• English
  • Business News
Wednesday, June 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamatin Amurka Ta Yi Alkawarin Tallafa Wa Mata ‘Yan Kasuwa A Nijeriya

by Bello Hamza and Sulaiman
8 months ago
in Tattalin Arziki
0
Gwamatin Amurka Ta Yi Alkawarin Tallafa Wa Mata ‘Yan Kasuwa A Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Amurka ta jaddada niyyar ta na tallafa wa ‘yan kasuwa mata a Nijeriya domin kai wa ga babban matakin tattalin arziki, domin samar da daidaito, tsaro da kuma ci gaba ga kowa da kowa.

 

Kasar Amurkan ta ce, wannan tallafin zai zo ne ta hanyar tsangayar ta na Yan Kasuwa mata. Ta bayyana hakan ne a wajen wani taro na kwana uku na tsaffin daliban tsangayar dari da hamsin domin zurfafa ilimin su na fasahar zamani a birnin Legas.

  • Babban Taron Samar Da Kayayyaki Na 2024 Ya Sa Kaimi Ga Kulla Ayyukan Hadin Gwiwa 718
  • Jan Kafar Tinubu Na Cire Harajin Shigo Da Abinci Na Ci Gaba Da Ta’azzara rayuwa

Shirin zai maida hankali ne wajen saita tsaffin daliban a kan gaba a fannin fasahar zamani, domin kawo kirkire-kirkire da kuma cigaba mai dorewa a harkar kasuwancinsu.

 

Labarai Masu Nasaba

Dantsoho Ya Kaddamar Da Aikin Tsaftace Tashar Jirgi Ta Tin-Can Island

Hukumar NPA Ta Yi Watsi Da Zargin Cin Hanci Da Rashawa Da Aka Lakaba Mata

Da yake magana a wajen taron Consul-General din Amurka a Nijeriya, Mr. Will Stebens, ya ce tsangayar ta yan kasuwa mata ta hada sama da mata 130 cikin 150 din da suka kammala karatu a tsangayar a ‘yan shekarun da suka wuce.

 

“Mun dade muna yin wannan a yan shekarun da suka gabata tun 2019. Wannan shiri wanda gwamnatin Amurka ta dauki nauyi domin koyar da mata masu kananan sana’o’i kuma a taimaka masu wajen inganta kasuwancinsu domin su ci gaba ta hanyar fasahar zamani, noma da kuma tattalin arziki”

 

Mr. Stebens ya kara da cewa; “Zai taimaka masu su hadu da mentors a Amurka a tsangayar kasuwanci na Arizona da kuma mentors masu zaman kansu kasar Amurka da kuma a tsakanin su. Wadannan matan da suka fito daga sassa a Nijeriya suna taimaka ma juna wajen habbaka kasuwancinsu da kuma samar da ayyuka ga yan Nijeriya”

 

Ya kuma kara da cewa abu ne mai matukar karfafawa ganin mata na fuskantar kalubalen kasuwanci da kuma hadin gwiwa da kasar Amurka.

 

Mr. Steben ya kuma ce duk shekara tsangayar tana daukar matan da suka nuna sha’awar shiga makarantar guda 30 zuwa 50 domin su anfana da wannan tsari.

 

Stebens ya kuma bayyana yadda tsarin yake cigaba da taka rawar gani wajen tallafa wa ‘yan kasuwa mata a Nijeriya ta hanyar tallafa masu da muhimman jarin kasuwanci.

 

Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Tallafin Kasar Rasha Don Kammala Kamfanin Mulmula Karafuna Na Ajakuta.

 

Gwamnatin tarayya ta sanya hannu a wata yarjejeniya da masu gina kamfanin mulmula karafuna na Ajakuta, Messrs Tyazhapromedport, domin ingantawa, kammalawa da kuma fara aikin kamfanin mulmula karfe a Nijeriya.

 

Babban ministan harkokin karafuna, Shuaibu Audu, ya sanya hannu a yarjejeniyar a madadin gwamnatin tarayya a birnin Moscow, a wata sanarwa da mai magana da yawun ministan ya fitar, Salamotu Jibaniya a ranar juma’a.

 

Kamar yadda ta bayyana, an sanya hannu a yarjejeniyar ne lokacin da ministan ya jagoranci tawagar Nijeriya zuwa birnin Moscow a kasar Rasha, daga ranar 14 zuwa 21 ga watan Satumba.

 

An samar da Kanfanin na Ajakuta ne a shekarar 1979, domin samar da Metallurgical Process Plant tare da Engineering compled da kuma sauran ayyuka makamantansu.

 

Kamfanin dai ya yi shekaru ba tare da ya sarrafa ko karfe kwara daya ba sakamakon cin hanci da kuma tirka tirkar Shari’a.

 

An samar da kamfanin ne domin samar da ayyukan kamfani mabanbanta da kuma ayyukan tattalin arziki wanda suke da muhimmanci wajen raba kafa a harkar tattalin arzikin Nijeriya zuwa industry.

 

Tun bayan zaman shi minista, ministan ya jaddada wa yan Nijeriya cewa kamfanin karfen zai fara aikin sarrafa karafuna domin kawo karshen shigo da karfe daga kasar waje.

 

Domin tabbatar da wannan buri, kwararrun masana daga Messrs TPE sun ziyarci kanfanin da kuma wajen hako karafuna a garin Irakpe domin fara duba yanayin wajen a watan Agusta, wanda hakan ya yi sanadiyar samun gayyata domin sanya hannu a yarjejeniyar.

 

Kamfanin Nobostal M and Proforce, wanda na karkashin kanfanin Tyazhpromedport’s consortium suma suna cikin yarjejeniyar.

 

A wata sanarwa, wakilan na Nijeriya sun duba kayan aikin Messrs Nobostal M, wanda yake a Balakobo a yankin Saratob a kasar Rasha.

