ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, November 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Za Ta Fafata Da Afirka Ta Kudu

by Abba Ibrahim Wada
2 years ago
Kofin duniya

Tawagar Super Eagles ta Nijeriya za ta fafata da Afirka ta Kudu da Benin da Rwanda da Zimbabwe da kuma Lesotho a wasannin rukuni na uku na gasar cin kofin duniya da za’a yi a shekara ta 2026.

A ranar Alhamis ne aka gudanar da bikin fitar da jadawalin wasannin a birnin Abidjan na kasar Ibory Coast wadda ita ce za ta karbi bakuncin gasar cin kofin nahiyar Afirka a shekara mai zuwa.

  • Matan Nijeriya Sun Buga Canjaras Da Kasar Canada A Wasan Farko Na Gasar Cin Kofin Duniya
  1. Sau 14 dai kasashen Nijeriya da Afirka ta Kudu suka fafata tsakanin su, inda Super Eagles ta yi nasara sau bakwai sannan suka yi canjaras biyu kuma karo na karshe da Nijeriya ta kara da Afirka Ta Kudun a wasan neman tikitin shiga gasar cin kofin duniya shi ne kafin gasar 2010.

Super Eagles ta samu nasara a wasanni biyu da suka fafata, amma Afirka ta Kudu ta samu gurbin shiga gasar la’akari da matsayin mai masaukin baki kamar yadda hukumar kwallon kafa ta duniya ta tsara.

ADVERTISEMENT

Kasar Senegal, zakarun Afirka, na rukunin na biyu ne tare da Jamhuriyar Dimokaradiyyar Kongo da Togo da Mauritania da Sudan da kuma Sudan ta Kudu.

Sai Kasar Morroco, wadda ta kai wasan dab da karshe a gasar kofin duniya da aka buga a Katar – ta samu kanta a rukuni na biyar inda za ta kara da Zambia da Tanzania da Congo Brazzabille da Jamhuriyar Nijar da kuma Eritrea.

LABARAI MASU NASABA

Hakimi, Osimhen Da Salah Ƴan Wasan Da Ke Takara A Ƙyautar Gwarzon Afrika

Yadda Za A Magance Yawan Faɗace-faɗace A Wasannin Gasar Firimiyar Nijeriya

Ghana tana rukuni na daya tare da Mali, da Madagascar da Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya, da Comoros da kuma Chadi kuma nan gaba kadan za’a saka ranar fara wasannin.

Cikakken Rukunin:
Rukuni na A: Masar, Burkina Faso, Guinea-Bissau, Saliyo, Ethiopia, da kuma Djibouti.
Rukuni na B: Senegal, Democratic Republic of Congo, Togo, Mauritania, Sudan da kuma Southern Sudan.
Rukuni na C: Nijeriya, Afirka ta Kudu, Benin Republic, Zimbabwe, Rwanda da kuma Lesotho.
Rukuni na D: Kamaru, Cape Berde, Angola, Libya, Eswatini da kuma Mauritius
Rukuni na E: Morroco, Zambia, Tanzania, Congo Brazzabille, Nijar da Eritrea.
Rukuni na F: Ibory Coast, Gabon, Kenya, Gambia, Burundi, da kuma Seychelles
Rukuni na G: Algeria, Guinea, Uganda, Mozambikue, Botswana, Somalia
Rukuni na H: Tunisia, Ekuatorial Guinea, Namibia, Malawi, Liberia, Sao Tome e Principe.
Rukuni na I: Ghana, Mali, Madagascar, the Central African Republic, Comoros da Chad. Za’a fara buga wasannin daga ranar 3 ga watan Nuwamban wannan shekarar
ta 2023, zuwa ranar 18 ga watan Nuwamban 2025 kuma kasashen Afirka na da gurbi tara, bayan da aka kara adadin kasashen da za su shiga gasar da za’a buga a shekarar 2026 zuwa 48.

Za dai a buga gasar a kasashen Amurka da Medico da kuma Canada daga ranar 11 ga watan Yuni zuwa 19 ga watan Yulin 2026, kasar Argentina ce dai ke rike da kofin gasar da ta dauka a shekarar 2022 da aka buga a Katar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Hakimi, Osimhen Da Salah Ƴan Wasan Da Ke Takara A Ƙyautar Gwarzon Afrika
Wasanni

Hakimi, Osimhen Da Salah Ƴan Wasan Da Ke Takara A Ƙyautar Gwarzon Afrika

November 17, 2025
Yadda Za A Magance Yawan Faɗace-faɗace A Wasannin Gasar Firimiyar Nijeriya
Nazari

Yadda Za A Magance Yawan Faɗace-faɗace A Wasannin Gasar Firimiyar Nijeriya

November 16, 2025
Hukumar Kwallon Kafa Ta Kasar Turkiyya Ta Dakatar Da ‘Yan Wasa 1024 Saboda Laifin Caca
Wasanni

Hukumar Kwallon Kafa Ta Kasar Turkiyya Ta Dakatar Da ‘Yan Wasa 1024 Saboda Laifin Caca

November 15, 2025
Next Post
An Bude Dandalin CMG Karo Na 2 A Shanghai

An Bude Dandalin CMG Karo Na 2 A Shanghai

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Sin Ba Ta Taba Bukatar Kamfanoni Su Tattara Ko Adana Bayanai Ba Bisa Ka’ida Ba Kuma Ba Za Ta Yi Hakan Ba 

Gwamnatin Sin Ba Ta Taba Bukatar Kamfanoni Su Tattara Ko Adana Bayanai Ba Bisa Ka’ida Ba Kuma Ba Za Ta Yi Hakan Ba 

November 17, 2025
Adadin Motocin Da Sin Ke Fitarwa Waje Ya Karu Da Kashi 15.7 Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana

Adadin Motocin Da Sin Ke Fitarwa Waje Ya Karu Da Kashi 15.7 Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana

November 17, 2025
Farashin Kayan Abinci Na Cigaba Da Sauka A Jihohin Arewa Maso Gabas

Farashin Kayan Abinci Na Cigaba Da Sauka A Jihohin Arewa Maso Gabas

November 17, 2025
An Bude Taron Tattaunawa Kan Wayewar Kai Tsakanin Sin Da Kasashen Larabawa Karo Na 11 A Beijing

An Bude Taron Tattaunawa Kan Wayewar Kai Tsakanin Sin Da Kasashen Larabawa Karo Na 11 A Beijing

November 17, 2025
NBS

Hauhawar Farashin Kayayyaki A Nijeriya Ta Ragu Zuwa Kashi 16.065%

November 17, 2025
Firaministan Sin Ya Isa Rasha Domin Halartar Taron SCO

Firaministan Sin Ya Isa Rasha Domin Halartar Taron SCO

November 17, 2025
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

November 17, 2025
Kudaden Kasafin Kudin Sin Sun Karu Da Kashi 0.8 Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana

Kudaden Kasafin Kudin Sin Sun Karu Da Kashi 0.8 Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana

November 17, 2025
Rashin Tsaro: Atiku Ya Yi Allah-wadai Da Harin Makarantar ‘Yan Mata Ta Kebbi

Rashin Tsaro: Atiku Ya Yi Allah-wadai Da Harin Makarantar ‘Yan Mata Ta Kebbi

November 17, 2025
An Sanya Hannu Kan Yarjejeniyoyin Cinikayya Na Biliyoyin Kudi Yayin Baje Kolin CHTF Na Kasar Sin

An Sanya Hannu Kan Yarjejeniyoyin Cinikayya Na Biliyoyin Kudi Yayin Baje Kolin CHTF Na Kasar Sin

November 17, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.