• English
  • Business News
Wednesday, July 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijeriya Da Brazil Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Kasuwanci Ta Dala Biliyan 1

by Khalid Idris Doya and Sulaiman
4 months ago
in Labarai
0
Nijeriya Da Brazil Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Kasuwanci Ta Dala Biliyan 1
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Nijeriya da kasar Brazil sun sanya hannu kan yarjejeniyar fahimtar juna a bangaren kasuwanci ta ‘Green Imperative Project’ (GIP) na dala biliyan 1.1 domin bunkasa harkokin noma da zuba hannun jari ga kamfanoni masu zaman kansu a Nijeriya.
Wannnan na cikin matakan kariya kan wadata kasa da abinci.

Shirin GIP, shiri ne kan aikin noma mafi girma a Afirka wanda ke ba da fifiko ga ci gaban noma mai dorewa, yana da nufin habaka yanayin tsari don samar da abinci a Nijeriya cikin inganci.

  • Hauhawar Farashi A Nijeriya Ta Ragu Zuwa 23.18 Cikin 100 A Fabrairu — NBS
  • Azumi Ya Dara Wa Sauran Ibadu

A shekarar 2018 ne aka fara rattaba hannu kan yarjejeniyar dala biliyan 1.1 na GIP 1, yayin da kashi na 2 na shirin dala biliyan 4.3 da kuma JBS na dala biliyan 2.5 aka sanya hannu a Brazil a ziyarar da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya kai kasar a bara.

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya misalta sanya hannu kan shirin farko na kasuwancin GIP 1 a wani mataki na gwamnatin Tinubu na wadata kasa da abinci.
Da yake jawabi yayin rattaba hannu a rukunin shirin kasuwanci GIP 1 a fadar shugaban kasa da ke Abuja, Shettima ya ce shirin GIP zai bude wasu damarmakin masu tarin yawa da za su kai ga bude kofofin ci gaban tattalin arzikin kasa da inganta kwarin gwiwa ga masu zuba hannun jari a Nijeriya.

Ya ce, “Yayin da wannan gwamnatin ke kan kokarin magance kalubalen samar da abinci da muke fuskanta tare da maida hankali kan ajandar guda 8 na Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu, ya zama wajibi mu hada hannu tare da yin amfani da shirye-shiryen da ake da su kamar su GIP domin ci gaba da manufofinsu, yin amfani da dabaru da hikimomin bunkasa tattalin arzikinmu da kuma kara kwarin gwiwar masu zuba jari.”
Shettima ya lura cewa, yayin da GIP ya yi daidai da manufofi da shirye-shiryen gwamnatin Tinubu, ya ce, shirin zai kyautata harkokin kananan manoma da sauran harkokin da suka shafi noma a fadin kasar nan.

Labarai Masu Nasaba

Ƙungiyar Buzaye Ta Yi Wa Nijeriya Ta’aziyyar Rasuwar Muhammadu Buhari

VFS Ta Ƙaddamar Da Cibiyar Yin Biza Zuwa Birtaniya A Kano

Ya ce tabbas shirin zai taimaka wajen magance matsaloli da dama da manoma ke fama a Nijeriya, musamman kananan manoma da suke fuskatar matsalar fitar da amfani gona.

Bisa wannan nasarar sanya hannun da aka samu, mataimakin shugaban ya jinjina wa ministan noma, ministan kudi, ministan shari’a da ministan harkokin waje da sauran wadanda suka dafa har aka kai ga wannan matakin.

Shi kuma a bangarensa, Jakadar Brazil a Nijeriya, Carlos Garcete, ya ce babban abin alfahari ne ga Brazil ta hada kai da ‘Green Imperatibe Project (GIP), yana mai cewa a cikin shekaru bakwai da suka gabata, an yi shawarwari da gwamnatin Nijeriya da nufin samun kudaden da ake bukata daga bankuna masu zaman kansu da na raya kasa na yanki don gudanar da wannan gagarumin aiki, wanda ya kai kusan dala biliyan 1.1.

