ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, November 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gobe Za a Tsunduma Yajin Aiki, An Gaza Cimma matsaya Tsakanin Gwamnati Da NLC

by Abubakar Sulaiman
1 year ago
NLC

Bayan ganawar sa’o’i huɗu da shugabannin majalisar dokoki da yammacin yau Lahadi a Abuja, ƙungiyar ƙwadago ta tabbatar da cewa za a gabatar gudanar da yajin aiki kamar yadda aka tsara a fadin ƙasar nan a ranar Litinin 3 ga watan Yuni, 2024.

Shugaban ƙungiyar ƙwadago (TUC) Festus Osifo ya bayyana cewa, matakin yajin aikin yana nan tsayin daka, kuma za su gabatar da koken Majalisar ga sassan ƙungiyarsu daban-daban, amma yajin aikin zai fara kamar yadda aka tsara.

  • NLC Na Gudanar Da Zanga-zanga A Ofishin KEDCO Na Kano Kan Ƙarin Ƙuɗin Wutar Lantarki
  • Mafi Ƙarancin Albashi: NLC Za Ta Tsunduma Yajin Aiki

Taron dai ya ƙunshi manyan mutane irin su shugaban majalisar dattawa Godswill Akpabio da kakakin majalisar wakilai Tajudeen Abbas, waɗanda suka yi yunƙurin hana ƙungiyoyin shiga yajin aikin saboda mummunan tasirin da zai iya yi ga al’umma da tattalin arziki Nijeriya.

ADVERTISEMENT

Rikicin da ke tsakanin gwamnatin tarayya da ƙungiyoyin ya samo asali ne daga taƙaddamar sabon mafi ƙarancin albashi na ƙasa da kuma ƙarin kuɗin wutar lantarki da aka yi a baya-bayan nan. Ƙungiyoyin ƙwadagon dai sun buƙaci a ƙara musu sabon mafi ƙarancin albashin ma’aikata, suna masu cewa ₦30,000 da ake biya a yanzu bai wadatar ba kuma ba dukkan gwamnoni ne ke biyan hakan ba.

 

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Gwamnan Anambra, Willie Obiano, Ya Rasu Yana Da Shekaru 70

Tsohon Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ya Rasu Yana Da Shekaru 86

Ƙungiyoyin dai sun tsayar da ranar 31 ga watan Mayu domin gwamnati ta amince da sabon mafi ƙarancin albashi, amma tattaunawar ta ci tura, lamarin da ya kai ga ayyana yajin aikin.

Ƙungiyoyin sun yi watsi da tayin da gwamnati ta yi masu da dama, ciki har da na baya-bayan nan na ₦60,000, inda suke neman sabon mafi ƙarancin albashi na ₦497,000.

Haka suna son a duba cikar yarjejeniyar mafi ƙarancin albashin ma’aikata a halin yanzu, wanda ba a sake duba shi ba kamar yadda dokar ƙasa ta tanada na tsawon shekaru biyar a ƙarƙashin dokar mafi ƙarancin albashi na shekarar 2019.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tsohon Gwamnan Anambra, Willie Obiano, Ya Rasu Yana Da Shekaru 70
Da ɗumi-ɗuminsa

Tsohon Gwamnan Anambra, Willie Obiano, Ya Rasu Yana Da Shekaru 70

November 14, 2025
Tsohon Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ya Rasu Yana Da Shekaru 86
Da ɗumi-ɗuminsa

Tsohon Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ya Rasu Yana Da Shekaru 86

November 5, 2025
ASUU Ta Dakatar Da Yajin Aiki, Ta Bai Wa Gwamnati Wa’adin Wata Guda Don Biyan Buƙatunta
Da ɗumi-ɗuminsa

ASUU Ta Dakatar Da Yajin Aiki, Ta Bai Wa Gwamnati Wa’adin Wata Guda Don Biyan Buƙatunta

October 22, 2025
Next Post
Taron Karawa Juna Sani Kan Wayewar Kan Kasar Sin Ta Zamani Ya Bukaci Karin Nasarori A Fannin Ilimi

Taron Karawa Juna Sani Kan Wayewar Kan Kasar Sin Ta Zamani Ya Bukaci Karin Nasarori A Fannin Ilimi

LABARAI MASU NASABA

Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima

Dalilin Asusun NADF Na Yin Hadaka Da Gwamnatin Jihar Jigawa

November 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Sarkin Thailand

Xi Jinping Ya Gana Da Sarkin Thailand

November 14, 2025
BUK Za Ta Kafa Cibiyar Horas da Aikin Jarida da Sabbin Kafofin Sadarwa Na Zamani

BUK Za Ta Kafa Cibiyar Horas da Aikin Jarida da Sabbin Kafofin Sadarwa Na Zamani

November 14, 2025
Babban Taron Kawancen Sin Da Afirka Ya Nuna Hadin Gwiwa Kan Gudanar Da Tsarin Shugabancin Duniya Na Bai-Daya

Babban Taron Kawancen Sin Da Afirka Ya Nuna Hadin Gwiwa Kan Gudanar Da Tsarin Shugabancin Duniya Na Bai-Daya

November 14, 2025
Sin Ta Yi Tsokaci Kan Kalaman Da Firaministar Japan Takaichi Sanae Ta Yi A Kanta

Sin Ta Yi Tsokaci Kan Kalaman Da Firaministar Japan Takaichi Sanae Ta Yi A Kanta

November 14, 2025
Tsohon Gwamnan Anambra, Willie Obiano, Ya Rasu Yana Da Shekaru 70

Tsohon Gwamnan Anambra, Willie Obiano, Ya Rasu Yana Da Shekaru 70

November 14, 2025
ADC Ta Tsara Ka’idojin Da Shugabanninta Za Su Bi Don Tunkarar Zaben 2027

ADC Ta Tsara Ka’idojin Da Shugabanninta Za Su Bi Don Tunkarar Zaben 2027

November 14, 2025

Rikicin PDP: Fiye Da Wakilai 3,000 Ne Za Su Raba Gardama A Babban Taron Jam’iyyar

November 14, 2025
Kasar Sin Ta Kara Azamar Kirkiro Da Fasahar Sadarwar 6G

Kasar Sin Ta Kara Azamar Kirkiro Da Fasahar Sadarwar 6G

November 14, 2025
GORON JUMA’A

GORON JUMA’A

November 14, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.