 

Da yake magana dangane da wannan ci gaba, Minista Audu ya ce yarjejeniyar wani babban hanya ne na samar da cigaba mai dorewa a harkar tattalin arzikin Nijeriya.

 

Ya kuma kara da cewa; “Dawo da kanfanin zai rage shigo da karfe Nijeriya wanda ya kai kusan kimanin dala biliyan hudu a duk shekara kuma zai taimaka wajen tattalin kudaden kasar waje”

 

A nashi bangaren, sakataren ministan, Chris Isokpunwu, ya ce Nijeriya a shirye take wajen dawo da kanfanin Ajakuta da kuma NIOMCO.

 

A nashi batun, wakilin kasar Rasha ya jaddada cewa za su yi kokari wajen ganin cewa sun girmama yarjejeniyar daidai da yadda gwamnatin Nijeriya ta bukata.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AjakutaKamfanin karafaRasha
ShareTweetSendShare
Previous Post

Manyan Batutuwan Taron Sanatoci Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya A Kano

Next Post

Tinubu Ya Naɗa Hukumar Gudanarwar Hukumar Raya Yankin Arewa Maso Yamma

Related

Dantsoho Ya Kaddamar Da Aikin Tsaftace Tashar Jirgi Ta Tin-Can Island
Tattalin Arziki

Dantsoho Ya Kaddamar Da Aikin Tsaftace Tashar Jirgi Ta Tin-Can Island

4 days ago
Hukumar NPA Ta Yi Watsi Da Zargin Cin Hanci Da Rashawa Da Aka Lakaba Mata
Tattalin Arziki

Hukumar NPA Ta Yi Watsi Da Zargin Cin Hanci Da Rashawa Da Aka Lakaba Mata

2 weeks ago
Yadda Cazar Kudade Da Yawa Ke Haifar Da Raguwar Fitar Da Kaya A Tashoshin Jiragen Ruwa – NPA
Tattalin Arziki

Hukumar NPA Ta Ce Za A Kammala Aikin NSWP A Zango Na Daya A 2026

1 month ago
Shugaban NPA Dantsoho Ya Bayyana Aniyar Inganta Ayyukan Hukumar A Wannan Shekarar
Tattalin Arziki

Shugaban NPA Dantsoho Ya Bayyana Aniyar Inganta Ayyukan Hukumar A Wannan Shekarar

1 month ago
Dalilin Da Ya Sa Nijeriya Ke Ci Gaba Da Rike Kambun Kasa Na Mafi Yawan Samar Da Danyen Mai A Afirka — OPEC
Tattalin Arziki

Dalilin Da Ya Sa Nijeriya Ke Ci Gaba Da Rike Kambun Kasa Na Mafi Yawan Samar Da Danyen Mai A Afirka — OPEC

1 month ago
Yadda Cazar Kudade Da Yawa Ke Haifar Da Raguwar Fitar Da Kaya A Tashoshin Jiragen Ruwa – NPA
Tattalin Arziki

Yadda Cazar Kudade Da Yawa Ke Haifar Da Raguwar Fitar Da Kaya A Tashoshin Jiragen Ruwa – NPA

1 month ago
Next Post
Tinubu Ya Naɗa Hukumar Gudanarwar Hukumar Raya Yankin Arewa Maso Yamma

Tinubu Ya Naɗa Hukumar Gudanarwar Hukumar Raya Yankin Arewa Maso Yamma

LABARAI MASU NASABA

Babban Sauyi Da Ba a Taba Ganin Irinsa Ba a Karni Guda: Alkiblar Da Sin Take Bi Wajen Samun Bunkasuwa 

Babban Sauyi Da Ba a Taba Ganin Irinsa Ba a Karni Guda: Alkiblar Da Sin Take Bi Wajen Samun Bunkasuwa 

June 4, 2025
‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Da Makamai Masu Yawa A Jihar Nasarawa

‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Da Makamai Masu Yawa A Jihar Nasarawa

June 4, 2025
Wang Yi Ya Gana Da Sabon Jakadan Amurka A Sin

Wang Yi Ya Gana Da Sabon Jakadan Amurka A Sin

June 4, 2025
Garkuwa: Sarkin Gobir Ya Bukaci Agajin Gaggawa Daga Gwamnatin Sakkwato

Mutum 7 Sun Rasu Sakamakon Kifewar Kwale-kwale A Sakkwato 

June 4, 2025
Sabon Shugaban Koriya Ta Kudu Ya Yi Alkawarin Sulhu Da Takwaransa Na Arewa

Sabon Shugaban Koriya Ta Kudu Ya Yi Alkawarin Sulhu Da Takwaransa Na Arewa

June 4, 2025
DSS

DSS Da Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 45 A Neja

June 4, 2025
Gwamna Bago Ya Amince Da Biyan Karin Albashin Naira 20,000 Ga Ma’aikata 

Yanzu-yanzu: Gwamnatin Neja Ta Soke Hawan Sallah Sakamakon Ambaliyar Ruwan Mokwa

June 4, 2025
katsina

Gwamnan Katsina Ya Bukaci Hadin Gwiwa Da ‘Yan Kasuwa Domin Cigaban Jihar

June 4, 2025
Ambaliya: Gwamna Zulum Ya Kaddamar Da Rabon Kayan Agaji A Borno

Zulum Ya Yaba Wa Sojoji Kan Kashe Babban Kwamandan ISWAP Abu Fatima

June 4, 2025
Manufar Bude Kofa Ta Shaida Niyyar Sin Ta Ingiza Dunkulewar Duniya

Manufar Bude Kofa Ta Shaida Niyyar Sin Ta Ingiza Dunkulewar Duniya

June 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.