ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, September 12, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamatin Amurka Ta Yi Alkawarin Tallafa Wa Mata ‘Yan Kasuwa A Nijeriya

by Bello Hamza and Sulaiman
2 years ago
Amurka

Gwamnatin Amurka ta jaddada niyyar ta na tallafa wa ‘yan kasuwa mata a Nijeriya domin kai wa ga babban matakin tattalin arziki, domin samar da daidaito, tsaro da kuma ci gaba ga kowa da kowa.

 

Kasar Amurkan ta ce, wannan tallafin zai zo ne ta hanyar tsangayar ta na Yan Kasuwa mata. Ta bayyana hakan ne a wajen wani taro na kwana uku na tsaffin daliban tsangayar dari da hamsin domin zurfafa ilimin su na fasahar zamani a birnin Legas.

ADVERTISEMENT
  • Babban Taron Samar Da Kayayyaki Na 2024 Ya Sa Kaimi Ga Kulla Ayyukan Hadin Gwiwa 718
  • Jan Kafar Tinubu Na Cire Harajin Shigo Da Abinci Na Ci Gaba Da Ta’azzara rayuwa

Shirin zai maida hankali ne wajen saita tsaffin daliban a kan gaba a fannin fasahar zamani, domin kawo kirkire-kirkire da kuma cigaba mai dorewa a harkar kasuwancinsu.

 

LABARAI MASU NASABA

Yadda Taron Bikin Maulidi Ya Gudana A Unguwar Mile 12 A Legas

NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba

Da yake magana a wajen taron Consul-General din Amurka a Nijeriya, Mr. Will Stebens, ya ce tsangayar ta yan kasuwa mata ta hada sama da mata 130 cikin 150 din da suka kammala karatu a tsangayar a ‘yan shekarun da suka wuce.

 

“Mun dade muna yin wannan a yan shekarun da suka gabata tun 2019. Wannan shiri wanda gwamnatin Amurka ta dauki nauyi domin koyar da mata masu kananan sana’o’i kuma a taimaka masu wajen inganta kasuwancinsu domin su ci gaba ta hanyar fasahar zamani, noma da kuma tattalin arziki”

 

Mr. Stebens ya kara da cewa; “Zai taimaka masu su hadu da mentors a Amurka a tsangayar kasuwanci na Arizona da kuma mentors masu zaman kansu kasar Amurka da kuma a tsakanin su. Wadannan matan da suka fito daga sassa a Nijeriya suna taimaka ma juna wajen habbaka kasuwancinsu da kuma samar da ayyuka ga yan Nijeriya”

 

Ya kuma kara da cewa abu ne mai matukar karfafawa ganin mata na fuskantar kalubalen kasuwanci da kuma hadin gwiwa da kasar Amurka.

 

Mr. Steben ya kuma ce duk shekara tsangayar tana daukar matan da suka nuna sha’awar shiga makarantar guda 30 zuwa 50 domin su anfana da wannan tsari.

 

Stebens ya kuma bayyana yadda tsarin yake cigaba da taka rawar gani wajen tallafa wa ‘yan kasuwa mata a Nijeriya ta hanyar tallafa masu da muhimman jarin kasuwanci.

 

Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Tallafin Kasar Rasha Don Kammala Kamfanin Mulmula Karafuna Na Ajakuta.

 

Gwamnatin tarayya ta sanya hannu a wata yarjejeniya da masu gina kamfanin mulmula karafuna na Ajakuta, Messrs Tyazhapromedport, domin ingantawa, kammalawa da kuma fara aikin kamfanin mulmula karfe a Nijeriya.

 

Babban ministan harkokin karafuna, Shuaibu Audu, ya sanya hannu a yarjejeniyar a madadin gwamnatin tarayya a birnin Moscow, a wata sanarwa da mai magana da yawun ministan ya fitar, Salamotu Jibaniya a ranar juma’a.

 

Kamar yadda ta bayyana, an sanya hannu a yarjejeniyar ne lokacin da ministan ya jagoranci tawagar Nijeriya zuwa birnin Moscow a kasar Rasha, daga ranar 14 zuwa 21 ga watan Satumba.

 

An samar da Kanfanin na Ajakuta ne a shekarar 1979, domin samar da Metallurgical Process Plant tare da Engineering compled da kuma sauran ayyuka makamantansu.

 

Kamfanin dai ya yi shekaru ba tare da ya sarrafa ko karfe kwara daya ba sakamakon cin hanci da kuma tirka tirkar Shari’a.

 

An samar da kamfanin ne domin samar da ayyukan kamfani mabanbanta da kuma ayyukan tattalin arziki wanda suke da muhimmanci wajen raba kafa a harkar tattalin arzikin Nijeriya zuwa industry.

 

Tun bayan zaman shi minista, ministan ya jaddada wa yan Nijeriya cewa kamfanin karfen zai fara aikin sarrafa karafuna domin kawo karshen shigo da karfe daga kasar waje.

 

Domin tabbatar da wannan buri, kwararrun masana daga Messrs TPE sun ziyarci kanfanin da kuma wajen hako karafuna a garin Irakpe domin fara duba yanayin wajen a watan Agusta, wanda hakan ya yi sanadiyar samun gayyata domin sanya hannu a yarjejeniyar.

 

Kamfanin Nobostal M and Proforce, wanda na karkashin kanfanin Tyazhpromedport’s consortium suma suna cikin yarjejeniyar.

 

A wata sanarwa, wakilan na Nijeriya sun duba kayan aikin Messrs Nobostal M, wanda yake a Balakobo a yankin Saratob a kasar Rasha.

