ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Goman Ƙarshe Na Watan Ramadan [Darajarsu Da Mutsayinsu] Na 1

by Nuhu Ubale Ibrahim
2 years ago
Ramadan

Goman ƙarshen Ramadan su ne mafi girman dararen duniya baki ɗaya, domin a cikinsu Lailatul-Ƙadari yake. Allah Ta’ala Yana cewa: “Lailatul-Ƙadari ya fi wata dubu alheri” Suratul Ƙadri aya ta 3.

Babban malamin tafsiri al-Imam al-Bagawi, Allah Ya yi masa rahama yana cewa: “Malaman tafsiri sun bayyana ma’anar ayar da cewa: aikata aikin ƙwarai a cikin daren Lailatul-Ƙadari shi ne ya fi alheri sama da aikin ƙwarai a cikin watanni dubu wanda babu Lailatul-Ƙadari a cikinsu”

  • CIYARWA [Falalarta Da Muhimmancinta] Na 1
  • SAHUR [Falalarsa Da Fa’idojinsa] Na 1

Hadisi ya tabbata a cikin Al-mujtaba na Imam an-Nasa’i da Musnad na Imam Ahmad daga Abu Huraira Allah Ya ƙara yarda a gare shi ya ce: Manzon Allah (S.A.W) ya ce: “Ramadana ya zo muku, wata ne mai wata irin albrka, Allah Mai girma da ɗaukaka ya wajabta muku azumtar sa, ana buɗe ƙofofin Aljanna a cikinsa, ana kuma rufe ƙofofin Jahannama a cikinsa, a cikinsa akwai wani dare da ya fi wata dubu alheri, duk wanda aka haramta masa alherinsa, to, tabbas an haramta masa alheri”

ADVERTISEMENT

Ya zo a cikin Sahihul Bukhari da Muslim, Manzon Allah (S.A.W) ya ce: “Duk wanda ya tsayu a daren Lailatul-Ƙadari yana mai imani da neman lada, to, an gafarta masa zunubansa”

Wannan dare yana cikin goman ƙarshe na Ramadan. Manzon Allah (S.A.W) ya kasance yana cewa da Sahabbai: Ku kirdadi Lailatul-Ƙadari a goman ƙarshe na Ramadan. Bukhari da Muslim ne suka ruwaito.

LABARAI MASU NASABA

Hukumar NCCE Ta Yi Tsare-tsaren Bunƙasa Horar Da Malamai

Abubuwan Da Ya Kamata Magidanci Ya Sani Bayan Matarsa Ta Haihu

Ana karɓo hadisi daga Nana Aishatu, Allah Ya ƙara yarda a gare ta, ta ce: Lalle Manzon Allah (S.A.W) ya ce: “Ku kirdadi Lailatul-Ƙadari a cikin dare mara na goman ƙarshe na Ramadana” Bukhari da Muslim ne suka ruwaito.

Manzon Allah (S.AW) ya fi kowa girman matsayi da alfarma da daraja da martaba a wurin Allah. Allah Ya gafarta masa abin da ya aikata da wanda bai aikata ba amma duk da haka yana ƙara ƙaimi da ƙwazo a goman ƙarshe na Ramadan sama da ƙwazonsa a goman farko da ta tsakiya na wannan wata mai albarka. Nana Aisha Allah Ya ƙara mata yarda ta ce: “Manzon Allah (S.A.W) ya kasance idan goman ƙarshe ta shiga, sai ya ƙara zage dantse, ya kuma raya daren gaba ɗaya, kuma ya tayar da iyalansa daga barci” Bukhari da Muslim ne suka ruwaito. A wata ruwaya ta Muslim cewa ta yi:” Manzon Allah (S.A.W) ya kasance yana ƙoƙari a goman ƙarshe irin ƙoƙarin da baya yinsa a waninsa”

Sayyadina Aliyu ɗan Abu Ɗalib, Allah Ya ƙara masa yarda ya ce: “Lalle annabi (S.A.W) ya kasance yana tayar da iyalansa a goman ƙarshe na Ramadana” Tirmizi ne ya ruwaito da salsala ingantacciya.

Ramadan
Nuhu Ubale Ibrahim
+ postsBio
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    Karamar Sallah: Sallar Idi A Wajen Musulmi…
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    SAHUR [Falalarsa Da Fa’idojinsa] Na 23
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    SAHUR [Falalarsa Da Fa’idojinsa] Na 22

MASU ALAKA

Hukumar NCCE Ta Yi Tsare-tsaren Bunƙasa Horar Da Malamai
Ilimi

Hukumar NCCE Ta Yi Tsare-tsaren Bunƙasa Horar Da Malamai

May 31, 2026
Abubuwan Da Ya Kamata Magidanci Ya Sani Bayan Matarsa Ta Haihu
Ilimi

Abubuwan Da Ya Kamata Magidanci Ya Sani Bayan Matarsa Ta Haihu

May 30, 2026
Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1
Bakon Marubuci

Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1

May 27, 2026
Next Post
Isra’ila Ta Kori Kafar Talabijin Ta Al Jazeera Daga Kasarta

Isra'ila Ta Kori Kafar Talabijin Ta Al Jazeera Daga Kasarta

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.