• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwaman Bauchi Ya Karya Farashin Taki Zuwa ₦20,000

by Abubakar Sulaiman
11 months ago
in Siyasa
0
Gwaman Bauchi Ya Karya Farashin Taki Zuwa ₦20,000
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan jihar Bauchi, Bala Muhammad a ranar Asabar ya ƙaddamar da fara sayar da takin zamani na daminar bana kan farashi mai rahusa da nufin bunƙasa harƙoƙin noma a jihar. 

Da ya ke jawabi a wajen ƙaddamar da daminar bana da fara sayar da takin zamani a farashi mai rahusa da ya gudana a ƙaramar hukumar Dass, gwamna Bala ya ce, gwamnatin jihar ta sanar da Naira dubu ₦20,000 a matsayin kuɗin buhun takin zamani NPK guda.

Kazalika, gwamnan ya kuma ƙaddamar da sabbin Tiraktocin noma guda 60, sabbin Injunan noma domin ƙarfafa wa noman zamani, ƙari kan shirin tallafin kuɗi na dalar Amurka 25,000 ga zaɓaɓɓen ƙungiyoyin manoma a faɗin jihar.

  • An Ɗage Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Bauchi
  • Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Rattaba Hannu Kan Dokar Da Ta Shafi Yankin Xizang 

Muhammad ya ce a bisa ƙoƙarin da suke yi kan shirye-shiryen da suka shafi noma, gwamnatinsa ta shirya samar da wasu ƙarin kayayyakin noma da ɗaukan malaman gona domin inganta samun amfanin gona.

Gwamna Bala ya kuma nuna aniyarsa ta ilmantar da manoma da dabaru da hanyoyin amfani da sabbin na’urorin noma na zamani. Ya kuma ba da tabbacin cewa, za su yi duk mai yiyuwa wajen tabbatar da tsaro ga manoma domin ba su ƙwarin gwuiwar shiga gonaki domin noma ba tare da fargaba ko razani ba.

Labarai Masu Nasaba

Shehu Sani Ya Buƙaci Shugabannin Arewa Su Mara Wa Tinubu Baya Ya Yi Shekaru 8 A Kan Mulki

Babu Wanda Zai Iya Kora Ta Daga PDP —  Wike

Ya nanata cewa gwamnatinsa ta ɗauki harƙar noma a matsayin abu mai muhimmanci lura da yadda yawancin ‘yan jihar suka kasance manoma.

Da ya ke jinjina wa gwamnatin tarayya da shirin inganta muhalli na bankin duniya wato ACReSAL da sauran abokan haɗaka, Gwamnan ya sha alwashin ci-gaba da shiga lunguna da saƙo domin nemo tallafi ga manoman da suke jiharsa.

Kan ɗumamar yanayi, gwamnan ya ce, za su shuka ire-iren shukoki daban-daban bisa shawarorin kwararru domin kyautata tattalin arziki.

Bauchi

Kan hakan, gwamnan ya yi gargaɗin cewa, duk wani mutum ko gungun mutane da aka samu da sayar da takin gwamnati kan farashi fiye da wanda ya sanar, to lallai mutum zai ɗanɗana kuɗarsa.

Tun da farko, Kwamishinan Ma’aikatar gona na jihar Bauchi, Farfesa Simom Madugu Yelams, ya ce, ma’aikatarsa ta ɗauki dabarbarun da suka dace wajen ganin noma da suke sassan jihar lungu da saƙo sun samu zarafin sayen takin ba tare da shan wahalhalun ba.

Shugaban riƙo na ƙaramar hukumar Dass, Muhammad Jibo, ya yaba wa gwamnan Bala Muhammad kan shirye-shiryensa na bunƙasa harkokin noma a faɗin jihar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BauchiFertilizerGwamna Bala Muhammad
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Katsina Za Ta Shirya Jarrabawa Ga Ma’aikata

Next Post

Wakilin Sin Ya Yi Kira Da A Tallafa Wa Kasashen Dake Yammacin Afirka Da Yankin Sahel Domin Lalubo Hanyoyin Samun Ci Gaba Da Suka Dace Da Yanayin Su

Related

Shehu Sani Ya Buƙaci Shugabannin Arewa Su Mara Wa Tinubu Baya Ya Yi Shekaru 8 A Kan Mulki
Manyan Labarai

Shehu Sani Ya Buƙaci Shugabannin Arewa Su Mara Wa Tinubu Baya Ya Yi Shekaru 8 A Kan Mulki

4 days ago
Babu Wanda Zai Iya Kora Ta Daga PDP —  Wike
Siyasa

Babu Wanda Zai Iya Kora Ta Daga PDP —  Wike

5 days ago
Sulhun PDP Ya Haɗu Da Cikas, Wike Ya Janye Daga Duk Wata Yarjejeniya
Siyasa

Sulhun PDP Ya Haɗu Da Cikas, Wike Ya Janye Daga Duk Wata Yarjejeniya

1 week ago
‘Aikin Yan Uba Ne’ — Yahaya Bello Ya Karyata Zargin Sha’awar Takarar Shugaban Kasa A 2027
Siyasa

‘Aikin Yan Uba Ne’ — Yahaya Bello Ya Karyata Zargin Sha’awar Takarar Shugaban Kasa A 2027

2 weeks ago
Sanata Adamu Aliero Ya Ƙaddamar Da Rabon Kayan Tallafi Ga Ƙananan Hukumomi Takwas A Kebbi
Labarai

Sanata Adamu Aliero Ya Ƙaddamar Da Rabon Kayan Tallafi Ga Ƙananan Hukumomi Takwas A Kebbi

2 weeks ago
PDP Ta Sake Zaɓar Amb. El-Gash A Yobe
Siyasa

PDP Ta Sake Zaɓar Amb. El-Gash A Yobe

3 weeks ago
Next Post
Wakilin Sin Ya Yi Kira Da A Tallafa Wa Kasashen Dake Yammacin Afirka Da Yankin Sahel Domin Lalubo Hanyoyin Samun Ci Gaba Da Suka Dace Da Yanayin Su

Wakilin Sin Ya Yi Kira Da A Tallafa Wa Kasashen Dake Yammacin Afirka Da Yankin Sahel Domin Lalubo Hanyoyin Samun Ci Gaba Da Suka Dace Da Yanayin Su

LABARAI MASU NASABA

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.