ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, November 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gobara Ta Lakume Kayayyakin Fiye Da Naira Miliyan 70 A Tsohuwar Kasuwar Gombe

by Sadiq
2 years ago
Gobara

Da tsakar daren ranar Larabar da ta gabata ce, gobara ta afku a tsohuwar kasuwar Gombe, wacce ake zargin wasu gungun ‘yan fashi da makami ne suka haddasa, da ta yi sanadin asarar dimbin dukiyar da aka kiyasta ta haura Naira miliyan 70.

Lamarin ya faru ne da misalin karfe 12 na dare a layin teloli, inda wutar ta mamaye shaguna kusan 20 tare da lalata su. Baya ga kadarorin da aka yi asara, ‘yan fashin sun kuma sace kayayyaki na miiyoyin nairori daga shagunan da lamarin ya shafa.

  • Gwamnatin Gombe Za Ta Dauki Sababbin Ma’aikatan Lafiya 200
  • Birnin Jinhua Na Kara Kyautata Alaka Da Kasashen Afirka

Daya daga cikin masu shagunan da lamarin ya shafa, Aminu Abdulrahman, ya bayyana cewa an buga masa waya ne da karfe 1:00 na dare, inda aka sanar da shi ibtila’in wutar.

ADVERTISEMENT

Ya ce ya yi asarar kekuna dinki guda goma da wasu kayayyaki masu daraja, wadanda aka kiyasta kudinsu ya kai naira miliyan biyu da dubu dari biyar.

Shi ma wani mai shago a tsohuwar kasuwar Gombe Sani Idris, ya bayyana abin da ya faru cikin bakin ciki, inda ya ce shi ma ya samu kiran waya ne da misalin karfe 1 na da re. Ya ce ya yi asarar kekunan dinki biyar da na saka da sauran kayayyaki wanda kudadensu ya kai na naira 800,000.

LABARAI MASU NASABA

Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4

NDLEA Ta Ƙona Miyagun Ƙwayoyi Sama Da Kilo 52,000 A Kaduna

Wadanda lamarin ya shafa sun yi kira ga gwamnati da masu hannu da shuni su kai wa wadanda ibtila’in ya shafa dauki gaggawa ddaga wannan mawuyacin hali.

Da yake tsokaci kan wannan mummunan lamari, shugaban kungiyar teloli reshen tsohuwar Kasuwar Gombe, Abu Safwan Muhammad Tukur, ya bayyana kaduwa da alhini kan lamarin.

Ya ce mambobinsu sun yi asarar dukiya mai dimbin yawa da suka hada da kekunan dinki da sauran kayayyaki da kudinsu ya haura naira miliyan 70.

Abu Safwan ya bukaci hukumar ba da agajin gaggawa ta Jihar Gombe ta gaggauta kai musu dauki tare da ba da tallafi ga masu shagunan da abin ya shafa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4
Manyan Labarai

Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4

November 13, 2025
NDLEA Ta Ƙona Miyagun Ƙwayoyi Sama Da Kilo 52,000 A Kaduna
Labarai

NDLEA Ta Ƙona Miyagun Ƙwayoyi Sama Da Kilo 52,000 A Kaduna

November 13, 2025
Jiga Jigan APC Sun Ziyarci Majalisar Wakilai Bayan Sauya Sheƙar Ƴan NNPP 2
Manyan Labarai

Jiga Jigan APC Sun Ziyarci Majalisar Wakilai Bayan Sauya Sheƙar Ƴan NNPP 2

November 13, 2025
Next Post
Maganar Da Na Taba Ji Da Ta Tsorata Ni A Kan Sana’ar Fim – Amina

Maganar Da Na Taba Ji Da Ta Tsorata Ni A Kan Sana’ar Fim - Amina

LABARAI MASU NASABA

Sin: Ya Zama Wajibi Japan Ta Janye Kalamanta Dangane Da Taiwan 

Sin: Ya Zama Wajibi Japan Ta Janye Kalamanta Dangane Da Taiwan 

November 13, 2025
Li Qiang Zai Halarci Tarukan SCO Da G20 Tare Da Ziyarar Aiki A Zambia

Li Qiang Zai Halarci Tarukan SCO Da G20 Tare Da Ziyarar Aiki A Zambia

November 13, 2025
Shugabar IOC: Gasar Wasanni Ta Kasar Sin Tana Da Babbar Ma’ana

Shugabar IOC: Gasar Wasanni Ta Kasar Sin Tana Da Babbar Ma’ana

November 13, 2025
Ayyukan Kirkire-kirkire Na Kamfanonin Sin Na Kara Zama Babbar Kadara Ga Duniya

Ayyukan Kirkire-kirkire Na Kamfanonin Sin Na Kara Zama Babbar Kadara Ga Duniya

November 13, 2025
Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4

Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4

November 13, 2025
An Gudanar Da Taro Mai Taken “Shugabancin Duniya: Ayyukan Matasa” A Johannesburg Dake Afirka Ta Kudu

An Gudanar Da Taro Mai Taken “Shugabancin Duniya: Ayyukan Matasa” A Johannesburg Dake Afirka Ta Kudu

November 13, 2025
Xi Ya Bukaci Matasa Masanan Harkokin Sin Su Kasance Gada Tsakanin Sin Da Duniya

Xi Ya Bukaci Matasa Masanan Harkokin Sin Su Kasance Gada Tsakanin Sin Da Duniya

November 13, 2025
Shugabannin Sin Da Comoros Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafa Alakar Diplomasiyya Tsakanin Kasashensu 

Shugabannin Sin Da Comoros Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafa Alakar Diplomasiyya Tsakanin Kasashensu 

November 13, 2025
Sanarwar Taron Ministocin Harkokin Waje Na Kungiyar G7 Ba Ta Da Tushe

Sanarwar Taron Ministocin Harkokin Waje Na Kungiyar G7 Ba Ta Da Tushe

November 13, 2025
NDLEA Ta Ƙona Miyagun Ƙwayoyi Sama Da Kilo 52,000 A Kaduna

NDLEA Ta Ƙona Miyagun Ƙwayoyi Sama Da Kilo 52,000 A Kaduna

November 13, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.