• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Inuwa Ya Bukaci Musulmai Su Ci Gaba Da Habbaka Darussan Ramadana

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Gwamna Inuwa Ya Bukaci Musulmai Su Ci Gaba Da Habbaka Darussan Ramadana
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya ya buƙaci al’ummar jihar su ci gaba da gudanar da ayyukan su na ibadah da suka yi a watan na Ramadana, da addu’o’in zaman lafiya da ci gaban jihar da Nijeriya baki daya. 

 

Gwamnan ya yi wannan kiran ne a sakon sa na Barka da Sallah da Ismaila Uba Misilli, hadiminsa a bangaren yada labarai da hulda da jama’a ya fitar.

  • Inuwa Ya Bai Wa ‘Yan Kasuwan Gombe Kyautar Naira Miliyan 500 Don Karfafa Kasuwancinsu 

Gwamna Inuwa, wadda ya bayyana sallar Eid-el-Fitr a matsayin lokacin tunani da nazari kan rahamomin Allah ga bayi, ya bukaci al’ummar Musulmi su rinka dabbaƙa darusan da suka koya a watan na Ramadan a rayuwar su ta yau da kullum.

 

Labarai Masu Nasaba

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

Ya ce, “Yayin da muke bukukuwan Eid-el-Fitr, ina yi mana nasiha da mu yi koyi da kyawawan darussa na watan Ramadan wadanda suke nuni da takawa, da biyayya, da sadaukarwa. Dole ne dukkan mu mu yi koyi da koyarwar Musulunci da ke tabbatar da zaman lafiya da hakuri, da kana’a da kuma kauna”.

 

Gwamna Inuwa ya kuma bukaci al’ummar jihar da cewa kar su sare game da kalubalen zamantakewa da na tattalin arziƙin da ake fuskanta a kasar nan, amma su jajirce wajen yin addu’o’i, yana mai cewa idan suka jajirce, jarabawar da ake ciki za ta wuce, kuma Nijeriya za ta kara karfi da karsashi da hadin kai.

 

Ya kuma bukaci jama’a su ci gaba da ririta zaman lafiya da kwanciyar hankali da ake da shi a jihar, inda ya yi kira ga malamai da sarakuna su ci gaba da wa’azin hadin kai da hakuri a tsakanin al’ummomi daban-daban don samun zaman lafiya da ci gaban Jihar Gombe da kasa baki daya, yana mai bayyana zaman lafiya a matsayin ginshilin ci gaban zamantakewa da tattalin arzikin kowace al’umma.

 

Gwamna Inuwa, ya kuma jaddada cewa gwamnatin sa ba za ta lamunci duk wani abu da zai iya kawo cikas ga zaman lafiya da ake da shi a jihar ba, kuma zata ci gaba da mai da hankali wajen ganin an samar da ribar demokradiyya ga al’ummar Jihar.

 

Sai ya yi kiran yin addu’o’i na musamman ga shugabanni a kowane mataki. “A irin wannan muhimmin lokaci na sauyin mulki da za a yi a kasar mu nan bada dadewa ba, ina kira a gare mu dukka, mu yi ta addu’a domin samun sauyin cikin kwanciyar hankali, musamman ma ga shugabanni masu zuwa a mukamai daban-daban, domin Allah ya basu hikima ya kuma yi musu jagora wajen sauke nauyin da ke kan su”.

 

“Ina mika godiya ta ga sarakuna da shugabannin al’umma da malaman addini da kuma dokacin al’ummar Jihar Gombe bisa goyon bayan da suke bai wa gwamnatin mu. Ina kira a gare mu, da mu sake sadaukar da kan mu, mu bada kyakkywar gudumawa ga ci gaban jihar mu. Ina mai tabbatar muku cewa gwamnatin mu ta himmatu wajen ganin Jihar Gombe ta samu ci gaba cikin sauri da kuma dorewar ci gabanta baki daya.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Qin Gang Zai Jagoranci Taron Ministocin Sin Da Kasashen Yankin Tsakiyar Asiya Karo Na 4

Next Post

Sin Da Zambia Sun Yi Bikin Cika Shekaru 60 Da Fara Tura Likitocin Sin Afirka

Related

Daurarru
Labarai

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

3 hours ago
Wutar lantarki
Labarai

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

5 hours ago
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka
Labarai

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

6 hours ago
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano
Manyan Labarai

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

7 hours ago
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu
Labarai

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

9 hours ago
Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara
Labarai

Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

10 hours ago
Next Post
Sin Da Zambia Sun Yi Bikin Cika Shekaru 60 Da Fara Tura Likitocin Sin Afirka

Sin Da Zambia Sun Yi Bikin Cika Shekaru 60 Da Fara Tura Likitocin Sin Afirka

LABARAI MASU NASABA

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.