ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijeriya Da Brazil Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Kasuwanci Ta Dala Biliyan 1

by Khalid Idris Doya and Sulaiman
1 year ago
Brazil

Nijeriya da kasar Brazil sun sanya hannu kan yarjejeniyar fahimtar juna a bangaren kasuwanci ta ‘Green Imperative Project’ (GIP) na dala biliyan 1.1 domin bunkasa harkokin noma da zuba hannun jari ga kamfanoni masu zaman kansu a Nijeriya.
Wannnan na cikin matakan kariya kan wadata kasa da abinci.

Shirin GIP, shiri ne kan aikin noma mafi girma a Afirka wanda ke ba da fifiko ga ci gaban noma mai dorewa, yana da nufin habaka yanayin tsari don samar da abinci a Nijeriya cikin inganci.

  • Hauhawar Farashi A Nijeriya Ta Ragu Zuwa 23.18 Cikin 100 A Fabrairu — NBS
  • Azumi Ya Dara Wa Sauran Ibadu

A shekarar 2018 ne aka fara rattaba hannu kan yarjejeniyar dala biliyan 1.1 na GIP 1, yayin da kashi na 2 na shirin dala biliyan 4.3 da kuma JBS na dala biliyan 2.5 aka sanya hannu a Brazil a ziyarar da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya kai kasar a bara.

ADVERTISEMENT

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya misalta sanya hannu kan shirin farko na kasuwancin GIP 1 a wani mataki na gwamnatin Tinubu na wadata kasa da abinci.
Da yake jawabi yayin rattaba hannu a rukunin shirin kasuwanci GIP 1 a fadar shugaban kasa da ke Abuja, Shettima ya ce shirin GIP zai bude wasu damarmakin masu tarin yawa da za su kai ga bude kofofin ci gaban tattalin arzikin kasa da inganta kwarin gwiwa ga masu zuba hannun jari a Nijeriya.

Ya ce, “Yayin da wannan gwamnatin ke kan kokarin magance kalubalen samar da abinci da muke fuskanta tare da maida hankali kan ajandar guda 8 na Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu, ya zama wajibi mu hada hannu tare da yin amfani da shirye-shiryen da ake da su kamar su GIP domin ci gaba da manufofinsu, yin amfani da dabaru da hikimomin bunkasa tattalin arzikinmu da kuma kara kwarin gwiwar masu zuba jari.”
Shettima ya lura cewa, yayin da GIP ya yi daidai da manufofi da shirye-shiryen gwamnatin Tinubu, ya ce, shirin zai kyautata harkokin kananan manoma da sauran harkokin da suka shafi noma a fadin kasar nan.

LABARAI MASU NASABA

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Ya ce tabbas shirin zai taimaka wajen magance matsaloli da dama da manoma ke fama a Nijeriya, musamman kananan manoma da suke fuskatar matsalar fitar da amfani gona.

Bisa wannan nasarar sanya hannun da aka samu, mataimakin shugaban ya jinjina wa ministan noma, ministan kudi, ministan shari’a da ministan harkokin waje da sauran wadanda suka dafa har aka kai ga wannan matakin.

Shi kuma a bangarensa, Jakadar Brazil a Nijeriya, Carlos Garcete, ya ce babban abin alfahari ne ga Brazil ta hada kai da ‘Green Imperatibe Project (GIP), yana mai cewa a cikin shekaru bakwai da suka gabata, an yi shawarwari da gwamnatin Nijeriya da nufin samun kudaden da ake bukata daga bankuna masu zaman kansu da na raya kasa na yanki don gudanar da wannan gagarumin aiki, wanda ya kai kusan dala biliyan 1.1.

A madadin gwamnatin kasar Burazil, Mista Garcete ya jinjina wa Shugaban Tinubu bisa nasarar tabbatar da dogon muhawarar yiyuwar shirin.

Brazil
Khalid Idris Doya
+ posts Bio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Jami’an Tsaro Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 4, Sun Ceto Uwa Da Ɗanta A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Brazil
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya
  • Sulaiman
    Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari
  • Sulaiman
    Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana
  • Sulaiman
    Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

MASU ALAKA

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF
Rahotonni

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin
Rahotonni

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026
Labarai

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
Next Post
Gobara Ta Kashe Yaro A Sansanin ‘Yan Gudun Hijira A Maiduguri

Gobara Ta Kashe Yaro A Sansanin 'Yan Gudun Hijira A Maiduguri

LABARAI MASU NASABA

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

June 13, 2026
Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.