ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Gombe Ya Aza Tubalin Gina Majalisar Dokoki Da Babbar Kotun Jiha Na Zamani

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Gombe

Gwamna Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya aza tubalin gina katafaren ginin Majalisar Dokoki da Babbar Kotun Jiha a wani bangare na gina cibiyoyin rukunan gwamnati 3 wanda zai kunshi bangaren zartarwa, da sashin majalisa da kuma na shari’a.

Da yake jawabi a wajen taron, Gwamna Inuwa ya bayyana kudirin gwamnatinsa na samar da kyakkyawan yanayin aiki ga dukkan bangarorin gwamnati, don ba su damar gudanar da aiki yadda ya kamata.

  • Dikko Radda Ya Bai Wa Gwarazan Hikayata Kyautar Kudi
  • Ruguza Tsohon Tsari Na Duniya Zai Haifar Da Ci Gaban Afirka

Gwamnan ya bayyana cewa an ba da kwangilar gina babbar kotun jihar ne kan kudi naira biliyan 14 da miliyan 900, yayin da ginin majalisar zai lakume naira biliyan 14. da miliyan 5.

ADVERTISEMENT

Ya yi amfani da wannar dama wajen bayyana aniyarsa ta maida tsohuwar Majalisar Dokoki da Babbar Kotun jihar zuwa asibiti da kwalejin ‘yan mata, don amfanin al’ummar yankin da kewaye.

Da yake bayyana aikin a matsayin wani matakin da ba a taba ganin irinsa ba na cike gibin ababen more rayuwa, Inuwa ya ce, “Tun da aka kirkiro ta shekaru 28 da suka gabata, Jihar Gombe ba ta taba ganin irin wannan aiki ba don samar da yanayin aiki da ya dace ga shugabanni da ma’aikatan gwamnati a jihar.

LABARAI MASU NASABA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

“Ta hanyar samar musu da wuraren aiki na zamani kamar ko’ina a duniya, muna kara tabbatar da aniya da jajircewarmu na karfafa tsarin gudanar da mulki da ke tabbatar da dimokuradiyya da ci gaban al’umma.

“Tare da wadannan ayyuka, muna fatan bude wani sabon babi da zai kara karfafa alaka da bai wa kowane rukunin gwamnati damar gudanar da ayyukansa yadda ya kamata.

“Wadannan ayyuka ba kawai gine-gine ne na zahiri ba, ginshiki ne na samun ci gaba mai dorewa, inda jagoranci da dimokuradiyya za su karfafa, kuma kowane dan kasa ya samu damar ci gaba yadda ya kamata,” in ji shi.

Gwamnan ya yaba da kyakkyawar alakar aiki da ke tsakanin bangaren zartaswa da sauran bangarorin gwamnati, wanda ya ce ya taimaka wajen cimma nasarorin da gwamnatin mai ci take samu.

Shi ma kwararren mai sanya ido kan aikin daga kamfanin Artec Practice Limited, Arc. Oni Oluseyi, ya ce aikin babbar kotun jihar gini ne na zamani wadda ya kunshi dakunan shari’a 12 masu iya daukar mutane 60, da dakin taro, da ofisoshin alkalai da sauran manyan jami’an shari’a, da dakin karatu na zamani (E-library) da kuma dakin ganawa da manema labarai da dai sauran wurare.

Dangane da ginin majalisar dokokin jihar kuwa, kwararren ya ce an tsara ginin ne zuwa bangarori biyu da suka kunshi zauren majalisa, da ofisoshin kakakin majalisa, da na mataimakinsa da sauran mambobin majalisar, da dakin karatu, da na taro, da wuraren liyafa da dakunan taro, da asibiti da zauren ganawa da manema labarai da dai sauransu.

Manajojin Daraktocin kamfanonin gine-ginen da aka bai wa kwangilolin, Kamfanin Datum Construction, Daher Kaworma da takwaransa na Kamfanin GMC George Maroum, sun tabbatarwa gwamna da al’ummar jihar cewa za su gudanar da ayyuka masu inganci da nagarta.

Gombe
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Zaɓen Fidda Gwani Na Gwamna: Ba Za Mu Lamunci Kaƙaba Mana Ɗan Takara A Bauchi Ba – Mambobin APC
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Sanata Buba Ya Janye Daga Takarar Fidda Gwani Ta Gwamnan APC A Bauchi, Ya Zargi Cewa ‘Ɗauki Ɗaura Ake Yi Ba Zaɓe Ba”

MASU ALAKA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna
Labarai

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Next Post
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

'Yansanda Sun Kama Barayin Shanu 7 A Jigawa

LABARAI MASU NASABA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.