• English
  • Business News
Saturday, October 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gobe Za a Tsunduma Yajin Aiki, An Gaza Cimma matsaya Tsakanin Gwamnati Da NLC

by Abubakar Sulaiman
1 year ago
NLC

Bayan ganawar sa’o’i huɗu da shugabannin majalisar dokoki da yammacin yau Lahadi a Abuja, ƙungiyar ƙwadago ta tabbatar da cewa za a gabatar gudanar da yajin aiki kamar yadda aka tsara a fadin ƙasar nan a ranar Litinin 3 ga watan Yuni, 2024.

Shugaban ƙungiyar ƙwadago (TUC) Festus Osifo ya bayyana cewa, matakin yajin aikin yana nan tsayin daka, kuma za su gabatar da koken Majalisar ga sassan ƙungiyarsu daban-daban, amma yajin aikin zai fara kamar yadda aka tsara.

  • NLC Na Gudanar Da Zanga-zanga A Ofishin KEDCO Na Kano Kan Ƙarin Ƙuɗin Wutar Lantarki
  • Mafi Ƙarancin Albashi: NLC Za Ta Tsunduma Yajin Aiki

Taron dai ya ƙunshi manyan mutane irin su shugaban majalisar dattawa Godswill Akpabio da kakakin majalisar wakilai Tajudeen Abbas, waɗanda suka yi yunƙurin hana ƙungiyoyin shiga yajin aikin saboda mummunan tasirin da zai iya yi ga al’umma da tattalin arziki Nijeriya.

Rikicin da ke tsakanin gwamnatin tarayya da ƙungiyoyin ya samo asali ne daga taƙaddamar sabon mafi ƙarancin albashi na ƙasa da kuma ƙarin kuɗin wutar lantarki da aka yi a baya-bayan nan. Ƙungiyoyin ƙwadagon dai sun buƙaci a ƙara musu sabon mafi ƙarancin albashin ma’aikata, suna masu cewa ₦30,000 da ake biya a yanzu bai wadatar ba kuma ba dukkan gwamnoni ne ke biyan hakan ba.

 

LABARAI MASU NASABA

ASUU Ta Dakatar Da Yajin Aiki, Ta Bai Wa Gwamnati Wa’adin Wata Guda Don Biyan Buƙatunta

Gobara Ta Tashi A Kasuwar Alaba Da Ke Legas

Ƙungiyoyin dai sun tsayar da ranar 31 ga watan Mayu domin gwamnati ta amince da sabon mafi ƙarancin albashi, amma tattaunawar ta ci tura, lamarin da ya kai ga ayyana yajin aikin.

Ƙungiyoyin sun yi watsi da tayin da gwamnati ta yi masu da dama, ciki har da na baya-bayan nan na ₦60,000, inda suke neman sabon mafi ƙarancin albashi na ₦497,000.

Haka suna son a duba cikar yarjejeniyar mafi ƙarancin albashin ma’aikata a halin yanzu, wanda ba a sake duba shi ba kamar yadda dokar ƙasa ta tanada na tsawon shekaru biyar a ƙarƙashin dokar mafi ƙarancin albashi na shekarar 2019.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

ASUU Ta Dakatar Da Yajin Aiki, Ta Bai Wa Gwamnati Wa’adin Wata Guda Don Biyan Buƙatunta
Da ɗumi-ɗuminsa

ASUU Ta Dakatar Da Yajin Aiki, Ta Bai Wa Gwamnati Wa’adin Wata Guda Don Biyan Buƙatunta

October 22, 2025
Gobara Ta Tashi A Kasuwar Alaba Da Ke Legas
Da ɗumi-ɗuminsa

Gobara Ta Tashi A Kasuwar Alaba Da Ke Legas

October 22, 2025
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Da ɗumi-ɗuminsa

DHQ Ta Ƙaryata Rahoton Yunƙurin Yi Wa Tinubu Juyin Mulki

October 18, 2025
Next Post
Taron Karawa Juna Sani Kan Wayewar Kan Kasar Sin Ta Zamani Ya Bukaci Karin Nasarori A Fannin Ilimi

Taron Karawa Juna Sani Kan Wayewar Kan Kasar Sin Ta Zamani Ya Bukaci Karin Nasarori A Fannin Ilimi

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Nemi Amurka Ta Dakatar Da Hare-haren Shafin Intanet Kan Muhimman Kayayyakinta Nan Take

Kasar Sin Ta Nemi Amurka Ta Dakatar Da Hare-haren Shafin Intanet Kan Muhimman Kayayyakinta Nan Take

October 24, 2025
Ba Zan Kwatanta Matsayina Da Na Sarkin Bauchi Ba – Sabon Sarkin Duguri

Ba Zan Kwatanta Matsayina Da Na Sarkin Bauchi Ba – Sabon Sarkin Duguri

October 24, 2025
Gwamnatin Kaduna Ta Gano Ma’adanin Zinari Da Tagulla Da Za Su Haɓaka Tattalin Arziƙin Jihar

Gwamnatin Kaduna Ta Gano Ma’adanin Zinari Da Tagulla Da Za Su Haɓaka Tattalin Arziƙin Jihar

October 24, 2025
An Kebe Ranar 25 Ga Oktoba A Matsayin Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

An Kebe Ranar 25 Ga Oktoba A Matsayin Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

October 24, 2025

Gwamnatin Katsina Ta Ƙara Samar Da Dakarun Tsaro 200 Domin Maganace Ta’addanci

October 24, 2025
Sin Ta Saka Burikan Da Za Ta Cika A Shekaru 5 Masu Zuwa

Sin Ta Saka Burikan Da Za Ta Cika A Shekaru 5 Masu Zuwa

October 24, 2025
Jam’iyyar NNPP A Kaduna Ta Ƙaryata Batun Tsige Shugabanta

Jam’iyyar NNPP A Kaduna Ta Ƙaryata Batun Tsige Shugabanta

October 24, 2025
An Shirya Harba Kumbon Shenzhou-21 A Kwanan Nan

An Shirya Harba Kumbon Shenzhou-21 A Kwanan Nan

October 24, 2025
Shugaba Xi Ya Jagoranci Zaman Jin Ra’ayoyin Wadanda Ba ‘Yan JKS Ba Game Da Tsara Shirin Raya Kasa Karo Na 15 

Shugaba Xi Ya Jagoranci Zaman Jin Ra’ayoyin Wadanda Ba ‘Yan JKS Ba Game Da Tsara Shirin Raya Kasa Karo Na 15 

October 24, 2025
Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Wa Sarakuna Ba Zai Rage Musu Iko Ba A Shirinsa Na Ƙirƙirar Sabbin Masarautu

Gwamnan Bauchi Ya Naɗa Yayansa A Matsayin Sabon Sarkin Duguri

October 24, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.