• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwaman Bauchi Ya Karya Farashin Taki Zuwa ₦20,000

by Abubakar Sulaiman
1 year ago
in Siyasa
0
Gwaman Bauchi Ya Karya Farashin Taki Zuwa ₦20,000
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan jihar Bauchi, Bala Muhammad a ranar Asabar ya ƙaddamar da fara sayar da takin zamani na daminar bana kan farashi mai rahusa da nufin bunƙasa harƙoƙin noma a jihar. 

Da ya ke jawabi a wajen ƙaddamar da daminar bana da fara sayar da takin zamani a farashi mai rahusa da ya gudana a ƙaramar hukumar Dass, gwamna Bala ya ce, gwamnatin jihar ta sanar da Naira dubu ₦20,000 a matsayin kuɗin buhun takin zamani NPK guda.

Kazalika, gwamnan ya kuma ƙaddamar da sabbin Tiraktocin noma guda 60, sabbin Injunan noma domin ƙarfafa wa noman zamani, ƙari kan shirin tallafin kuɗi na dalar Amurka 25,000 ga zaɓaɓɓen ƙungiyoyin manoma a faɗin jihar.

  • An Ɗage Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Bauchi
  • Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Rattaba Hannu Kan Dokar Da Ta Shafi Yankin Xizang 

Muhammad ya ce a bisa ƙoƙarin da suke yi kan shirye-shiryen da suka shafi noma, gwamnatinsa ta shirya samar da wasu ƙarin kayayyakin noma da ɗaukan malaman gona domin inganta samun amfanin gona.

Gwamna Bala ya kuma nuna aniyarsa ta ilmantar da manoma da dabaru da hanyoyin amfani da sabbin na’urorin noma na zamani. Ya kuma ba da tabbacin cewa, za su yi duk mai yiyuwa wajen tabbatar da tsaro ga manoma domin ba su ƙwarin gwuiwar shiga gonaki domin noma ba tare da fargaba ko razani ba.

Labarai Masu Nasaba

Kotu Ta Yi Watsi Da Ƙarar Da Aka Shigar Da Tinubu Kan Sanya Dokar Ta-Ɓaci A Ribas

Jam’iyyar PDP Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni A Kwara

Ya nanata cewa gwamnatinsa ta ɗauki harƙar noma a matsayin abu mai muhimmanci lura da yadda yawancin ‘yan jihar suka kasance manoma.

Da ya ke jinjina wa gwamnatin tarayya da shirin inganta muhalli na bankin duniya wato ACReSAL da sauran abokan haɗaka, Gwamnan ya sha alwashin ci-gaba da shiga lunguna da saƙo domin nemo tallafi ga manoman da suke jiharsa.

Kan ɗumamar yanayi, gwamnan ya ce, za su shuka ire-iren shukoki daban-daban bisa shawarorin kwararru domin kyautata tattalin arziki.

Bauchi

Kan hakan, gwamnan ya yi gargaɗin cewa, duk wani mutum ko gungun mutane da aka samu da sayar da takin gwamnati kan farashi fiye da wanda ya sanar, to lallai mutum zai ɗanɗana kuɗarsa.

Tun da farko, Kwamishinan Ma’aikatar gona na jihar Bauchi, Farfesa Simom Madugu Yelams, ya ce, ma’aikatarsa ta ɗauki dabarbarun da suka dace wajen ganin noma da suke sassan jihar lungu da saƙo sun samu zarafin sayen takin ba tare da shan wahalhalun ba.

Shugaban riƙo na ƙaramar hukumar Dass, Muhammad Jibo, ya yaba wa gwamnan Bala Muhammad kan shirye-shiryensa na bunƙasa harkokin noma a faɗin jihar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BauchiFertilizerGwamna Bala Muhammad
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Katsina Za Ta Shirya Jarrabawa Ga Ma’aikata

Next Post

Wakilin Sin Ya Yi Kira Da A Tallafa Wa Kasashen Dake Yammacin Afirka Da Yankin Sahel Domin Lalubo Hanyoyin Samun Ci Gaba Da Suka Dace Da Yanayin Su

Related

Kotu Ta Yi Watsi Da Ƙarar Da Aka Shigar Da Tinubu Kan Sanya Dokar Ta-Ɓaci A Ribas
Labarai

Kotu Ta Yi Watsi Da Ƙarar Da Aka Shigar Da Tinubu Kan Sanya Dokar Ta-Ɓaci A Ribas

3 days ago
Jam’iyyar PDP Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni A Kwara
Siyasa

Jam’iyyar PDP Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni A Kwara

7 days ago
Tinubu Zai Gana Da Manyan Ƴan Kasuwa, Zai Ƙaddamar Da Muhimman Aiyuka A Legas
Siyasa

Tinubu Zai Gana Da Manyan Ƴan Kasuwa, Zai Ƙaddamar Da Muhimman Aiyuka A Legas

1 week ago
Manyan Ƴan Siyasa Sun Yi Watsi Da Kafa Sabuwar Jam’iyyar ADA Sun Rungumi ADC
Siyasa

Manyan Ƴan Siyasa Sun Yi Watsi Da Kafa Sabuwar Jam’iyyar ADA Sun Rungumi ADC

1 week ago
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Siyasa

Wa’adin Mulki Ɗaya Kacal Za Ka Yi — ADC Ga Tinubu

2 weeks ago
Gwamna Kefas Ya Bamu Damar Ƙwatar Mulkin Taraba A 2027 – APC
Labarai

Gwamna Kefas Ya Bamu Damar Ƙwatar Mulkin Taraba A 2027 – APC

2 weeks ago
Next Post
Wakilin Sin Ya Yi Kira Da A Tallafa Wa Kasashen Dake Yammacin Afirka Da Yankin Sahel Domin Lalubo Hanyoyin Samun Ci Gaba Da Suka Dace Da Yanayin Su

Wakilin Sin Ya Yi Kira Da A Tallafa Wa Kasashen Dake Yammacin Afirka Da Yankin Sahel Domin Lalubo Hanyoyin Samun Ci Gaba Da Suka Dace Da Yanayin Su

LABARAI MASU NASABA

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

October 4, 2025
Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

October 4, 2025
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.