ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mata Ke Shugabantar Kashi 36 Na Bankunan Nijeriya

by Bello Hamza
2 years ago
Bankunan Nijeriya

A shekarun baya, maza ne suka mamaye harkokin shugabancin bankunan Nijeriya amma a sannu a hankali a ‘yan shekarun nan mata na ci gaba da samun tagomashin zama shugabannin manyan bankuna a Nijeriya.

A halin yanzu akwai manyan bankuna 25 kuma yawan mata da ke shugabantar bankuna yana kara karuwa, a shekarar 2019 mace 1 ce ke shugabantar wani babban banki a Nijeriya amma a shekarar 2024 mata masu shugabantar bankuna sun kai 10 wanda ke nuna sun kai kashi 36 ke nan na yawan mata masu shugabantar bankuna a Nijeriya.

  • Goman Ƙarshe Na Watan Ramadan [Darajarsu Da Mutsayinsu] Na 2
  • CBN Ya Kara Adadin Kudin Ruwa Zuwa Kashi 24.75

Bayani ya nuna cewa, duk da wannan ci gaban da mata suka samu a bangaren harkokin banki suna ci gaba da fuskantar kalubale masu yawa. A kan haka ya kamata a taimaka wajen kara buda musu don su samu cika burinsu a bangaren harkar banki a kasar nan. Ga shugabanin banki mata da ke jagorantar manyan bankunan kasar nan a wannnan lokacin.

ADVERTISEMENT

1. Miriam Olusanya, Shugabar Guaranty Trust Bank (GTBank)
Miriam Olusanya ta kafa tarihin zama mace ta farko na zama shugabar Guaranty Trust Bank, ta dare wannan mukamin ne a watan Yuni na shekarar 2021. Ta yi digirinta na farko ne a bangaren hahada magunguna (Pharmacy) daga Jami’ar Ibadan, daga nan ta yi digirinta na biyu a bangaren harkokin kasuwanci daga Jami’ar Liberpool ta kasar Birtaniya. Ta fara aiki a GTB ne a shekararJ 1998 inda ta ci gaba da samun karin girma har zuwa mastayin shugabar banking gaba daya.

2 Yemisi Edun, Shugabar First City Monument Bank (FCMB)
An nada Yemisi Edun shugabancin bankin ne a watan Yuli na shekarar 2021. Ta yi karatun ta gaba daya ne a kan bangaren harkokin banki ta kuma dade tana aiki a bangaren.
Edun ta jagoranci bankin zuwa matsayin bunkasar da ba a taba gani ba, har bankin ya zama cikin manya-manyan bankunan da ake ji dasu a Nijeriya. A tsarin jagorancinta ta fi bayar da muhimmanci a kan gamsar da abokan hulda, wannan ya sa bankin ya samu karin masu hulda, abin kuma da ya kara wa bankin riba mai yawa. Bayani ya nuna cewa, ana matukar mutuntata a cikin gammayar kungiyoyin bankuna na kasar nan.

LABARAI MASU NASABA

Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya

NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho

3 Halima Buba, Shugabar SunTrust Bank
Halima Buba, kwararriyar ma’aikaciyar banki, ta zama shugabar Sun Trust Bank ne a watan Janairu na shekarar 2012, bayan ta shafe akalla shekara 22 tana aiki a bangaren bankunan Nijeriya, cikin bankuna da ta yi aiki a ciki sun hada da All States Trust Bank, Zenith Bank, Inland Bank Plc, Oceanic Bank Plc, da kuma Ecobank Nigeria Limited, tana kuma cikin daidaikun matan da suka samu irin wannan nasarar a kasar nan.

4 Ireti Samuel-Ogbu, Shugabar Citibank Nigeria
An nada Ireti Samuel-Ogbu shugabancin bankin ne a watan Satumba na shekarar 2020. Wannan ne karo na farko da bankin ya nada mace a matsayin shugaba, tun da aka kafa bankin shekara 36 da suka wuce.
Kafin ta zama shugabar bankin ta rike mukamin shugaba mai kula da yankin Turai, Gabas ta tsakiya da Afrika a ofishinsu da ke Landan.

5 Mrs. Nneka Onyeali-Ikpe, Shugabar Fidelity Bank
Mrs Onyeali-Ikpe ta kama aiki a matsayin shugabar banki ne a ranar 1 ga watan Janairu na shekarar 2021
Ta kuma kasance a kan gaba a jagororin da suka bayar da gudummawar bunkasa bankin a cikin shekara 6 da suka wuce. Tun da farko ta taba rike babbar darakta mai kula da yankin kudu maso yammacin Nijeriya da ke da hedikwata a Legas, ta kuma jagoranci bunkasa bankin har ta kai wannan matsayin.
A cikin shekaru 30 da ta yi tana aikin banki, ta samu nasarar zama shugabar bankin ta yi aiki a bankuna da dama da suka hada da Standard Chartered Bank Plc, Zenith Bank Plc, da kuma Citizens International Bank Limited.

6 Tomi Somefun, Shugabar Unity Bank
Tomi Somefun ta zama shugabar Unity Bank ne a watan Agusta na shekarar 2015.
Ta yi karatu a wurare da dama ciki har da Jami’a Obafemi Awolowo, Ile-Ife a Jihar Osun da Jami’ar Harbard Business School da kuma Jami’ar Columbia da ke Amurka.
Somefun ta fara aikin banki ne a kamfanin Peat Marwick and Co. daga na ta koma Arthur Andersen (KPMG) kafin aka nada ta shugabancin Unity Bank Plc.

7 Kafilat Araoye, Shugabar Lotus Bank
An nada Kafilat Araoye shugabancin Lotus bank ne tun a watan Mayu na shekarar 2021.
Ta karantar tarihi a Jami’ar Obafemi Awolowo ta garin Ile-Ife a shekarar (1985), ta yi digirinta na biyu a Jami’ar Legas a shekarar 1987 ta kuma yi karatu don kwarewa a harkokin bankin musulunci a wata makaranta da ke kasar Bahrain.
Ta kuma samu nasarar halartar kwasa-kwasai don kara kwarewa a ciki da wajen kasar nan.

8 Bukola Smith, Shugabar FSDH Merchant Bank
Bukola Smith ta yi karatu a bangaren harkokin sarrafa kudi a Jami’ar Manchester da ke Birtaniya.
Ta zama shugabar bankin ne a watan Afrilu na shekarar 2021. Bankin ya samu ci gaba mai muhimmanci a karkashin jagorancinta.

9 Yetunde Bolanle Oni, Shugabar Union Bank
A cikin watan Janairu na wannan shekarar aka nada Yetunde Bolanle Oni shugabancin Union Bank, ta samu horo a ciki da wajen kasar nan ciki har da Jami’ar Odford da ke Birtaniya. Tun da ta zama shugabar bankin an samu gaggarumin ci gaba ta kuma dora bankin a kan alkibla mai muhimmanci.

10 Dr. Adaora Umeoji, Shugabar Zenith Bank
Nadin Dr. Adaora Umeoji matsayin shugabar bankin Zenith zai fara aiki ne daga ranar 1 ga watan Yuni na shekarar 2024, za ta kasane mace ta farko da za ta dana wannan mukamin.

Kafin nadata ta rike mukamin mataimakiyar shugabar bankin tun daga watan Oktoba na shekarar 2016. A shekaru 30 da ta yi a bangaren harkokin bankuna shekara 26 daga ciki ta yi sune a bankin Zenith.

Masu sharhin sun bayyana cewa, samun mata a shugabancin bankuna a kasar nan wata lama ce ta jajircewar mata da kuma rikon gaskiyarsu haka kuma wannan yana nuna irin gudummawar da suke bayarwa a bangaren bunkasar tattalin arzikin Nijeriya.

Bankunan Nijeriya
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Hijira 1448:Za A Samu Yalwar Tattalin Arziƙi A Nijeriya —Sheikh Muhajjadina
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Amfani Da Matar Soja Wajen Isar Da Sakon Bukata

MASU ALAKA

Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
Tattalin Arziki

Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya

June 20, 2026
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho
Tattalin Arziki

NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho

June 20, 2026
Yawan Man Da Nijeriya Ke Hakowa Ya Karu Da Ganga 177,000 A Janairu
Tattalin Arziki

Dalilin Da Ya Sa Matatar Dangote Ta Kara Habaka Tura Man Fetur

June 13, 2026
Next Post
NLC

Tsohon Shugaban NLC, Ali Ciroma, Ya Rasu

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.