A madadin gwamnatin kasar Burazil, Mista Garcete ya jinjina wa Shugaban Tinubu bisa nasarar tabbatar da dogon muhawarar yiyuwar shirin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Yi Tarukan Tattaunawar Kasa Da Kasa Kan More Damammakin Sin A Havana Da Doha

Next Post

Gobara Ta Kashe Yaro A Sansanin ‘Yan Gudun Hijira A Maiduguri

Related

Ƙungiyar Buzaye Ta Yi Wa Nijeriya Ta’aziyyar Rasuwar Muhammadu Buhari
Labarai

Ƙungiyar Buzaye Ta Yi Wa Nijeriya Ta’aziyyar Rasuwar Muhammadu Buhari

3 hours ago
VFS Ta Ƙaddamar Da Cibiyar Yin Biza Zuwa Birtaniya A Kano
Labarai

VFS Ta Ƙaddamar Da Cibiyar Yin Biza Zuwa Birtaniya A Kano

4 hours ago
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 20, Sun Ƙona Gidaje A Ƙauyukan Filato
Labarai

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 20, Sun Ƙona Gidaje A Ƙauyukan Filato

6 hours ago
Ƴansanda Sun Cafke Mutane Biyu Bisa Zargin Kashe Ɗan Ƙasar China
Labarai

Ƴansanda Sun Cafke Mutane Biyu Bisa Zargin Kashe Ɗan Ƙasar China

8 hours ago
Girman Kai Da Son Zuciya Ba Za Su Sa A Amince Ko Ba Da Hadin Kai Ba
Ra'ayi Riga

Girman Kai Da Son Zuciya Ba Za Su Sa A Amince Ko Ba Da Hadin Kai Ba

9 hours ago
Bayan Shekaru 6 A Hannun Boko Haram, Wasu Yara Biyu Sun Kuɓuta
Labarai

Bayan Shekaru 6 A Hannun Boko Haram, Wasu Yara Biyu Sun Kuɓuta

9 hours ago
Next Post
Gobara Ta Kashe Yaro A Sansanin ‘Yan Gudun Hijira A Maiduguri

Gobara Ta Kashe Yaro A Sansanin 'Yan Gudun Hijira A Maiduguri

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Yi Nasarar Harba Kumbon Dakon Kaya Na Tianzhou-9

Sin Ta Yi Nasarar Harba Kumbon Dakon Kaya Na Tianzhou-9

July 15, 2025
Ƙungiyar Buzaye Ta Yi Wa Nijeriya Ta’aziyyar Rasuwar Muhammadu Buhari

Ƙungiyar Buzaye Ta Yi Wa Nijeriya Ta’aziyyar Rasuwar Muhammadu Buhari

July 15, 2025
VFS Ta Ƙaddamar Da Cibiyar Yin Biza Zuwa Birtaniya A Kano

VFS Ta Ƙaddamar Da Cibiyar Yin Biza Zuwa Birtaniya A Kano

July 15, 2025
Xi Ya Gana Da Shugabannin Tawagogin Kasa Da Kasa Masu Halartar Taron SCO

Xi Ya Gana Da Shugabannin Tawagogin Kasa Da Kasa Masu Halartar Taron SCO

July 15, 2025
An Gudanar Da Taro Game Da Sana’ar Sarrafa Sinadarai Na Kasa Da Kasa Karo Na 12 A Beijing

An Gudanar Da Taro Game Da Sana’ar Sarrafa Sinadarai Na Kasa Da Kasa Karo Na 12 A Beijing

July 15, 2025
Yawan Karuwar GDPn Sin A Rabin Farkon Bana Ya Kai 5.3%

Yawan Karuwar GDPn Sin A Rabin Farkon Bana Ya Kai 5.3%

July 15, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 20, Sun Ƙona Gidaje A Ƙauyukan Filato

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 20, Sun Ƙona Gidaje A Ƙauyukan Filato

July 15, 2025
Shugaba Xi Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Game Da Aikin Raya Birane 

Shugaba Xi Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Game Da Aikin Raya Birane 

July 15, 2025
Ƴansanda Sun Cafke Mutane Biyu Bisa Zargin Kashe Ɗan Ƙasar China

Ƴansanda Sun Cafke Mutane Biyu Bisa Zargin Kashe Ɗan Ƙasar China

July 15, 2025
Taron Matasan Sin Da Afrika Kan Tsaro Zai Kirkiro Wata Sabuwar Mahanga Ta Magance Matsalolin Tsaro

Taron Matasan Sin Da Afrika Kan Tsaro Zai Kirkiro Wata Sabuwar Mahanga Ta Magance Matsalolin Tsaro

July 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.