• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gombe Da Gidauniyar ‘Bill & Melinda Gates’ Sun Hada Gwiwa Don Bunkasa Kiwon Lafiya Da Noma

by Khalid Idris Doya
11 months ago
gombe

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

Gwamnatin Jihar Gombe da Gidauniyar ‘Bill and Melinda Gates’ (BMGF) sun jaddada aniyarsu ta samar da hadin gwiwa mai karfi da samar da muhimman dabaru don inganta bangarorin kiwon lafiya da noma.

An cimma wannar matsaya ce yayin wata muhimmiyar ganawa tsakanin Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya da tawagar gidauniyar ta BMGF, karkashin jagorancin Manajanta na Nijeriya, Mista Uche Amaonwu, a masaukin Gwamnan Gombe da ke Abuja.

  • Trump Ya Gayyaci Mark Zuckerberg Cin Abinci
  • Me Ya Sa Lee Hsien Loong Yake Da Karfin Gwiwa Kan Makomar Kasar Sin?

A yayin taron, Mista Amaonwu ya yaba wa Gwamna Inuwa bisa irin nasarorin da gwamnatinsa ta samu a fannonin kiwon lafiya, da ilimi, da sauransu, inda ya ce Jihar Gombe ta yi fice bisa tsare-tsarenta na kiwon lafiya masu inganci da nagarta.

Ya jaddada cewa an zabi Jihar Gombe a sabon shirin hadin gwiwa na gidauniyar ne saboda nagartattun tsare-tsarenta na kula da lafiya.

Ya kuma bayyana fatan cewa sabunta hadin gwiwar zai kara habaka ci gaba a fannin kiwon lafiya da bunkasa noma tare da samar da ingantacciyar rayuwa ga al’ummar Jihar Gombe.

A nasa jawabin, Gwamna Inuwa ya bayyana wasu nasarorin da gwamnatinsa ta samu tun hawansa karagar mulki, inda ya bayyana cewa Jihar Gombe ta tashi daga mataki na kuran baya a fagen ci gaba zuwa mataki na gaba a fannonin tattalin arziki da zamantakewa.

Gwamnan ya jaddada fifikon da gwamnatinsa take bai wa fannin kiwon lafiya, ilimi, noma, da gina al’umma, wadanda duk suke da muhimmanci wajen samun ci gaba mai dorewa.

A bangaren kiwon lafiya, Gwamna Inuwa ya yi karin bayani kan wasu nasarorin da ya samu, ciki har da tabbatar da cewa dukkan gundumomi 114 da ke jihar suna da akalla cibiyar kiwon lafiya daya a matakin farko da kuma kafa hukumar taimakekeniyar lafiya ta Jihar Gombe (GoHealth), wacce ta dauki masu rauni da ke cin gajiyar jinya su fiye da 340,000.

Sauran nasarorin a cewarsa, sun hada da kafa hukumar kula da asibitoci don inganta harkokin kiwon lafiya, da gina sabin manya da kananan asibitoci a fadin jihar da daukar ma’aikatan lafiya aiki don magance gibin ma’aikata a fannin da dai sauransu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta
Manyan Labarai

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

October 9, 2025
Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin
Manyan Labarai

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

October 9, 2025
Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu
Siyasa

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
Next Post
Gwamnan Gombe Ya Aza Tubalin Gina Majalisar Dokoki Da Babbar Kotun Jiha Na Zamani

Gwamnan Gombe Ya Aza Tubalin Gina Majalisar Dokoki Da Babbar Kotun Jiha Na Zamani

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

October 9, 2025
Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

October 9, 2025
Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

October 9, 2025
Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.