har ta dauki kasar Sin a matsayin babbar abokiyar takararta, lamarin da ya sa ta dauki matakan dakile kasar Sin daga dukkan fannoni, ciki har da fannin yada labarai. Musamman ma a yayin da Sin da kasashen Afirka suka yi ta inganta hadin gwiwarsu, har kuma aka aiwatar da shawarar “ziri daya da hanya daya” yadda ya kamata, tattalin arzikin kasashen da abin ya shafa ya yi ta bunkasa, kuma manyan ababen more rayuwa da ma rayuwar al’ummar kasashen ma sun kyautata. Amma Amurka wadda ta dade tana nuna fin karfi a duniya ba ta ji dadin hakan ba, don haka ma muke ta kara karanta rahotanni da ke shafar “sabon salon mulkin mallaka” da “tarkon bashi” da “barazana daga kasar Sin” daga wasu kafofin yada labarai.

LABARAI MASU NASABA

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

Sai dai yadda gwamnatin Trump ta sanar da rufe USAID ya ba da damar tona asirinta, kuma tabbas tarihi zai tabbatar da cewa, gaskiya na hannun wadanda ke kokarin samar da ci gaba da kiyaye hadin gwiwar cin moriyar juna da ma wadanda ke kokarin tabbatar da makomar dan Adam ta bai daya.

 

 

Amurka
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta
  • Sulaiman
    Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
  • Sulaiman
    Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

MASU ALAKA

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka
Ra'ayi Riga

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

July 10, 2026
Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?

July 9, 2026
Next Post
Masana’antar Mutum-mutumi Mai Basira Ta Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Mai Inganci A Shekarar 2024

Masana’antar Mutum-mutumi Mai Basira Ta Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Mai Inganci A Shekarar 2024

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.