 

Da yake magana dangane da wannan ci gaba, Minista Audu ya ce yarjejeniyar wani babban hanya ne na samar da cigaba mai dorewa a harkar tattalin arzikin Nijeriya.

 

Ya kuma kara da cewa; “Dawo da kanfanin zai rage shigo da karfe Nijeriya wanda ya kai kusan kimanin dala biliyan hudu a duk shekara kuma zai taimaka wajen tattalin kudaden kasar waje”

 

A nashi bangaren, sakataren ministan, Chris Isokpunwu, ya ce Nijeriya a shirye take wajen dawo da kanfanin Ajakuta da kuma NIOMCO.

 

A nashi batun, wakilin kasar Rasha ya jaddada cewa za su yi kokari wajen ganin cewa sun girmama yarjejeniyar daidai da yadda gwamnatin Nijeriya ta bukata.

Amurka
Bello Hamza
+ posts Bio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Abin Da Ya Kamata Ka Sani Kan Hannun Jarin Matatar Dangote
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Jihar Kano Za Ta Amfana Matuka Da Gidauniyar Aliko Dangote – Masu Ruwa Da Tsaki
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    An Nuna Damuwa Kan Sake Kamun Da DSS Ta Yi Wa Boɗejo Bayan Samun Belin EFCC
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Dole Al’ummar Arewa Su Rungumi Hanyoyin Kasuwanci Na Zamani —Alfa Musa
Amurka
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Kalaman Christopher Musa Game Da El-Rufa’i Na Ci Gaba Da Tayar Da Ƙura
  • Sulaiman
    Gwamna Dauda Lawal Ya Raba Motocin Aiki Ga Manyan Makarantu A Zamfara
  • Sulaiman
    Jam’iyyar APC Ce Za Ta Lashe Zaɓen Shugaban Ƙasa Da Gwamnoni A Nijeriya -Dikko Raɗɗa
  • Sulaiman
    Mene Ne Ra’ayinku Kan Dawo Da Tallafin Man Fetur Ko Barin Sa?

MASU ALAKA

Yadda Taron Bikin Maulidi Ya Gudana A Unguwar Mile 12 A Legas
Tattalin Arziki

Yadda Taron Bikin Maulidi Ya Gudana A Unguwar Mile 12 A Legas

September 4, 2026
NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba
Tattalin Arziki

NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba

September 4, 2026
NPA Ta Tabbatar Da Maido Da Manyan Kayan Aikin Hukumar Wuta Ta Neja Delta —Babbar Manaja
Tattalin Arziki

NPA Ta Tabbatar Da Maido Da Manyan Kayan Aikin Hukumar Wuta Ta Neja Delta —Babbar Manaja

August 28, 2026
Next Post
Tinubu Ya Naɗa Hukumar Gudanarwar Hukumar Raya Yankin Arewa Maso Yamma

Tinubu Ya Naɗa Hukumar Gudanarwar Hukumar Raya Yankin Arewa Maso Yamma

LABARAI MASU NASABA

Zan Dawo Da Tallafin Mai Ne Don Rage Farashin Fetur Da Na Sufuri – Atiku

Zan Dawo Da Tallafin Mai Ne Don Rage Farashin Fetur Da Na Sufuri – Atiku

September 12, 2026
An Gargaɗi Mazauna Kusa Da Kogin Kaduna Kan Sako Ruwa Daga Shiroro

An Gargaɗi Mazauna Kusa Da Kogin Kaduna Kan Sako Ruwa Daga Shiroro

September 12, 2026
Shekaru 22 Bayan Rushewar Nigeria Airways, Gwamnati Ta Biya Ma’aikata 2,700 Biliyan 18

Shekaru 22 Bayan Rushewar Nigeria Airways, Gwamnati Ta Biya Ma’aikata 2,700 Biliyan 18

September 12, 2026
Kalaman Christopher Musa Game Da El-Rufa’i Na Ci Gaba Da Tayar Da Ƙura

Kalaman Christopher Musa Game Da El-Rufa’i Na Ci Gaba Da Tayar Da Ƙura

September 12, 2026
Dangote Ya Ƙara Farashin Fetur, Kwana 2 Kafin Shiga Kasuwar Hannun jari

Sanata Yari Ya Gudanar Da Taron Masu Ruwa Da Tsaki A Zamfara

September 12, 2026
Gwamna Dauda Lawal Ya Raba Motocin Aiki Ga Manyan Makarantu A Zamfara

Gwamna Dauda Lawal Ya Raba Motocin Aiki Ga Manyan Makarantu A Zamfara

September 12, 2026
Dangote Ya Ƙara Farashin Fetur, Kwana 2 Kafin Shiga Kasuwar Hannun jari

Dangote Ya Ƙara Farashin Fetur, Kwana 2 Kafin Shiga Kasuwar Hannun jari

September 12, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Jam’iyyar APC Ce Za Ta Lashe Zaɓen Shugaban Ƙasa Da Gwamnoni A Nijeriya -Dikko Raɗɗa

September 12, 2026
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN

Mene Ne Ra’ayinku Kan Dawo Da Tallafin Man Fetur Ko Barin Sa?

September 12, 2026
Sin Ta Nuna Rashin Jin Dadinta Ga Italiya Da Tarayyar Turai Kan Ziyarar Jami’ar DPP

Sin Ta Nuna Rashin Jin Dadinta Ga Italiya Da Tarayyar Turai Kan Ziyarar Jami’ar DPP

September 11, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.