• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Idris Ya Nada Dan Marigayi Sheikh Giro Mukami A Hukumar Alhazai Ta Kebbi

by Muhammad
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Gwamna Idris Ya Nada Dan Marigayi Sheikh Giro Mukami A Hukumar Alhazai Ta Kebbi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamna Nasir Idris na Jihar Kebbi ya nada, Hussaini Abubakar-Giro, a matsayin mamba a hukumar jin dadin alhazai ta jihar Kebbi, don maye gurbin mahaifinsa, Sheik Abubakar Giro, wanda ya rasu a ranar Laraba.

Kungiyar Jama’atu Izalatil Bid’a Wa’iqamatus Sunnah ta kasa (JIBWIS) ta kasa ta roki Gwamnan da ya duba daya daga cikin ‘ya’yan marigayin kan mukamin da aka bai wa mahaifinsu wanda Gwamnan ya amince da hakan.

  • Tinubu Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Babban Malamin Addinin Musulunci Giro Argungu
  • NUJ Kebbi Ta Yi Alhini Rasuwar Tsohon dan Jarida Ibrahim Argungu

Alhaji Ahmed Idris, Babban Sakataren Yada Labarai na Gwamnan ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya raba wa manema labarai a Birnin Kebbi ranar Lahadi.

Ahmed Idris ya bayyana cewa gwamnan ya amince da nadin ne a lokacin da ya karbi bakuncin shugabannin kungiyar (JIBWIS) karkashin jagorancin shugaban kungiyar na kasa, Sheik Abdullahi Bala-Lau, wanda ya kai ziyarar ta’aziyya ga gwamnan a gidan gwamnati da ke Birnin Kebbi.

Gwamnan ya tabbatar wa kungiyar Izalar cewa an riga an karbi wannan kiran.

Labarai Masu Nasaba

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

‘Yan Bindiga Sun Harbi Fasinjoji 2 A Jihar Neja

Idris ya godewa kungiyar bisa wannan ziyarar, inda ya ce: “Rashin ba ga iyalansa kadai ya shafa ba har kowa da kowa.”

Ya ce Abubakar Giro wani ginshiki ne na yada addinin Musulunci a kasashen Afirka da dama, ya kuma yi addu’ar Allah Ta’ala ya gafarta masa kurakuransa, ya karbi ayyukansa na alheri, ya saka masa da Jannatul Firdaus.

Malaman sun kuma gabatar da addu’o’i na musamman ga marigayin, da sauran musulmin da suka rasu tare da addu’ar samun zaman lafiya a dukkan sassan Nijeriya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Giro ArgunguGwamna KebbiNasir AhmadSheikh Giro
ShareTweetSendShare
Previous Post

Brazil Ta Cire Sunan Antony Daga Tawagarta Saboda Zargin Dukan Budurwarsa

Next Post

Gwamnonin Arewa Maso Gabas Sun Koka Kan Kwararar ‘Yan Bindiga Zuwa Jihohinsu

Related

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido
Manyan Labarai

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

13 hours ago
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Harbi Fasinjoji 2 A Jihar Neja

14 hours ago
Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano
Manyan Labarai

Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano

17 hours ago
Ahlul Faidhati Mai Diwani Group
Rahotonni

Yadda Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Suka Yi Maulidin Cikar Annabi (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa 

18 hours ago
Ƙungiyar Ƙwadago Ta Ba Gwamnati Wa’adin Kwana 14 Ta Janye Sabon Harajin Man Fetur
Manyan Labarai

Ƙungiyar Ƙwadago Ta Ba Gwamnati Wa’adin Kwana 14 Ta Janye Sabon Harajin Man Fetur

19 hours ago
Likitoci Masu Neman Ƙwarewa Sun Fara Yajin Aikin Ƙasa A Nijeriya
Manyan Labarai

Likitoci Masu Neman Ƙwarewa Sun Fara Yajin Aikin Ƙasa A Nijeriya

20 hours ago
Next Post
Gwamnonin Arewa Maso Gabas Sun Koka Kan Kwararar ‘Yan Bindiga Zuwa Jihohinsu

Gwamnonin Arewa Maso Gabas Sun Koka Kan Kwararar ‘Yan Bindiga Zuwa Jihohinsu

LABARAI MASU NASABA

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido Ba

September 13, 2025
Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

September 12, 2025
Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

September 12, 2025
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

September 12, 2025
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

September 12, 2025
Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

September 12, 2025
Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

September 12, 2025
Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

September 12, 2025
Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154

Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154

September 12, 2025
Korafin Philippines Ya Tabbatar Da Halascin Matakan Da Sin Ke Dauka Na Kare Muhalli a Tsibirin Huangyan

Korafin Philippines Ya Tabbatar Da Halascin Matakan Da Sin Ke Dauka Na Kare Muhalli a Tsibirin Huangyan

September 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.