• English
  • Business News
Monday, August 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamatin Amurka Ta Yi Alkawarin Tallafa Wa Mata ‘Yan Kasuwa A Nijeriya

by Bello Hamza and Sulaiman
11 months ago
in Tattalin Arziki
0
Gwamatin Amurka Ta Yi Alkawarin Tallafa Wa Mata ‘Yan Kasuwa A Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Amurka ta jaddada niyyar ta na tallafa wa ‘yan kasuwa mata a Nijeriya domin kai wa ga babban matakin tattalin arziki, domin samar da daidaito, tsaro da kuma ci gaba ga kowa da kowa.

 

Kasar Amurkan ta ce, wannan tallafin zai zo ne ta hanyar tsangayar ta na Yan Kasuwa mata. Ta bayyana hakan ne a wajen wani taro na kwana uku na tsaffin daliban tsangayar dari da hamsin domin zurfafa ilimin su na fasahar zamani a birnin Legas.

  • Babban Taron Samar Da Kayayyaki Na 2024 Ya Sa Kaimi Ga Kulla Ayyukan Hadin Gwiwa 718
  • Jan Kafar Tinubu Na Cire Harajin Shigo Da Abinci Na Ci Gaba Da Ta’azzara rayuwa

Shirin zai maida hankali ne wajen saita tsaffin daliban a kan gaba a fannin fasahar zamani, domin kawo kirkire-kirkire da kuma cigaba mai dorewa a harkar kasuwancinsu.

 

Labarai Masu Nasaba

NBS Ta Bayyana Dalilin Raguwar Farashin Kaya A Nijeriya

Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci Bunkasa Fannin Mai Da Ake Hakowa A Teku

Da yake magana a wajen taron Consul-General din Amurka a Nijeriya, Mr. Will Stebens, ya ce tsangayar ta yan kasuwa mata ta hada sama da mata 130 cikin 150 din da suka kammala karatu a tsangayar a ‘yan shekarun da suka wuce.

 

“Mun dade muna yin wannan a yan shekarun da suka gabata tun 2019. Wannan shiri wanda gwamnatin Amurka ta dauki nauyi domin koyar da mata masu kananan sana’o’i kuma a taimaka masu wajen inganta kasuwancinsu domin su ci gaba ta hanyar fasahar zamani, noma da kuma tattalin arziki”

 

Mr. Stebens ya kara da cewa; “Zai taimaka masu su hadu da mentors a Amurka a tsangayar kasuwanci na Arizona da kuma mentors masu zaman kansu kasar Amurka da kuma a tsakanin su. Wadannan matan da suka fito daga sassa a Nijeriya suna taimaka ma juna wajen habbaka kasuwancinsu da kuma samar da ayyuka ga yan Nijeriya”

 

Ya kuma kara da cewa abu ne mai matukar karfafawa ganin mata na fuskantar kalubalen kasuwanci da kuma hadin gwiwa da kasar Amurka.

 

Mr. Steben ya kuma ce duk shekara tsangayar tana daukar matan da suka nuna sha’awar shiga makarantar guda 30 zuwa 50 domin su anfana da wannan tsari.

 

Stebens ya kuma bayyana yadda tsarin yake cigaba da taka rawar gani wajen tallafa wa ‘yan kasuwa mata a Nijeriya ta hanyar tallafa masu da muhimman jarin kasuwanci.

 

Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Tallafin Kasar Rasha Don Kammala Kamfanin Mulmula Karafuna Na Ajakuta.

 

Gwamnatin tarayya ta sanya hannu a wata yarjejeniya da masu gina kamfanin mulmula karafuna na Ajakuta, Messrs Tyazhapromedport, domin ingantawa, kammalawa da kuma fara aikin kamfanin mulmula karfe a Nijeriya.

 

Babban ministan harkokin karafuna, Shuaibu Audu, ya sanya hannu a yarjejeniyar a madadin gwamnatin tarayya a birnin Moscow, a wata sanarwa da mai magana da yawun ministan ya fitar, Salamotu Jibaniya a ranar juma’a.

 

Kamar yadda ta bayyana, an sanya hannu a yarjejeniyar ne lokacin da ministan ya jagoranci tawagar Nijeriya zuwa birnin Moscow a kasar Rasha, daga ranar 14 zuwa 21 ga watan Satumba.

 

An samar da Kanfanin na Ajakuta ne a shekarar 1979, domin samar da Metallurgical Process Plant tare da Engineering compled da kuma sauran ayyuka makamantansu.

 

Kamfanin dai ya yi shekaru ba tare da ya sarrafa ko karfe kwara daya ba sakamakon cin hanci da kuma tirka tirkar Shari’a.

 

An samar da kamfanin ne domin samar da ayyukan kamfani mabanbanta da kuma ayyukan tattalin arziki wanda suke da muhimmanci wajen raba kafa a harkar tattalin arzikin Nijeriya zuwa industry.

