ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gobara Ta Lakume Kayayyakin Fiye Da Naira Miliyan 70 A Tsohuwar Kasuwar Gombe

by Sadiq
3 years ago
Gobara

Da tsakar daren ranar Larabar da ta gabata ce, gobara ta afku a tsohuwar kasuwar Gombe, wacce ake zargin wasu gungun ‘yan fashi da makami ne suka haddasa, da ta yi sanadin asarar dimbin dukiyar da aka kiyasta ta haura Naira miliyan 70.

Lamarin ya faru ne da misalin karfe 12 na dare a layin teloli, inda wutar ta mamaye shaguna kusan 20 tare da lalata su. Baya ga kadarorin da aka yi asara, ‘yan fashin sun kuma sace kayayyaki na miiyoyin nairori daga shagunan da lamarin ya shafa.

  • Gwamnatin Gombe Za Ta Dauki Sababbin Ma’aikatan Lafiya 200
  • Birnin Jinhua Na Kara Kyautata Alaka Da Kasashen Afirka

Daya daga cikin masu shagunan da lamarin ya shafa, Aminu Abdulrahman, ya bayyana cewa an buga masa waya ne da karfe 1:00 na dare, inda aka sanar da shi ibtila’in wutar.

ADVERTISEMENT

Ya ce ya yi asarar kekuna dinki guda goma da wasu kayayyaki masu daraja, wadanda aka kiyasta kudinsu ya kai naira miliyan biyu da dubu dari biyar.

Shi ma wani mai shago a tsohuwar kasuwar Gombe Sani Idris, ya bayyana abin da ya faru cikin bakin ciki, inda ya ce shi ma ya samu kiran waya ne da misalin karfe 1 na da re. Ya ce ya yi asarar kekunan dinki biyar da na saka da sauran kayayyaki wanda kudadensu ya kai na naira 800,000.

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

Wadanda lamarin ya shafa sun yi kira ga gwamnati da masu hannu da shuni su kai wa wadanda ibtila’in ya shafa dauki gaggawa ddaga wannan mawuyacin hali.

Da yake tsokaci kan wannan mummunan lamari, shugaban kungiyar teloli reshen tsohuwar Kasuwar Gombe, Abu Safwan Muhammad Tukur, ya bayyana kaduwa da alhini kan lamarin.

Ya ce mambobinsu sun yi asarar dukiya mai dimbin yawa da suka hada da kekunan dinki da sauran kayayyaki da kudinsu ya haura naira miliyan 70.

Abu Safwan ya bukaci hukumar ba da agajin gaggawa ta Jihar Gombe ta gaggauta kai musu dauki tare da ba da tallafi ga masu shagunan da abin ya shafa.

MASU ALAKA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Next Post
Maganar Da Na Taba Ji Da Ta Tsorata Ni A Kan Sana’ar Fim – Amina

Maganar Da Na Taba Ji Da Ta Tsorata Ni A Kan Sana’ar Fim - Amina

LABARAI MASU NASABA

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.