Wuta ta tashi a safiyar ranar Sallah babba a mashahuriyar kasuwar wayoyi da ake kira Farm Centre a Kano, inda ta ƙone shaguna da dama.
Wani mutum ne ya fara bayyana tashin wutar a kafafen sada zumunta, inda ya wallafa bidiyo wanda ya nuna hayaƙi mai yawa yana tashi daga wani sashe na kasuwar.
- Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4
- Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet
Har yanzu ba a san musabbabin tashin wutar ba, sai dai ganau sun ce shagunan da wutar ta fi shafa su ne na masu sayar da wayoyin salula.
Zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, Hukumar kashe gobara ta Jihar Kano ba ta fitar da wata sanarwa ba dangane da dalilin gobarar ko kuma adadin ɓarnar da aka yi.
Wani ɗan kasuwa a kasuwar, Muhammad Daula, ya shaida wa LEADERSHIP cewa mafi yawan masu shaguna ba su je kasuwa ba saboda bukukuwan Sallah, kuma sun ji labarin gobarar ne a kafafen sada zumunta.
“Yawancinmu ba mu je kasuwa ba yau saboda Sallah. Bidiyon da aka ɗora ne ya sa muka samu labarin wutar. Abin takaici, wasu shaguna da ke kusa da nawa sun ƙone,” in ji shi.
Ƙoƙarin da wakilinmu ya na tuntuɓar mai magana da yawun hukumar kashe gobara ta Jihar Kano, Saminu Yusuf, bai yi nasara ba domin wayarsa ba ta shiga.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp