ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, November 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwaman Bauchi Ya Karya Farashin Taki Zuwa ₦20,000

by Abubakar Sulaiman
1 year ago
Bauchi

Gwamnan jihar Bauchi, Bala Muhammad a ranar Asabar ya ƙaddamar da fara sayar da takin zamani na daminar bana kan farashi mai rahusa da nufin bunƙasa harƙoƙin noma a jihar. 

Da ya ke jawabi a wajen ƙaddamar da daminar bana da fara sayar da takin zamani a farashi mai rahusa da ya gudana a ƙaramar hukumar Dass, gwamna Bala ya ce, gwamnatin jihar ta sanar da Naira dubu ₦20,000 a matsayin kuɗin buhun takin zamani NPK guda.

Kazalika, gwamnan ya kuma ƙaddamar da sabbin Tiraktocin noma guda 60, sabbin Injunan noma domin ƙarfafa wa noman zamani, ƙari kan shirin tallafin kuɗi na dalar Amurka 25,000 ga zaɓaɓɓen ƙungiyoyin manoma a faɗin jihar.

ADVERTISEMENT
  • An Ɗage Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Bauchi
  • Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Rattaba Hannu Kan Dokar Da Ta Shafi Yankin Xizang 

Muhammad ya ce a bisa ƙoƙarin da suke yi kan shirye-shiryen da suka shafi noma, gwamnatinsa ta shirya samar da wasu ƙarin kayayyakin noma da ɗaukan malaman gona domin inganta samun amfanin gona.

Gwamna Bala ya kuma nuna aniyarsa ta ilmantar da manoma da dabaru da hanyoyin amfani da sabbin na’urorin noma na zamani. Ya kuma ba da tabbacin cewa, za su yi duk mai yiyuwa wajen tabbatar da tsaro ga manoma domin ba su ƙwarin gwuiwar shiga gonaki domin noma ba tare da fargaba ko razani ba.

LABARAI MASU NASABA

Sanusi II Kaɗai Muka Sani A Matsayin Halataccen Sarkin Kano – Kwankwaso

Wakilai Daga Jihohi 19 Sun Isa Ibadan Don Taron PDP Na Ƙasa

Ya nanata cewa gwamnatinsa ta ɗauki harƙar noma a matsayin abu mai muhimmanci lura da yadda yawancin ‘yan jihar suka kasance manoma.

Da ya ke jinjina wa gwamnatin tarayya da shirin inganta muhalli na bankin duniya wato ACReSAL da sauran abokan haɗaka, Gwamnan ya sha alwashin ci-gaba da shiga lunguna da saƙo domin nemo tallafi ga manoman da suke jiharsa.

Kan ɗumamar yanayi, gwamnan ya ce, za su shuka ire-iren shukoki daban-daban bisa shawarorin kwararru domin kyautata tattalin arziki.

Bauchi

Kan hakan, gwamnan ya yi gargaɗin cewa, duk wani mutum ko gungun mutane da aka samu da sayar da takin gwamnati kan farashi fiye da wanda ya sanar, to lallai mutum zai ɗanɗana kuɗarsa.

Tun da farko, Kwamishinan Ma’aikatar gona na jihar Bauchi, Farfesa Simom Madugu Yelams, ya ce, ma’aikatarsa ta ɗauki dabarbarun da suka dace wajen ganin noma da suke sassan jihar lungu da saƙo sun samu zarafin sayen takin ba tare da shan wahalhalun ba.

