Wata gobara da ta tashi a sansanin ‘yan gudun hijira na Munna Albadawi, a Ƙaramar Hukumar Jere a Jihar Borno, ta yi É“arna mai yawa tare da kashe wani yaro É—an shekara bakwai.
Shugaban sansanin, Malam Babangida Mahmud, ya ce gobarar ta fara ne da misalin Æ™arfe 3 na Asuba a ranar Alhamis, inda ta laÆ™ume tantuna da É—akunan kwanan ‘yan gudun hijira da kuma kayayyakinsu.
- Nijeriya Da Brazil Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Kasuwanci Ta Dala Biliyan 1
- Gaggan Masu Garkuwa Da Mutane 10 Da Kayan Aikinsu Sun Shiga Hannu A Kano
Har yanzu ba a tantance adadin É“arnar da aka yi ba.
Jami’an hukumar kashe gobara da haɗin gwiwar hukumomin tsaro sun yi ƙoƙari wajen shawo kan wutar bayan ta yi mummunan ta’adi.
Yaron da ya rasu a gobarar mai suna Abubakar Gargar, an gano gawarsa kuma an miƙa wa iyalansa don jana’iza bisa koyarwar addinin Musulunci.
A halin yanzu, Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Jihar Borno (SEMA) da Hukumar Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA) tare da wasu ƙungiyoyin jin-ƙai sun tura wakilansu don duba girman ɓarnar da gobarar ta haifar.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp