ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, July 6, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijeriya Da Brazil Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Kasuwanci Ta Dala Biliyan 1

by Khalid Idris Doya and Sulaiman
1 year ago
Brazil

Nijeriya da kasar Brazil sun sanya hannu kan yarjejeniyar fahimtar juna a bangaren kasuwanci ta ‘Green Imperative Project’ (GIP) na dala biliyan 1.1 domin bunkasa harkokin noma da zuba hannun jari ga kamfanoni masu zaman kansu a Nijeriya.
Wannnan na cikin matakan kariya kan wadata kasa da abinci.

Shirin GIP, shiri ne kan aikin noma mafi girma a Afirka wanda ke ba da fifiko ga ci gaban noma mai dorewa, yana da nufin habaka yanayin tsari don samar da abinci a Nijeriya cikin inganci.

  • Hauhawar Farashi A Nijeriya Ta Ragu Zuwa 23.18 Cikin 100 A Fabrairu — NBS
  • Azumi Ya Dara Wa Sauran Ibadu

A shekarar 2018 ne aka fara rattaba hannu kan yarjejeniyar dala biliyan 1.1 na GIP 1, yayin da kashi na 2 na shirin dala biliyan 4.3 da kuma JBS na dala biliyan 2.5 aka sanya hannu a Brazil a ziyarar da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya kai kasar a bara.

ADVERTISEMENT

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya misalta sanya hannu kan shirin farko na kasuwancin GIP 1 a wani mataki na gwamnatin Tinubu na wadata kasa da abinci.
Da yake jawabi yayin rattaba hannu a rukunin shirin kasuwanci GIP 1 a fadar shugaban kasa da ke Abuja, Shettima ya ce shirin GIP zai bude wasu damarmakin masu tarin yawa da za su kai ga bude kofofin ci gaban tattalin arzikin kasa da inganta kwarin gwiwa ga masu zuba hannun jari a Nijeriya.

Ya ce, “Yayin da wannan gwamnatin ke kan kokarin magance kalubalen samar da abinci da muke fuskanta tare da maida hankali kan ajandar guda 8 na Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu, ya zama wajibi mu hada hannu tare da yin amfani da shirye-shiryen da ake da su kamar su GIP domin ci gaba da manufofinsu, yin amfani da dabaru da hikimomin bunkasa tattalin arzikinmu da kuma kara kwarin gwiwar masu zuba jari.”
Shettima ya lura cewa, yayin da GIP ya yi daidai da manufofi da shirye-shiryen gwamnatin Tinubu, ya ce, shirin zai kyautata harkokin kananan manoma da sauran harkokin da suka shafi noma a fadin kasar nan.

LABARAI MASU NASABA

Yajin Aiki: Ƙungiyar Likitocin Nijeriya Ta Ba Gwamnati Wa’adin Mako Huɗu

Rashin Tarbiyya Da Ilimin Addini Ne Ke Sa Matasa Ɗaukar Doka a Hannu – Hon. Aminu Adam

Ya ce tabbas shirin zai taimaka wajen magance matsaloli da dama da manoma ke fama a Nijeriya, musamman kananan manoma da suke fuskatar matsalar fitar da amfani gona.

Bisa wannan nasarar sanya hannun da aka samu, mataimakin shugaban ya jinjina wa ministan noma, ministan kudi, ministan shari’a da ministan harkokin waje da sauran wadanda suka dafa har aka kai ga wannan matakin.

Shi kuma a bangarensa, Jakadar Brazil a Nijeriya, Carlos Garcete, ya ce babban abin alfahari ne ga Brazil ta hada kai da ‘Green Imperatibe Project (GIP), yana mai cewa a cikin shekaru bakwai da suka gabata, an yi shawarwari da gwamnatin Nijeriya da nufin samun kudaden da ake bukata daga bankuna masu zaman kansu da na raya kasa na yanki don gudanar da wannan gagarumin aiki, wanda ya kai kusan dala biliyan 1.1.

A madadin gwamnatin kasar Burazil, Mista Garcete ya jinjina wa Shugaban Tinubu bisa nasarar tabbatar da dogon muhawarar yiyuwar shirin.

Brazil
Khalid Idris Doya
+ posts Bio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi
Brazil
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sabbin Shaidu Sun Bulla Dake Kara Tabbatar Da Ta’asar Amfani Da Sinadarai Masu Guba Yayin Da Dakarun Japan Ke Mamaya A Sassan Kasar Sin
  • Sulaiman
    An Gabatar Da Littafin “Bayanan Xi Jinping Kan Basirar Gudanar Da Ayyuka A Kananan Hukumomi”
  • Sulaiman
    Kayayyakin Sin Sun Jawo Hankalin Sassan Kasa Da Kasa
  • Sulaiman
    Sin Da Rasha Za Su Gudanar Da Atisayen Sojojin Ruwa Da Sintiri Na Hadin Gwiwa

MASU ALAKA

Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje
Labarai

Yajin Aiki: Ƙungiyar Likitocin Nijeriya Ta Ba Gwamnati Wa’adin Mako Huɗu

July 5, 2026
Rashin Tarbiyya Da Ilimin Addini Ne Ke Sa Matasa Ɗaukar Doka a Hannu – Hon. Aminu Adam
Labarai

Rashin Tarbiyya Da Ilimin Addini Ne Ke Sa Matasa Ɗaukar Doka a Hannu – Hon. Aminu Adam

July 5, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan ‘Ƴan Nijeriya 2 A Afrika Ta Kudu
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan ‘Ƴan Nijeriya 2 A Afrika Ta Kudu

July 5, 2026
Next Post
Gobara Ta Kashe Yaro A Sansanin ‘Yan Gudun Hijira A Maiduguri

Gobara Ta Kashe Yaro A Sansanin 'Yan Gudun Hijira A Maiduguri

LABARAI MASU NASABA

FIFA Ta Dakatar Da Aiwatar Da Hukuncin Hana Folarin Balogun Buga Wasa

FIFA Ta Dakatar Da Aiwatar Da Hukuncin Hana Folarin Balogun Buga Wasa

July 5, 2026
Sabbin Shaidu Sun Bulla Dake Kara Tabbatar Da Ta’asar Amfani Da Sinadarai Masu Guba Yayin Da Dakarun Japan Ke Mamaya A Sassan Kasar Sin

Sabbin Shaidu Sun Bulla Dake Kara Tabbatar Da Ta’asar Amfani Da Sinadarai Masu Guba Yayin Da Dakarun Japan Ke Mamaya A Sassan Kasar Sin

July 5, 2026
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

Yajin Aiki: Ƙungiyar Likitocin Nijeriya Ta Ba Gwamnati Wa’adin Mako Huɗu

July 5, 2026
An Gabatar Da Littafin “Bayanan Xi Jinping Kan Basirar Gudanar Da Ayyuka A Kananan Hukumomi”

An Gabatar Da Littafin “Bayanan Xi Jinping Kan Basirar Gudanar Da Ayyuka A Kananan Hukumomi”

July 5, 2026
Ko Kafa Ƴansandan Jihohi Zai Taimaka Wajen Kawo Ƙarshen Matsalolin Tsaro?

Ko Kafa Ƴansandan Jihohi Zai Taimaka Wajen Kawo Ƙarshen Matsalolin Tsaro?

July 5, 2026
Rashin Tarbiyya Da Ilimin Addini Ne Ke Sa Matasa Ɗaukar Doka a Hannu – Hon. Aminu Adam

Rashin Tarbiyya Da Ilimin Addini Ne Ke Sa Matasa Ɗaukar Doka a Hannu – Hon. Aminu Adam

July 5, 2026
Kayayyakin Sin Sun Jawo Hankalin Sassan Kasa Da Kasa

Kayayyakin Sin Sun Jawo Hankalin Sassan Kasa Da Kasa

July 5, 2026
Sin Da Rasha Za Su Gudanar Da Atisayen Sojojin Ruwa Da Sintiri Na Hadin Gwiwa

Sin Da Rasha Za Su Gudanar Da Atisayen Sojojin Ruwa Da Sintiri Na Hadin Gwiwa

July 5, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan ‘Ƴan Nijeriya 2 A Afrika Ta Kudu

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan ‘Ƴan Nijeriya 2 A Afrika Ta Kudu

July 5, 2026
Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ta Kafa Cibiyar Horar Da Ma’aikatan Jinya A Saliyo

Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ta Kafa Cibiyar Horar Da Ma’aikatan Jinya A Saliyo

July 5, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.