 

Tun bayan zaman shi minista, ministan ya jaddada wa yan Nijeriya cewa kamfanin karfen zai fara aikin sarrafa karafuna domin kawo karshen shigo da karfe daga kasar waje.

 

Domin tabbatar da wannan buri, kwararrun masana daga Messrs TPE sun ziyarci kanfanin da kuma wajen hako karafuna a garin Irakpe domin fara duba yanayin wajen a watan Agusta, wanda hakan ya yi sanadiyar samun gayyata domin sanya hannu a yarjejeniyar.

 

Kamfanin Nobostal M and Proforce, wanda na karkashin kanfanin Tyazhpromedport’s consortium suma suna cikin yarjejeniyar.

 

A wata sanarwa, wakilan na Nijeriya sun duba kayan aikin Messrs Nobostal M, wanda yake a Balakobo a yankin Saratob a kasar Rasha.

 

Da yake magana dangane da wannan ci gaba, Minista Audu ya ce yarjejeniyar wani babban hanya ne na samar da cigaba mai dorewa a harkar tattalin arzikin Nijeriya.

 

Ya kuma kara da cewa; “Dawo da kanfanin zai rage shigo da karfe Nijeriya wanda ya kai kusan kimanin dala biliyan hudu a duk shekara kuma zai taimaka wajen tattalin kudaden kasar waje”

 

A nashi bangaren, sakataren ministan, Chris Isokpunwu, ya ce Nijeriya a shirye take wajen dawo da kanfanin Ajakuta da kuma NIOMCO.

 

A nashi batun, wakilin kasar Rasha ya jaddada cewa za su yi kokari wajen ganin cewa sun girmama yarjejeniyar daidai da yadda gwamnatin Nijeriya ta bukata.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AjakutaKamfanin karafaRasha
ShareTweetSendShare
Previous Post

Manyan Batutuwan Taron Sanatoci Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya A Kano

Next Post

Tinubu Ya Naɗa Hukumar Gudanarwar Hukumar Raya Yankin Arewa Maso Yamma

Related

NBS Ta Bayyana Dalilin Raguwar Farashin Kaya A Nijeriya
Tattalin Arziki

NBS Ta Bayyana Dalilin Raguwar Farashin Kaya A Nijeriya

3 days ago
Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci Bunkasa Fannin Mai Da Ake Hakowa A Teku
Tattalin Arziki

Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci Bunkasa Fannin Mai Da Ake Hakowa A Teku

3 days ago
Dalilin Da Ya Sa Gwamnatin Jihar Kuros Ribas Ta Yi Hadaka Da Hukumar NPA
Tattalin Arziki

Dalilin Da Ya Sa Gwamnatin Jihar Kuros Ribas Ta Yi Hadaka Da Hukumar NPA

3 days ago
Ma’aikatan Sufurin Jiregen Sama Sun Bukaci Tinubu Ya Janye Shirin Sayar Da Filayen Jiragen Sama
Tattalin Arziki

Ma’aikatan Sufurin Jiregen Sama Sun Bukaci Tinubu Ya Janye Shirin Sayar Da Filayen Jiragen Sama

1 week ago
NPA Ta Fito Da Sabuwar Doka Kan Kayan Da Ake Ajiyewa A Tashoshinta
Tattalin Arziki

NPA Ta Fito Da Sabuwar Doka Kan Kayan Da Ake Ajiyewa A Tashoshinta

1 week ago
Shirin Iskar Gas Na CNG Abin A Yaba Wa Shugaba Tinubu Ne -Shugaban IPMAN Na Ƙasa
Tattalin Arziki

Shirin Iskar Gas Na CNG Abin A Yaba Wa Shugaba Tinubu Ne -Shugaban IPMAN Na Ƙasa

2 weeks ago
Next Post
Tinubu Ya Naɗa Hukumar Gudanarwar Hukumar Raya Yankin Arewa Maso Yamma

Tinubu Ya Naɗa Hukumar Gudanarwar Hukumar Raya Yankin Arewa Maso Yamma

LABARAI MASU NASABA

Ɗaruruwan Mambobin APC Sun Sauya Sheka Zuwa ADC A Sokoto

August 24, 2025
Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

August 24, 2025
Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

August 24, 2025
An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao

An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao

August 24, 2025
CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 

CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 

August 24, 2025
Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

August 24, 2025
An Kaddamar Da Gini Mara Fitar Da Hayakin Carbon Irinsa Na Farko A Duniya

An Kaddamar Da Gini Mara Fitar Da Hayakin Carbon Irinsa Na Farko A Duniya

August 24, 2025
Kasar Sin Ta Gudanar Da Bita Na 3 Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasara A Yakin Kin Harin Japan

Kasar Sin Ta Gudanar Da Bita Na 3 Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasara A Yakin Kin Harin Japan

August 24, 2025
Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

August 24, 2025
Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

August 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.