ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gina Al’ummar Sin Da Afrika Mai Makoma Ta Bai Daya, Zai Kai Afrika Ga Samun Tsaro Da Wadata Tamkar Kasar Sin

by CMG Hausa
4 years ago
Kasar Sin

Shugaban kasar Sin ya jaddada muhimmancin hadin gwiwar tsaro da zaman lafiya tsakanin Sin da Afrika, tare da gabatar da shawarar gina al’ummar Sin da Afrika mai makoma ta bai daya a sabon zamani, domin cimma tsaro na bai daya. Shugaban ya bayyana haka ne yayin taro karo na biyu na ministocin kasashen Sin da Afrika kan dangantakar tsaro da zaman lafiya. 

Amini na kwarai shi ke kasancewa da amininsa a ko wanne hali. Matsalar tsaro batu ne da ke ciwa kasashen Afrika tuwo a kwarya, la’akari da mummunan tasirinta ga zaman lafiya da ci gaba. Babu wata kasa da za ta samu ci gaban da take muradi, muddun ta na fama da matsalar tsaro. Don haka a matsayinta na Aminiya ga kasashen Afrika, kuma babbar kasar da ta san ya kamata, Sin na kokarin hada gwiwa da su domin magance matsalar.

  • Kasar Sin Ta Harba Muhimmin Bangare Na Dakin Bincike Na Farko Na Tashar Sararin Samaniyarta

Kasar Sin ce kasa mafi yawan jama’a a duniya, amma kuma, tana cikin kasashe kalilan dake more zaman lafiya da tsaro a duniya. Yadda kasar Sin ta ke kokarin karfafa hadin gwiwar tsaro da zaman lafiya da kasashen Afrika, ya nuna cewa ta damu da yanayin da suke ciki, kuma tana muradin taimaka musu.

ADVERTISEMENT

Har ila yau, kasashen Afrika da Sin na da kamanceceniya ta fuskar yawan al’umma, kuma kasashe masu tasowa, wannan ya samar wa kasashen Afrika wata dama mai sauki na koyi tare da aiwatar da dabarun Sin ba tare da samun matsala ba.

Taimakon kasar Sin daya ne daga cikin kyawawan manufofinta da suka saba da na kasashen yamma, wadanda suke ingiza rikici da yin katsalandan cikin harkokin gidan kasashe, har ma da rura wutar rikici da uwa uba kitsa juyin mulki.

LABARAI MASU NASABA

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Ko da yake, wanda ya gaza tabbatar da tsaro da zaman lafiya da kare al’ummarsa, ina zai samu gogewar bayar da shawara ko kuma zama abun koyi?
Duk wanda yake bibiyar kasar Sin, ko yake zaune a kasar, dole ne ya jinjinawa irin kwanciyar hankalin dake akwai.

Alkaluman kididdiga sun shaida cewa, yadda al’umma suke jin dadin yanayin tsaro a kasar Sin, ya karu zuwa kaso 98.62 a shekarar 2021, daga kaso 87.55 da ya kasance a shekarar 2012.

A ganina, hadin gwiwa a fannin tsaro da kasar Sin, abu ne da ya kamata gwamnatocin Afrika su dauka da muhimmanci idan suna son shawo kan matsalolin da ke addabarsu.

Shawarar gina al’ummar Sin da Afrika mai makoma ta bai daya da shugaba Xi Jinping ya gabatar, ba makawa kyakkyawar dabara ce da zata yi gagarumin tasiri a Afrika.

Wannan na nufin samun tsaro kamar kasar Sin har ma da ci gaba da kwanciyar hankali da wadata tamkar kasar Sin.

Kasar Sin
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya
Daga Birnin Sin

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026
Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar
Daga Birnin Sin

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

June 12, 2026
Next Post
Gwamnatin Kaduna Ta Ba Da Hutun Kwana 3 Don Jama’a Su Yi Rijistar Katin Zabe

Gwamnatin Kaduna Ta Ba Da Hutun Kwana 3 Don Jama'a Su Yi Rijistar Katin Zabe

LABARAI MASU NASABA

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

June 13, 2026
Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.