ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Za Ta Fafata Da Afirka Ta Kudu

by Abba Ibrahim Wada
3 years ago
Kofin duniya

Tawagar Super Eagles ta Nijeriya za ta fafata da Afirka ta Kudu da Benin da Rwanda da Zimbabwe da kuma Lesotho a wasannin rukuni na uku na gasar cin kofin duniya da za’a yi a shekara ta 2026.

A ranar Alhamis ne aka gudanar da bikin fitar da jadawalin wasannin a birnin Abidjan na kasar Ibory Coast wadda ita ce za ta karbi bakuncin gasar cin kofin nahiyar Afirka a shekara mai zuwa.

  • Matan Nijeriya Sun Buga Canjaras Da Kasar Canada A Wasan Farko Na Gasar Cin Kofin Duniya
  1. Sau 14 dai kasashen Nijeriya da Afirka ta Kudu suka fafata tsakanin su, inda Super Eagles ta yi nasara sau bakwai sannan suka yi canjaras biyu kuma karo na karshe da Nijeriya ta kara da Afirka Ta Kudun a wasan neman tikitin shiga gasar cin kofin duniya shi ne kafin gasar 2010.

Super Eagles ta samu nasara a wasanni biyu da suka fafata, amma Afirka ta Kudu ta samu gurbin shiga gasar la’akari da matsayin mai masaukin baki kamar yadda hukumar kwallon kafa ta duniya ta tsara.

ADVERTISEMENT

Kasar Senegal, zakarun Afirka, na rukunin na biyu ne tare da Jamhuriyar Dimokaradiyyar Kongo da Togo da Mauritania da Sudan da kuma Sudan ta Kudu.

Sai Kasar Morroco, wadda ta kai wasan dab da karshe a gasar kofin duniya da aka buga a Katar – ta samu kanta a rukuni na biyar inda za ta kara da Zambia da Tanzania da Congo Brazzabille da Jamhuriyar Nijar da kuma Eritrea.

LABARAI MASU NASABA

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Lionel Messi Ya Kafa Tarihin Wanda Yafi Kowa Zura Kwallaye A Tarihin Gasar Cin Kofin Duniya

Ghana tana rukuni na daya tare da Mali, da Madagascar da Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya, da Comoros da kuma Chadi kuma nan gaba kadan za’a saka ranar fara wasannin.

Cikakken Rukunin:
Rukuni na A: Masar, Burkina Faso, Guinea-Bissau, Saliyo, Ethiopia, da kuma Djibouti.
Rukuni na B: Senegal, Democratic Republic of Congo, Togo, Mauritania, Sudan da kuma Southern Sudan.
Rukuni na C: Nijeriya, Afirka ta Kudu, Benin Republic, Zimbabwe, Rwanda da kuma Lesotho.
Rukuni na D: Kamaru, Cape Berde, Angola, Libya, Eswatini da kuma Mauritius
Rukuni na E: Morroco, Zambia, Tanzania, Congo Brazzabille, Nijar da Eritrea.
Rukuni na F: Ibory Coast, Gabon, Kenya, Gambia, Burundi, da kuma Seychelles
Rukuni na G: Algeria, Guinea, Uganda, Mozambikue, Botswana, Somalia
Rukuni na H: Tunisia, Ekuatorial Guinea, Namibia, Malawi, Liberia, Sao Tome e Principe.
Rukuni na I: Ghana, Mali, Madagascar, the Central African Republic, Comoros da Chad. Za’a fara buga wasannin daga ranar 3 ga watan Nuwamban wannan shekarar
ta 2023, zuwa ranar 18 ga watan Nuwamban 2025 kuma kasashen Afirka na da gurbi tara, bayan da aka kara adadin kasashen da za su shiga gasar da za’a buga a shekarar 2026 zuwa 48.

Za dai a buga gasar a kasashen Amurka da Medico da kuma Canada daga ranar 11 ga watan Yuni zuwa 19 ga watan Yulin 2026, kasar Argentina ce dai ke rike da kofin gasar da ta dauka a shekarar 2022 da aka buga a Katar.

Kofin duniya
Abba Ibrahim Wada
Website |  + postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada
  • Abba Ibrahim Wada
    FIFA Za Ta Biya Omar Artan Alawus Ɗin Da Za A Bai Wa Kowanne Alƙalin Wasa
  • Abba Ibrahim Wada
    Duk Da Rashin Halartar ‘Super Eagles’ Gasar Kofin Duniya, Nijeriya Ba Ta Rasa Wakilai Ba
  • Abba Ibrahim Wada
    Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

MASU ALAKA

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino
Wasanni

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
Lionel Messi Ya Kafa Tarihin Wanda Yafi Kowa Zura Kwallaye A Tarihin Gasar Cin Kofin Duniya
Wasanni

Lionel Messi Ya Kafa Tarihin Wanda Yafi Kowa Zura Kwallaye A Tarihin Gasar Cin Kofin Duniya

June 22, 2026
Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada
Wasanni

Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada

June 21, 2026
Next Post
An Bude Dandalin CMG Karo Na 2 A Shanghai

An Bude Dandalin CMG Karo Na 2 A Shanghai

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.