• English
  • Business News
Saturday, November 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gazawar Gwamnati Ta Tsananta Fatara Da Rashin Tsaro A Nijeriya –Atiku

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Gwamnati

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya bayyana cewa an samu tsananin fatara da yunwa da kuma rashin tsaro a Nijeriya a halin yanzu sakamakon gazawar gwamnati na kasa sauke nauyin da tsarin mulki ya dora mata na kare rayukan mutane da dukiyoyin al’ummar Nijeriya.  

Dan takarar jam’iyyar PDP a zaben da ya gabata ya bayyana hakan ne a shafinsa na sada zumunta sakamakon kashe-kashen ‘yan bindiga da aka samu a Abuja tsakanin ranakun Asabar da Lahadi.

  • NIS Shiyyar Arewa Maso Gabas Ta Kaddamar Da “Operation Tsaron Iyaka”
  • ‘Yansanda Sun Cafke Wasu Mutane Biyu Da Ake Zargi Da Satar Keke-napep A Kano

A cewar Atikun, muddin gwamnati ta gaza kare rayukan mutane da dukiyoyinsu, to lallai za a ci gaba da samun tsananin rashin tsaro a cikin kasar nan.

Ya ce, “Yadda ake ci gaba da samun tashin hankali a kasar nan yana mutukar damuna, musamman ma yadda ‘yan bindiga da masu garkuwa da mutane suke cin karensu babu babbaka.

“A kulluma ana kashe mana matasa da mutanen da ba su ji ba su gani ba. Ko a ranar Asabar ma sai da muka rasa Nabeeha wacce aka yi garkuwa da ita. Haka kuma a ranar Lahadi mun rasa mutane da dama ci har da dalibi mai suna Folorunsho Ariyo, dan shekara 13.

LABARAI MASU NASABA

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara

“Folorunsho yana daya daga cikin mutanen da aka yi garkuwa da su a rukunin gidaje na Sagwari da ke Dutse a karamar hukumar Bwari na Abuja a ranar 7 ga watan Janairun 2024.

“Tsananin talauci da yunwa yana kara karuwa ne a daidai lokacin da masu garkuwa da mutane ke haddasa rashin tsaro a Nijeriya, musamman ma a Abuja, Babbar Birnin Tarayya.

“A duk lokacin da gwamnati ta gaza sauke hakkin da tsarin mulki ya dora mata na tsare rayukan mutane da kuma dokiyoyinsu, za a samu ci gaba da ayyukan masu garkuwa da kuma sauran manyan laifuka a gidaje da otal-otel a garuruwa. Wannan babban abun takaici ne a kasar nan.”

Atiku ya kara da cewa wajibi ne ga hukumomi su dauki matakan da suka dace wajen shawo kan matsalar tsaro cikin gaggawa domin sanya aminci a zukatan ‘yan Nijeriya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta
Tambarin Dimokuradiyya

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

October 17, 2025
peter
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara

October 17, 2025
peter
Tambarin Dimokuradiyya

Peter Obi Ya Bukaci INEC Ta Tabbatar Da Shaidar Karatun Dan Takara Kafin Shiga Zabe

October 10, 2025
Next Post
Mahalartan WEF: Sin Muhimmiyar Injin Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa

Mahalartan WEF: Sin Muhimmiyar Injin Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa

LABARAI MASU NASABA

Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

Babban Burina Zama Fitacciyar Jaruma A Duniya —Aisha Umar

November 1, 2025
Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik

Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik

November 1, 2025
Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami

Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami

November 1, 2025
Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 20, Sun Ceto Mutane 17 Da Aka Yi Garkuwa Da Su

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 20, Sun Ceto Mutane 17 Da Aka Yi Garkuwa Da Su

November 1, 2025
Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025?

Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025?

November 1, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Martani Kan Iƙirarin Trump Na Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Martani Kan Iƙirarin Trump Na Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci

November 1, 2025
Shugabar Tanzania Samia Suluhu Ta Lashe Zaɓe, Duk Da Rikicin Da Ya Mamaye Ƙasar

Shugabar Tanzania Samia Suluhu Ta Lashe Zaɓe, Duk Da Rikicin Da Ya Mamaye Ƙasar

November 1, 2025
An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3

An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3

November 1, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

Yadda Gwamnatin Tarayya Ta Dakile Yaɗuwar Ɓarkewar Cutar Dabbobi A Jihar Jigawa

November 1, 2025
Jerin Gwarazan Taurarinmu

Jerin Gwarazan Taurarinmu

November 1, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.