• English
  • Business News
Tuesday, September 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gombe Da Gidauniyar ‘Bill & Melinda Gates’ Sun Hada Gwiwa Don Bunkasa Kiwon Lafiya Da Noma

by Khalid Idris Doya
10 months ago
in Labarai
0
Gombe Da Gidauniyar ‘Bill & Melinda Gates’ Sun Hada Gwiwa Don Bunkasa Kiwon Lafiya Da Noma
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?

‘Yan Bindiga Sun Yi Wa Hakimi Yankan Rago A Zamfara

Gwamnatin Jihar Gombe da Gidauniyar ‘Bill and Melinda Gates’ (BMGF) sun jaddada aniyarsu ta samar da hadin gwiwa mai karfi da samar da muhimman dabaru don inganta bangarorin kiwon lafiya da noma.

An cimma wannar matsaya ce yayin wata muhimmiyar ganawa tsakanin Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya da tawagar gidauniyar ta BMGF, karkashin jagorancin Manajanta na Nijeriya, Mista Uche Amaonwu, a masaukin Gwamnan Gombe da ke Abuja.

  • Trump Ya Gayyaci Mark Zuckerberg Cin Abinci
  • Me Ya Sa Lee Hsien Loong Yake Da Karfin Gwiwa Kan Makomar Kasar Sin?

A yayin taron, Mista Amaonwu ya yaba wa Gwamna Inuwa bisa irin nasarorin da gwamnatinsa ta samu a fannonin kiwon lafiya, da ilimi, da sauransu, inda ya ce Jihar Gombe ta yi fice bisa tsare-tsarenta na kiwon lafiya masu inganci da nagarta.

Ya jaddada cewa an zabi Jihar Gombe a sabon shirin hadin gwiwa na gidauniyar ne saboda nagartattun tsare-tsarenta na kula da lafiya.

Ya kuma bayyana fatan cewa sabunta hadin gwiwar zai kara habaka ci gaba a fannin kiwon lafiya da bunkasa noma tare da samar da ingantacciyar rayuwa ga al’ummar Jihar Gombe.

A nasa jawabin, Gwamna Inuwa ya bayyana wasu nasarorin da gwamnatinsa ta samu tun hawansa karagar mulki, inda ya bayyana cewa Jihar Gombe ta tashi daga mataki na kuran baya a fagen ci gaba zuwa mataki na gaba a fannonin tattalin arziki da zamantakewa.

Gwamnan ya jaddada fifikon da gwamnatinsa take bai wa fannin kiwon lafiya, ilimi, noma, da gina al’umma, wadanda duk suke da muhimmanci wajen samun ci gaba mai dorewa.

A bangaren kiwon lafiya, Gwamna Inuwa ya yi karin bayani kan wasu nasarorin da ya samu, ciki har da tabbatar da cewa dukkan gundumomi 114 da ke jihar suna da akalla cibiyar kiwon lafiya daya a matakin farko da kuma kafa hukumar taimakekeniyar lafiya ta Jihar Gombe (GoHealth), wacce ta dauki masu rauni da ke cin gajiyar jinya su fiye da 340,000.

Sauran nasarorin a cewarsa, sun hada da kafa hukumar kula da asibitoci don inganta harkokin kiwon lafiya, da gina sabin manya da kananan asibitoci a fadin jihar da daukar ma’aikatan lafiya aiki don magance gibin ma’aikata a fannin da dai sauransu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Bill & Melinda GatesGidauniyaGombe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Farashin Litar Mai Ka Iya Dawowa N900 A Bukukuwan Sabuwar Shekara – Dillalai

Next Post

Gwamnan Gombe Ya Aza Tubalin Gina Majalisar Dokoki Da Babbar Kotun Jiha Na Zamani

Related

Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?
Labarai

Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?

2 hours ago
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Yi Wa Hakimi Yankan Rago A Zamfara

3 hours ago
Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana
Labarai

Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana

5 hours ago
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Manyan Labarai

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Mayar Wa Atiku Martani Kan Cewar ‘Yan Nijeriya Na Fama Da Yunwa

6 hours ago
Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 
Manyan Labarai

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

14 hours ago
Tinubu
Labarai

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Yanke Hutu, Zai Dawo Abuja Gobe Talata

15 hours ago
Next Post
Gwamnan Gombe Ya Aza Tubalin Gina Majalisar Dokoki Da Babbar Kotun Jiha Na Zamani

Gwamnan Gombe Ya Aza Tubalin Gina Majalisar Dokoki Da Babbar Kotun Jiha Na Zamani

LABARAI MASU NASABA

Dan Sanda Ya Kashe Abokin Aikinsa Da Almakashi Har Lahira A Kebbi

Wata Ta Kashe ’Yar Uwarta Kan Bashin Naira 800 A Ondo

September 16, 2025
Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?

Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?

September 16, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Yi Wa Hakimi Yankan Rago A Zamfara

September 16, 2025
Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana

Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana

September 16, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Mayar Wa Atiku Martani Kan Cewar ‘Yan Nijeriya Na Fama Da Yunwa

September 16, 2025
Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

September 15, 2025
Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

September 15, 2025
Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu

Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu

September 15, 2025
Tinubu

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Yanke Hutu, Zai Dawo Abuja Gobe Talata

September 15, 2025
Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”

Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”

September 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.