Shugaban riƙo na ƙaramar hukumar Dass, Muhammad Jibo, ya yaba wa gwamnan Bala Muhammad kan shirye-shiryensa na bunƙasa harkokin noma a faɗin jihar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Yanzu Satar Da Kuka Yi Ba Ta Da Amfani: Kwankwaso Ga Gwamnonin APC
Manyan Labarai

Sanusi II Kaɗai Muka Sani A Matsayin Halataccen Sarkin Kano – Kwankwaso

November 15, 2025
Wakilai Daga Jihohi 19 Sun Isa Ibadan Don Taron PDP Na Ƙasa
Siyasa

Wakilai Daga Jihohi 19 Sun Isa Ibadan Don Taron PDP Na Ƙasa

November 15, 2025
Injiniya Sagir Ibrahim Ƙoƙi Ya Fice Daga Jam’iyyar NNPP
Siyasa

Injiniya Sagir Ibrahim Ƙoƙi Ya Fice Daga Jam’iyyar NNPP

November 12, 2025
Next Post
Wakilin Sin Ya Yi Kira Da A Tallafa Wa Kasashen Dake Yammacin Afirka Da Yankin Sahel Domin Lalubo Hanyoyin Samun Ci Gaba Da Suka Dace Da Yanayin Su

Wakilin Sin Ya Yi Kira Da A Tallafa Wa Kasashen Dake Yammacin Afirka Da Yankin Sahel Domin Lalubo Hanyoyin Samun Ci Gaba Da Suka Dace Da Yanayin Su

LABARAI MASU NASABA

Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN Sun Shaida Adawar Sassan Kasa da Kasa Da Burin Masu Tsattsauran Ra’ayi Na Japan Na Ruguza Odar Kasa Da Kasa Ta Bayan Yakin Duniya Na 2 Dangane Da Batun Taiwan

Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN Sun Shaida Adawar Sassan Kasa da Kasa Da Burin Masu Tsattsauran Ra’ayi Na Japan Na Ruguza Odar Kasa Da Kasa Ta Bayan Yakin Duniya Na 2 Dangane Da Batun Taiwan

November 15, 2025
Hukumar Kwallon Kafa Ta Kasar Turkiyya Ta Dakatar Da ‘Yan Wasa 1024 Saboda Laifin Caca

Hukumar Kwallon Kafa Ta Kasar Turkiyya Ta Dakatar Da ‘Yan Wasa 1024 Saboda Laifin Caca

November 15, 2025
Sin Ta Bayyana Damuwa Dangane Da Matakin Amurka Na Ingiza Daftarin Tsawaita Aikin Tawagar UNISFA 

Sin Ta Bayyana Damuwa Dangane Da Matakin Amurka Na Ingiza Daftarin Tsawaita Aikin Tawagar UNISFA 

November 15, 2025
Za A Yi Gwanjon Rigunan Messi Na Gasar Kofin Duniya Ta 2022 Da Kudi Tsagwagwa

Ina Son Kasancewa Cikin Koshin Lafiya Kafin Buga Gasar Kofin Duniya Na Shekarar 2026 – Messi

November 15, 2025
Za A Wallafa Makalar Xi Game Da Gina Sabbin Ginshikan Samar Da Ci Gaban Kasa Masu Inganci

Za A Wallafa Makalar Xi Game Da Gina Sabbin Ginshikan Samar Da Ci Gaban Kasa Masu Inganci

November 15, 2025
Duk Niyyar Da Mutum Ya Shigo Da Ita Kannywood Ita Za Ta Bi Shi —HAUWA KUJAMA

Duk Niyyar Da Mutum Ya Shigo Da Ita Kannywood Ita Za Ta Bi Shi —HAUWA KUJAMA

November 15, 2025
Sin Ta Sha Alwashin Bunkasa Goyon Bayan Juna Tsakaninta Da Saliyo

Sin Ta Sha Alwashin Bunkasa Goyon Bayan Juna Tsakaninta Da Saliyo

November 15, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7

Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7

November 15, 2025
An Gabatar Da Sabuwar Hanyar Raya Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Tsakanin Sin Da Afirka

An Gabatar Da Sabuwar Hanyar Raya Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Tsakanin Sin Da Afirka

November 15, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Yi Taka-tsantsan Da Batun Yankin Taiwan 

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Yi Taka-tsantsan Da Batun Yankin Taiwan 

November 15, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.