ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gobara Ta Lakume Kayayyakin Fiye Da Naira Miliyan 70 A Tsohuwar Kasuwar Gombe

by Sadiq
3 years ago
Gobara

Da tsakar daren ranar Larabar da ta gabata ce, gobara ta afku a tsohuwar kasuwar Gombe, wacce ake zargin wasu gungun ‘yan fashi da makami ne suka haddasa, da ta yi sanadin asarar dimbin dukiyar da aka kiyasta ta haura Naira miliyan 70.

Lamarin ya faru ne da misalin karfe 12 na dare a layin teloli, inda wutar ta mamaye shaguna kusan 20 tare da lalata su. Baya ga kadarorin da aka yi asara, ‘yan fashin sun kuma sace kayayyaki na miiyoyin nairori daga shagunan da lamarin ya shafa.

  • Gwamnatin Gombe Za Ta Dauki Sababbin Ma’aikatan Lafiya 200
  • Birnin Jinhua Na Kara Kyautata Alaka Da Kasashen Afirka

Daya daga cikin masu shagunan da lamarin ya shafa, Aminu Abdulrahman, ya bayyana cewa an buga masa waya ne da karfe 1:00 na dare, inda aka sanar da shi ibtila’in wutar.

ADVERTISEMENT

Ya ce ya yi asarar kekuna dinki guda goma da wasu kayayyaki masu daraja, wadanda aka kiyasta kudinsu ya kai naira miliyan biyu da dubu dari biyar.

Shi ma wani mai shago a tsohuwar kasuwar Gombe Sani Idris, ya bayyana abin da ya faru cikin bakin ciki, inda ya ce shi ma ya samu kiran waya ne da misalin karfe 1 na da re. Ya ce ya yi asarar kekunan dinki biyar da na saka da sauran kayayyaki wanda kudadensu ya kai na naira 800,000.

LABARAI MASU NASABA

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

Wadanda lamarin ya shafa sun yi kira ga gwamnati da masu hannu da shuni su kai wa wadanda ibtila’in ya shafa dauki gaggawa ddaga wannan mawuyacin hali.

Da yake tsokaci kan wannan mummunan lamari, shugaban kungiyar teloli reshen tsohuwar Kasuwar Gombe, Abu Safwan Muhammad Tukur, ya bayyana kaduwa da alhini kan lamarin.

Ya ce mambobinsu sun yi asarar dukiya mai dimbin yawa da suka hada da kekunan dinki da sauran kayayyaki da kudinsu ya haura naira miliyan 70.

Abu Safwan ya bukaci hukumar ba da agajin gaggawa ta Jihar Gombe ta gaggauta kai musu dauki tare da ba da tallafi ga masu shagunan da abin ya shafa.

MASU ALAKA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja
Labarai

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Next Post
Maganar Da Na Taba Ji Da Ta Tsorata Ni A Kan Sana’ar Fim – Amina

Maganar Da Na Taba Ji Da Ta Tsorata Ni A Kan Sana’ar Fim - Amina

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.