ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, November 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gina Al’ummar Sin Da Afrika Mai Makoma Ta Bai Daya, Zai Kai Afrika Ga Samun Tsaro Da Wadata Tamkar Kasar Sin

by CMG Hausa
3 years ago
Kasar Sin

Shugaban kasar Sin ya jaddada muhimmancin hadin gwiwar tsaro da zaman lafiya tsakanin Sin da Afrika, tare da gabatar da shawarar gina al’ummar Sin da Afrika mai makoma ta bai daya a sabon zamani, domin cimma tsaro na bai daya. Shugaban ya bayyana haka ne yayin taro karo na biyu na ministocin kasashen Sin da Afrika kan dangantakar tsaro da zaman lafiya. 

Amini na kwarai shi ke kasancewa da amininsa a ko wanne hali. Matsalar tsaro batu ne da ke ciwa kasashen Afrika tuwo a kwarya, la’akari da mummunan tasirinta ga zaman lafiya da ci gaba. Babu wata kasa da za ta samu ci gaban da take muradi, muddun ta na fama da matsalar tsaro. Don haka a matsayinta na Aminiya ga kasashen Afrika, kuma babbar kasar da ta san ya kamata, Sin na kokarin hada gwiwa da su domin magance matsalar.

  • Kasar Sin Ta Harba Muhimmin Bangare Na Dakin Bincike Na Farko Na Tashar Sararin Samaniyarta

Kasar Sin ce kasa mafi yawan jama’a a duniya, amma kuma, tana cikin kasashe kalilan dake more zaman lafiya da tsaro a duniya. Yadda kasar Sin ta ke kokarin karfafa hadin gwiwar tsaro da zaman lafiya da kasashen Afrika, ya nuna cewa ta damu da yanayin da suke ciki, kuma tana muradin taimaka musu.

ADVERTISEMENT

Har ila yau, kasashen Afrika da Sin na da kamanceceniya ta fuskar yawan al’umma, kuma kasashe masu tasowa, wannan ya samar wa kasashen Afrika wata dama mai sauki na koyi tare da aiwatar da dabarun Sin ba tare da samun matsala ba.

Taimakon kasar Sin daya ne daga cikin kyawawan manufofinta da suka saba da na kasashen yamma, wadanda suke ingiza rikici da yin katsalandan cikin harkokin gidan kasashe, har ma da rura wutar rikici da uwa uba kitsa juyin mulki.

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Bukaci Japan Ta Daina Yi Wa Masu Fafutukar “‘Yancin Kan Taiwan” Ingiza Mai Kantu Ruwa

Peng Liyuan Da Sarauniya Letizia Ta Spain Sun Ziyarci Cibiyar Kula Da Nakasassu A Beijing

Ko da yake, wanda ya gaza tabbatar da tsaro da zaman lafiya da kare al’ummarsa, ina zai samu gogewar bayar da shawara ko kuma zama abun koyi?
Duk wanda yake bibiyar kasar Sin, ko yake zaune a kasar, dole ne ya jinjinawa irin kwanciyar hankalin dake akwai.

Alkaluman kididdiga sun shaida cewa, yadda al’umma suke jin dadin yanayin tsaro a kasar Sin, ya karu zuwa kaso 98.62 a shekarar 2021, daga kaso 87.55 da ya kasance a shekarar 2012.

A ganina, hadin gwiwa a fannin tsaro da kasar Sin, abu ne da ya kamata gwamnatocin Afrika su dauka da muhimmanci idan suna son shawo kan matsalolin da ke addabarsu.

Shawarar gina al’ummar Sin da Afrika mai makoma ta bai daya da shugaba Xi Jinping ya gabatar, ba makawa kyakkyawar dabara ce da zata yi gagarumin tasiri a Afrika.

