ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gombe Da Gidauniyar ‘Bill & Melinda Gates’ Sun Hada Gwiwa Don Bunkasa Kiwon Lafiya Da Noma

by Khalid Idris Doya
2 years ago
gombe

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

Gwamnatin Jihar Gombe da Gidauniyar ‘Bill and Melinda Gates’ (BMGF) sun jaddada aniyarsu ta samar da hadin gwiwa mai karfi da samar da muhimman dabaru don inganta bangarorin kiwon lafiya da noma.

An cimma wannar matsaya ce yayin wata muhimmiyar ganawa tsakanin Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya da tawagar gidauniyar ta BMGF, karkashin jagorancin Manajanta na Nijeriya, Mista Uche Amaonwu, a masaukin Gwamnan Gombe da ke Abuja.

  • Trump Ya Gayyaci Mark Zuckerberg Cin Abinci
  • Me Ya Sa Lee Hsien Loong Yake Da Karfin Gwiwa Kan Makomar Kasar Sin?

A yayin taron, Mista Amaonwu ya yaba wa Gwamna Inuwa bisa irin nasarorin da gwamnatinsa ta samu a fannonin kiwon lafiya, da ilimi, da sauransu, inda ya ce Jihar Gombe ta yi fice bisa tsare-tsarenta na kiwon lafiya masu inganci da nagarta.

Ya jaddada cewa an zabi Jihar Gombe a sabon shirin hadin gwiwa na gidauniyar ne saboda nagartattun tsare-tsarenta na kula da lafiya.

Ya kuma bayyana fatan cewa sabunta hadin gwiwar zai kara habaka ci gaba a fannin kiwon lafiya da bunkasa noma tare da samar da ingantacciyar rayuwa ga al’ummar Jihar Gombe.

A nasa jawabin, Gwamna Inuwa ya bayyana wasu nasarorin da gwamnatinsa ta samu tun hawansa karagar mulki, inda ya bayyana cewa Jihar Gombe ta tashi daga mataki na kuran baya a fagen ci gaba zuwa mataki na gaba a fannonin tattalin arziki da zamantakewa.

Gwamnan ya jaddada fifikon da gwamnatinsa take bai wa fannin kiwon lafiya, ilimi, noma, da gina al’umma, wadanda duk suke da muhimmanci wajen samun ci gaba mai dorewa.

A bangaren kiwon lafiya, Gwamna Inuwa ya yi karin bayani kan wasu nasarorin da ya samu, ciki har da tabbatar da cewa dukkan gundumomi 114 da ke jihar suna da akalla cibiyar kiwon lafiya daya a matakin farko da kuma kafa hukumar taimakekeniyar lafiya ta Jihar Gombe (GoHealth), wacce ta dauki masu rauni da ke cin gajiyar jinya su fiye da 340,000.

Sauran nasarorin a cewarsa, sun hada da kafa hukumar kula da asibitoci don inganta harkokin kiwon lafiya, da gina sabin manya da kananan asibitoci a fadin jihar da daukar ma’aikatan lafiya aiki don magance gibin ma’aikata a fannin da dai sauransu.

gombe
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Yaro Ya Harbe Kansa Har Lahira Bayan Mafarauci Ya Yi Sakaci Da Bindigarsa A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    An Kama Mutane 5 Da Sassan Jikin Ɗan’Adam Za Su Yi Tsafi A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mai Neman Takarar Gwamnan Bauchi, Bala Jibrin, Ya Fice Daga APC Kan Zargin Ɗoki-ɗora
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu
Labarai

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu
Manyan Labarai

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin
Labarai

Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

September 9, 2026
Next Post
Gwamnan Gombe Ya Aza Tubalin Gina Majalisar Dokoki Da Babbar Kotun Jiha Na Zamani

Gwamnan Gombe Ya Aza Tubalin Gina Majalisar Dokoki Da Babbar Kotun Jiha Na Zamani

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026
Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

September 9, 2026
Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

September 9, 2026
Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

September 9, 2026
“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

September 9, 2026
’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

September 9, 2026
Taron Kolin Urumqi Ya Mayar Da Hankali Kan Kwarewar Shugabanci A Xinjiang Da Muhimmancinta Ga Duniya

Taron Kolin Urumqi Ya Mayar Da Hankali Kan Kwarewar Shugabanci A Xinjiang Da Muhimmancinta Ga Duniya

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.