ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, December 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gobe Za a Tsunduma Yajin Aiki, An Gaza Cimma matsaya Tsakanin Gwamnati Da NLC

by Abubakar Sulaiman
2 years ago
NLC

Bayan ganawar sa’o’i huɗu da shugabannin majalisar dokoki da yammacin yau Lahadi a Abuja, ƙungiyar ƙwadago ta tabbatar da cewa za a gabatar gudanar da yajin aiki kamar yadda aka tsara a fadin ƙasar nan a ranar Litinin 3 ga watan Yuni, 2024.

Shugaban ƙungiyar ƙwadago (TUC) Festus Osifo ya bayyana cewa, matakin yajin aikin yana nan tsayin daka, kuma za su gabatar da koken Majalisar ga sassan ƙungiyarsu daban-daban, amma yajin aikin zai fara kamar yadda aka tsara.

  • NLC Na Gudanar Da Zanga-zanga A Ofishin KEDCO Na Kano Kan Ƙarin Ƙuɗin Wutar Lantarki
  • Mafi Ƙarancin Albashi: NLC Za Ta Tsunduma Yajin Aiki

Taron dai ya ƙunshi manyan mutane irin su shugaban majalisar dattawa Godswill Akpabio da kakakin majalisar wakilai Tajudeen Abbas, waɗanda suka yi yunƙurin hana ƙungiyoyin shiga yajin aikin saboda mummunan tasirin da zai iya yi ga al’umma da tattalin arziki Nijeriya.

ADVERTISEMENT

Rikicin da ke tsakanin gwamnatin tarayya da ƙungiyoyin ya samo asali ne daga taƙaddamar sabon mafi ƙarancin albashi na ƙasa da kuma ƙarin kuɗin wutar lantarki da aka yi a baya-bayan nan. Ƙungiyoyin ƙwadagon dai sun buƙaci a ƙara musu sabon mafi ƙarancin albashin ma’aikata, suna masu cewa ₦30,000 da ake biya a yanzu bai wadatar ba kuma ba dukkan gwamnoni ne ke biyan hakan ba.

 

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Alƙalin Alƙalan Nijeriya, Ibrahim Tanko Muhammad, Ya Rasu

Juyin Mulki: ECOWAS Ta Ayyana Dokar Ta-ɓaci A Yammacin Afirka

Ƙungiyoyin dai sun tsayar da ranar 31 ga watan Mayu domin gwamnati ta amince da sabon mafi ƙarancin albashi, amma tattaunawar ta ci tura, lamarin da ya kai ga ayyana yajin aikin.

Ƙungiyoyin sun yi watsi da tayin da gwamnati ta yi masu da dama, ciki har da na baya-bayan nan na ₦60,000, inda suke neman sabon mafi ƙarancin albashi na ₦497,000.

Haka suna son a duba cikar yarjejeniyar mafi ƙarancin albashin ma’aikata a halin yanzu, wanda ba a sake duba shi ba kamar yadda dokar ƙasa ta tanada na tsawon shekaru biyar a ƙarƙashin dokar mafi ƙarancin albashi na shekarar 2019.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tsohon Alƙalin Alƙalan Nijeriya, Ibrahim Tanko Muhammad, Ya Rasu
Da ɗumi-ɗuminsa

Tsohon Alƙalin Alƙalan Nijeriya, Ibrahim Tanko Muhammad, Ya Rasu

December 16, 2025
Juyin Mulki: ECOWAS Ta Ayyana Dokar Ta-ɓaci A Yammacin Afirka
Da ɗumi-ɗuminsa

Juyin Mulki: ECOWAS Ta Ayyana Dokar Ta-ɓaci A Yammacin Afirka

December 9, 2025
An Tsare Sojojin Nijeriya 11 A Burkina Faso Bayan Jirginsu Ya Yi Saukar Gaggawa
Da ɗumi-ɗuminsa

An Tsare Sojojin Nijeriya 11 A Burkina Faso Bayan Jirginsu Ya Yi Saukar Gaggawa

December 9, 2025
Next Post
Taron Karawa Juna Sani Kan Wayewar Kan Kasar Sin Ta Zamani Ya Bukaci Karin Nasarori A Fannin Ilimi

Taron Karawa Juna Sani Kan Wayewar Kan Kasar Sin Ta Zamani Ya Bukaci Karin Nasarori A Fannin Ilimi

LABARAI MASU NASABA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

December 21, 2025
Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

December 21, 2025
Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.