Wannan na nufin samun tsaro kamar kasar Sin har ma da ci gaba da kwanciyar hankali da wadata tamkar kasar Sin.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sin Ta Bukaci Japan Ta Daina Yi Wa Masu Fafutukar “‘Yancin Kan Taiwan” Ingiza Mai Kantu Ruwa
Daga Birnin Sin

Sin Ta Bukaci Japan Ta Daina Yi Wa Masu Fafutukar “‘Yancin Kan Taiwan” Ingiza Mai Kantu Ruwa

November 12, 2025
Peng Liyuan Da Sarauniya Letizia Ta Spain Sun Ziyarci Cibiyar Kula Da Nakasassu A Beijing
Daga Birnin Sin

Peng Liyuan Da Sarauniya Letizia Ta Spain Sun Ziyarci Cibiyar Kula Da Nakasassu A Beijing

November 12, 2025
Madalla Da Sabon Binciken Jami’ar Nankai Ta Kasar Sin Kan Mata Marasa Haihuwa
Daga Birnin Sin

Madalla Da Sabon Binciken Jami’ar Nankai Ta Kasar Sin Kan Mata Marasa Haihuwa

November 12, 2025
Next Post
Gwamnatin Kaduna Ta Ba Da Hutun Kwana 3 Don Jama’a Su Yi Rijistar Katin Zabe

Gwamnatin Kaduna Ta Ba Da Hutun Kwana 3 Don Jama'a Su Yi Rijistar Katin Zabe

LABARAI MASU NASABA

Zaɓen 2027: Jam’iyyar ADC ta Ƙaddamar Da Kwamitin Sake Fasalinta A Kaduna

Zaɓen 2027: Jam’iyyar ADC ta Ƙaddamar Da Kwamitin Sake Fasalinta A Kaduna

November 12, 2025
Sin Ta Bukaci Japan Ta Daina Yi Wa Masu Fafutukar “‘Yancin Kan Taiwan” Ingiza Mai Kantu Ruwa

Sin Ta Bukaci Japan Ta Daina Yi Wa Masu Fafutukar “‘Yancin Kan Taiwan” Ingiza Mai Kantu Ruwa

November 12, 2025
Gwamnati Ta Janye Buƙatar Amfani Da Harshen Gida Wurin Koyarwa A Makarantu 

Gwamnati Ta Janye Buƙatar Amfani Da Harshen Gida Wurin Koyarwa A Makarantu 

November 12, 2025
Peng Liyuan Da Sarauniya Letizia Ta Spain Sun Ziyarci Cibiyar Kula Da Nakasassu A Beijing

Peng Liyuan Da Sarauniya Letizia Ta Spain Sun Ziyarci Cibiyar Kula Da Nakasassu A Beijing

November 12, 2025
Madalla Da Sabon Binciken Jami’ar Nankai Ta Kasar Sin Kan Mata Marasa Haihuwa

Madalla Da Sabon Binciken Jami’ar Nankai Ta Kasar Sin Kan Mata Marasa Haihuwa

November 12, 2025
'yansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutane 4 Kan Zargin Fashi Da Makami A Bauchi

November 12, 2025
Ana Ci Gaba Da Raya Kasar Sin Daga Matakin Kasa Mai Sauri Zuwa Kasa Mai Inganci

Ana Ci Gaba Da Raya Kasar Sin Daga Matakin Kasa Mai Sauri Zuwa Kasa Mai Inganci

November 12, 2025
Sin Ta Mayar Da Martani Game Da Matakin Amurka Na Dakatar Da Ka’idar Fadada Jerin Wadanda Kasar Ta Takaita Fitar Wa Kayayyaki

Sin Ta Mayar Da Martani Game Da Matakin Amurka Na Dakatar Da Ka’idar Fadada Jerin Wadanda Kasar Ta Takaita Fitar Wa Kayayyaki

November 12, 2025
Kashi 74% Na Marasa Lafiya Sun Gamsu Da Ayyukan Kiwon Lafiya Na Nijeriya — Minista

Kashi 74% Na Marasa Lafiya Sun Gamsu Da Ayyukan Kiwon Lafiya Na Nijeriya — Minista

November 12, 2025
Majalisar Kogi Ta Dakatar Da Shugaban Ƙaramar Hukuma Bisa Zargin Rashin Ɗa’a

Majalisar Jihar Kogi Ta Dakatar Da Shugaban Ƙaramar Hukuma Kan Laifin Rashin Ɗa’a

November 12, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.