ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 26, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Gombe Ya Aza Tubalin Gina Majalisar Dokoki Da Babbar Kotun Jiha Na Zamani

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Gombe

Gwamna Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya aza tubalin gina katafaren ginin Majalisar Dokoki da Babbar Kotun Jiha a wani bangare na gina cibiyoyin rukunan gwamnati 3 wanda zai kunshi bangaren zartarwa, da sashin majalisa da kuma na shari’a.

Da yake jawabi a wajen taron, Gwamna Inuwa ya bayyana kudirin gwamnatinsa na samar da kyakkyawan yanayin aiki ga dukkan bangarorin gwamnati, don ba su damar gudanar da aiki yadda ya kamata.

  • Dikko Radda Ya Bai Wa Gwarazan Hikayata Kyautar Kudi
  • Ruguza Tsohon Tsari Na Duniya Zai Haifar Da Ci Gaban Afirka

Gwamnan ya bayyana cewa an ba da kwangilar gina babbar kotun jihar ne kan kudi naira biliyan 14 da miliyan 900, yayin da ginin majalisar zai lakume naira biliyan 14. da miliyan 5.

ADVERTISEMENT

Ya yi amfani da wannar dama wajen bayyana aniyarsa ta maida tsohuwar Majalisar Dokoki da Babbar Kotun jihar zuwa asibiti da kwalejin ‘yan mata, don amfanin al’ummar yankin da kewaye.

Da yake bayyana aikin a matsayin wani matakin da ba a taba ganin irinsa ba na cike gibin ababen more rayuwa, Inuwa ya ce, “Tun da aka kirkiro ta shekaru 28 da suka gabata, Jihar Gombe ba ta taba ganin irin wannan aiki ba don samar da yanayin aiki da ya dace ga shugabanni da ma’aikatan gwamnati a jihar.

LABARAI MASU NASABA

Jagoran Matasan AAC Kwamret Yahaya Soje Ya Nemi A Saki Sowore

Har Yanzu Ba Mu Karɓi Kuɗaɗen Da Aka Ware Mana Na Zaɓukan 2027 Ba – INEC

“Ta hanyar samar musu da wuraren aiki na zamani kamar ko’ina a duniya, muna kara tabbatar da aniya da jajircewarmu na karfafa tsarin gudanar da mulki da ke tabbatar da dimokuradiyya da ci gaban al’umma.

“Tare da wadannan ayyuka, muna fatan bude wani sabon babi da zai kara karfafa alaka da bai wa kowane rukunin gwamnati damar gudanar da ayyukansa yadda ya kamata.

“Wadannan ayyuka ba kawai gine-gine ne na zahiri ba, ginshiki ne na samun ci gaba mai dorewa, inda jagoranci da dimokuradiyya za su karfafa, kuma kowane dan kasa ya samu damar ci gaba yadda ya kamata,” in ji shi.

Gwamnan ya yaba da kyakkyawar alakar aiki da ke tsakanin bangaren zartaswa da sauran bangarorin gwamnati, wanda ya ce ya taimaka wajen cimma nasarorin da gwamnatin mai ci take samu.

Shi ma kwararren mai sanya ido kan aikin daga kamfanin Artec Practice Limited, Arc. Oni Oluseyi, ya ce aikin babbar kotun jihar gini ne na zamani wadda ya kunshi dakunan shari’a 12 masu iya daukar mutane 60, da dakin taro, da ofisoshin alkalai da sauran manyan jami’an shari’a, da dakin karatu na zamani (E-library) da kuma dakin ganawa da manema labarai da dai sauran wurare.

Dangane da ginin majalisar dokokin jihar kuwa, kwararren ya ce an tsara ginin ne zuwa bangarori biyu da suka kunshi zauren majalisa, da ofisoshin kakakin majalisa, da na mataimakinsa da sauran mambobin majalisar, da dakin karatu, da na taro, da wuraren liyafa da dakunan taro, da asibiti da zauren ganawa da manema labarai da dai sauransu.

Manajojin Daraktocin kamfanonin gine-ginen da aka bai wa kwangilolin, Kamfanin Datum Construction, Daher Kaworma da takwaransa na Kamfanin GMC George Maroum, sun tabbatarwa gwamna da al’ummar jihar cewa za su gudanar da ayyuka masu inganci da nagarta.

Gombe
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa

MASU ALAKA

Sowore Ya Sha Alwashin Ci Gaba Da Gwagwarmaya Duk Da Tsare Shi A Gidan Yarin Kuje
Labarai

Jagoran Matasan AAC Kwamret Yahaya Soje Ya Nemi A Saki Sowore

June 26, 2026
Har Yanzu Ba Mu Karɓi Kuɗaɗen Da Aka Ware Mana Na Zaɓukan 2027 Ba – INEC
Manyan Labarai

Har Yanzu Ba Mu Karɓi Kuɗaɗen Da Aka Ware Mana Na Zaɓukan 2027 Ba – INEC

June 26, 2026
Husaini Isa Ya Gargaɗi Ƴan Takarar NDC A Kano Kan Buƙatar Kiyaye Ƙa’dojin Jam’iyya
Labarai

Husaini Isa Ya Gargaɗi Ƴan Takarar NDC A Kano Kan Buƙatar Kiyaye Ƙa’dojin Jam’iyya

June 26, 2026
Next Post
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

'Yansanda Sun Kama Barayin Shanu 7 A Jigawa

LABARAI MASU NASABA

Sowore Ya Sha Alwashin Ci Gaba Da Gwagwarmaya Duk Da Tsare Shi A Gidan Yarin Kuje

Jagoran Matasan AAC Kwamret Yahaya Soje Ya Nemi A Saki Sowore

June 26, 2026
Har Yanzu Ba Mu Karɓi Kuɗaɗen Da Aka Ware Mana Na Zaɓukan 2027 Ba – INEC

Har Yanzu Ba Mu Karɓi Kuɗaɗen Da Aka Ware Mana Na Zaɓukan 2027 Ba – INEC

June 26, 2026
Husaini Isa Ya Gargaɗi Ƴan Takarar NDC A Kano Kan Buƙatar Kiyaye Ƙa’dojin Jam’iyya

Husaini Isa Ya Gargaɗi Ƴan Takarar NDC A Kano Kan Buƙatar Kiyaye Ƙa’dojin Jam’iyya

June 26, 2026
Noma

Ƙa’idojin Gudanar Da Biyan Kuɗi Nan Take Domin Kare Kai Daga Zamba

June 26, 2026
Darussan Da Suka Fi Dacewa A Fahimta Daga Alkur’ani A Wannan Zamanin (2)

Falalar Yawaita Tuba Ga Ubangiji (Istigfari)

June 26, 2026
Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincike Kan Mutuwar Ɗaliba A Wata Sakandiren Kano

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincike Kan Mutuwar Ɗaliba A Wata Sakandiren Kano

June 26, 2026
Birtaniya Da Nijeriya Sun Ƙulla Yarjejeniya Kan Yaƙi Da Ta’addanci

Birtaniya Da Nijeriya Sun Ƙulla Yarjejeniya Kan Yaƙi Da Ta’addanci

June 26, 2026
Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

ACF Ta Ƙaddamar Da Gidauniyar Tallafa Wa Ilimi A Arewa

June 26, 2026
Damunar Bana: Yadda Gwamnati Da Manoma Ke Tunkarar Barazanar Ƴan Ta’adda

Damunar Bana: Yadda Gwamnati Da Manoma Ke Tunkarar Barazanar Ƴan Ta’adda

June 26, 2026
Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

June 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.