• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Goman Ƙarshe Na Watan Ramadan [Darajarsu Da Mutsayinsu] Na 2

by Nuhu Ubale Ibrahim
2 years ago
in Bakon Marubuci, Fatawa, Ilimi
0
Goman Ƙarshe Na Watan Ramadan [Darajarsu Da Mutsayinsu] Na 1
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Daga cikin abin da Manzon Allah (S.A.W) yake shagaltuwa da shi a goman ƙarshe na Ramadan akwai ittikafi (al-Li’itikaf). An karɓo hadisi daga Abdullahi ɗan Umar Allah ya ƙara yarda a gare su, ya ce: “Manzon Allah (S.A.W) ya kasance yana ittikafi a goman ƙarshe na Ramadan” Bukhari da Muslim ne suka ruwaito.

Nana Aishatu Allah ya ƙara yarda a gare ta, ta ce: “Lalle Annabi (S.A.W) ya kasance yana ittikafi a goman ƙarshe na Ramadan har Allah ya karɓi rayuwarsa, sa’an nan matansa ma suka yi ittilafi a bayansa” Bukhari da Muslim ne suka ruwaito.

  • Goman Ƙarshe Na Watan Ramadan [Darajarsu Da Mutsayinsu] Na 1
  • SAHUR [Falalarsa Da Fa’idojinsa] Na 1

Manzon Allah (S.A.W) a ƙarahen rayuwarsa ya yi ittikafi na kwana 20 ne. Abu Huraira, Allah ya ƙara yarda a gare shi ya ce: “Mamzon Allah (S.A.W) ya kasnace yana ittikafi na kwana goma a kowace shekara, amma a shekarar da ya yi wafati a cikinta sai ya yi ittikafi na kwana ashirin” Bukhari ne ya ruwaito.

Ya tabbata Annabi (S.A.W) ya taba yin ittikafi a goman ƙarshe na watan Shauwal da bai sami yinsa a Ramadan ba kamar yadda Bukhari da Muslim suka ruwaito.

Mene ne ittikafi?
Ittikafi a harshen Larabci yana nufin tsayuwa da dauwwama a kan wani abu. Saboda haka ne ma ake cewa da ya zauna kuma lazimci masallaci ‘Mu’utakifun da kuma Akifun.’ Domin ƙarin haske duba al-Faiyumi; Misbahul Munir [shafi na 219] da Ibnu al-Manzur; Lisanul Arab [9/252]

Labarai Masu Nasaba

Jami’ar Ibadan Ta Bude Sashen Karatu A Gida Ta Intanet

Raya Al’ada: Bikin Kalankuwa Na 2025 A Kano

A shari’a ittikafi yana nufin wani mutum ya zauna ya lazimci masallaci a wata keɓantacciyar sifa ta daban” Ibnu Hajar; Fathul Bari [3/627].

Babban malamin Malikiyya al-Ƙarafi yana cewa: “Mutum ya tsare kansa a masallaci domin yin bauta ga Allah da wata keɓantacciyar sifa” al-Ƙarafi;¡ az-Zakhira [2/534].

Ittikafi yana daga cikin nafiloli da sunna ne aikata su. Duba Ibnu Abi Zaid al-Ƙairawani; ar-Risalatu [shafi na 88] da Khalil; Mukhtasar [shafi ma 105] da Ibnu Hajar Fathul Bari [4/627].


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AzumiGoman ƘarsheLailatul-ƘadariRamadan
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Gano Dajin Da Ya Fi Shekara Miliyan Hudu A Duniya

Next Post

Mata Ke Shugabantar Kashi 36 Na Bankunan Nijeriya

Related

Jami’ar Ibadan Ta Bude Sashen Karatu A Gida Ta Intanet
Ilimi

Jami’ar Ibadan Ta Bude Sashen Karatu A Gida Ta Intanet

1 day ago
Raya Al’ada: Bikin Kalankuwa Na 2025 A Kano
Bakon Marubuci

Raya Al’ada: Bikin Kalankuwa Na 2025 A Kano

2 days ago
Ilimin Fasaha Shi Ne Tafarkin Cire Nijeriya Daga Kangin Fatara – NBTE
Ilimi

Ilimin Fasaha Shi Ne Tafarkin Cire Nijeriya Daga Kangin Fatara – NBTE

1 week ago
Me Ake Nufi Da Ado? 
Bakon Marubuci

Me Ake Nufi Da Ado? 

1 week ago
Makarantun Da Ba Ƙwararrun Malamai Za Su Rasa Zama Cibiyar Rubuta Jarrabawar NECO
Ilimi

Makarantun Da Ba Ƙwararrun Malamai Za Su Rasa Zama Cibiyar Rubuta Jarrabawar NECO

2 weeks ago
Ɗalibai 750 Sun Amfana Da Bashin Karatu Na Naira Milyan 32.14 A Jihar Gombe
Ilimi

Ɗalibai 750 Sun Amfana Da Bashin Karatu Na Naira Milyan 32.14 A Jihar Gombe

3 weeks ago
Next Post
Bankunan Nijeriya

Mata Ke Shugabantar Kashi 36 Na Bankunan Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Ko Kin San… Amfanin Sabaya Ga Mace?

Ko Kin San… Amfanin Sabaya Ga Mace?

October 5, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Wanda Ake Zargi Da Haɗa-baki Kan Sace Mai Anguwa A Kano

October 5, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

October 5, 2025
Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.